(FINAL)CHAPTER 38

IDAN KUNA KARUWA DA LABARINNAN AYI FOLLOWING DINA SANNAN AYI VOTING

Mikewa su aunty maryam sukayi uncle ABBA yace toh malam aliyu mu zamu wuce abinda ya faru a baya a yafe mu tunda de kasan ba laifin mu bane mantuwa ce ni bazan iya cewa komai ba saide Allah ya bada zaman lafiya.

Tunda kuma kunyi shawara kamin kuka yanke hukunci mu bazance komai ba. Aunty maryam tace mun kuma gane kuskuren mu na auren sirri da mukayi muku muna kuma bawa iyaye shawara kimin rintsi kar suyi ma yaransu aure a boye ko na dole domin duk sun Saba addinin musulunci domin hakan bai taba faruwa a zamanin magabata ba.

A kwana a tashi wasa wasa cikin luba ya baiyana ya girma kuma ladidi ta fita a iddarta. Kullum kaman yaya da kanwa ita da luba suna dinke idan aliyu ya dawo daga wajen aiki tsakaninsu gaisuwa. Daga nan ya shige ciki luba tabi bayansa.

Yauma kamar kullum suna kitchen luba an bararraje akan island kamar uwar Mata ladidi na dama Mata kunun madara. Sallamar aliyu da musa sukaji domin kuwa shugaban leburori aliyu ya bashi tunda daga karatun primary ya tsaya amma ya jona yaki da jahilai kuma yana skill acquisition na computer so yana sa rai yayi using certificate dinsa ya shiga jami'a nan da watanni 7.

Mika Mata kunun ladidi tayi tace toh maman yan uku mijinki ya dawo nima najiyo Muryan future hubby na bari nabi bayan labule na wuce ko? Dariya Luba tayi ta zamo dakyar sanadiyyar nauyin da cikin ya fara saboda ya shiga wata na bakwai.

Bin bayan ladidi luba tayi da kallo tana mai tausaya Mata yadda ta rabu da mijinta kuma bata hassada ma matarsa.
Fitowa parlour tayi musa wato mus yace a ah auntyn mu ashe kece a kitchen din tace wallahi kuwa yaya mus ina wuni? Yace lafiya mun sameku lafiya ko? Tace Alhamdulillah dan kyakkyalla ido yake ko zakiga ladidi amma bai ganta ba.

Luba da ta gano sa tace aiko yanzunnan aunty ladidi ta shige daki nasan zata fito diba maka abinci da wannan ta shige dakinta aliyu yabi bayanta bayan ya dauko ludayi a kitchen. Bata ankare ba kawai taji ya tsindumo Ma ta ludayi a cikin kunu turo baki tayi tace wai kai wani irin baba ne kullum kana cikin shanye ma yaranka kunu ? Gwaliyo ya Mata yana dariya ta matsar da kunun tace kasha rabonka.

Yace haba maman babies kar muyi haka dake please kinji kunun ne dadi dukda cewa na jiya yafi dadi tace Allah ya soka ni nayi na ajiyan bani ludayin in diba maka rabi.
Yace uhm uhm kishi na damun wata ko? Ya fada yana dauke kai tace a bakin kunun ka yace tuba nake sarauniya yana miko Ma ta ludayin Suka kyalkyale da dariya.

Ladidi kuwa tana shiga daki ta goge hawayenta ta fada kan gado tana cire hijab din dake jikinta tace ya Allah ka yaye min kashin dake damuna Allah ka gani bawai Dan inason musa nabar aliyu ba na barshi ne saboda ina tsoro. Bazan iya zama da kishiya ba kar na cutar da luba Allah ko digon son musa ne kasa min Allah indai na taba yin wani aiki na ALKHAIRI ina tawassali dashi ka zaba min mafi alkhairi.

Mayar da hijab dinta tayi ta fita ba kowa a parlourn ta dauki abincin mus ta nufi dakinsa dake bayan gidan tu da saura satu a gama gyaran gidan da aliyu ya basu. Kwankwasawa tayi ya bude yana Mata murmushi ta tsuguna ta gaisheshi yana fadin nagode sosai ladidi aci gaba da hakuri dani tace ba komai ni zan koma yace toh anjima zanzo inji me da me kike bukata na auren dukda cewa kinsan har yanzu abubuwan basu bude ba.

Tace ai ba komai kasan ba wani shagali za'ayi bama nagode. Tana kaiwa nan ta Mike ta shige gida abinta. Ita fa har ga Allah a wani sako na zuciyar ta haushin mus takeji.

Bayan Sati biyu aka daura auren musa da ladidi saide luba abin bai Mata dadi ba saboda bata iya tafiya Dan yara 3 sunyi Mata nauyi idan ba ya zama dole kamar zuwa bandaki ba toh bata tashi yaso ayi auren bayan ta haihu musa yace AI bazai hana ladidin zuwa Gidan ba.

Su aunty maryam da makota kadan ne kawai suka kaita ba wani taro Dan ma kwana 3 kamin biki aunty maryam uwar gyara ta dauketa akayi Mata gyara Wanda ko aurensa na farko ba'ayi Mata ba.

Bayan sun tafi tana zaune a dakinta taji shigowan su mus kukanta ya tsananta shi da aliyu ne kadai nan de aliyu yayi musu nasha da fata na gari ya gudu Dan shi kanshi kishi ke taso masa wai matarsa ce ke daukan sunan matan wani.

Koda ya koma gida ya samu luba ma an zuba tagumi ga rid'ed'en ciki taga ya shigo jiki a sanyaye. Zama yayi a gefenta baice komai ba sai hawayen da yake gogewa. Bata ce masa komai ba Dan itama tayi missing ladidi amma tana jin kishin yadda yake ma wata kuka ganin zai fashe da kuka yasa ta rungumo shi a kirjinta tana shafa kanshi ya gama kukansa harda shessheka ita kam mamaki ma ya bata a haka har yayi bacci.

Zata kwantar dashi a gefe saboda yadda bayanta ya rike ya kankameta yana fadin lubabatu Karki barni ke daya ce gareni Dan Allah. Shafa kanshi tayi a hankali tace bazan barka ba tana kwantar dashi kamin ta shige ban daki Dan fitsari take ji.

Dakin su mus kuwa tsoro yakeji kar ladidi tace baikai aliyu ba gashi shi ba gwani bane a fannin Dan bai taba sanin mace ba. Yace toh ladidi godiya ta tabbata ga Allah..... haka dai ya gama Mata jawaban shi ya ce su tashi suyi sallah. Shi yajasu domin kuwa cikin watannin nan ya zage ya koyi karatu sosai.

Riko hannunta tayi yace zo muci abinci kinji ? Kawai sai ta fashe masa da kuka shi rikecewa yayi dama haka amaren keyi ko ladidin ne? Da kyar ya lallabata ta bada hadin kai badan taso ba.

Bayan wata daya da sati uku ladidi tana bakin gadon luba tana zaune luba tace aunty ladidi Anya kuwa kinajin dadin zamanki da mus? Naga sai ramewa kike kina baki. Ladidi tace banida lafiya ne nace ma a kawo min sakamakon zasu iya zuwa ko wani lokaci. Nan take cewa kema haihuwa yau ko gobe gara na karasa hada miki jakan nan.

Baifi minti 5 da hiran ba akace Mata an kawo result din karbowa tayi ta bude taga maleria and typhoid report ne kuma negative dayan ta bude taga....

PREGNANCY REPORT ne kuma positive wani ihu ta buga tayi zaman daba tana fadin na shiga uku lubabatu innalillah wa inna ilaihi raji'un. Zabura luba tayi ganin yadda ta rude tace aunty karde kice min HIV gareki? Ladidi tace HIV din banza lubabatu ciki gareni na shiga uku na.

Luba tace kamar yaya aunty ladidi ? Cikin ne masifa ko me? Ladidi tace wallahi Allah banason mus kawai zama nake dashi yanzu kuma saina Haifa masa da? Aliyu ne ya shigo da gudu hannu a ka yana fadin innalillah wa inna ilaihi raji'un ladidi ashe har kinji sakon saide hakuri Allah yayinwa musa rasuwa. Dam! dam !! Kukeji take labour ya rike luba Wanda bata shirya ba ladidi ko shako aliyu tayi tace kaji maganar banza, kai ka kasheshi? Yace hakuri zakiyi ladidi.

Tace karya ne wallahi karyane musa na bai mutu ba ko a Nemo min shi ko nayi tashin hankali kace masa ya tashi, bai isa ya mutu ya barni ba. Aliyu yace haba ladidi karkiyi sabo mana. Bayan kin gama takaba sai na aureki ko?

Atake fire din luba ya fashe amma basu ma lura da ita ba ladidi tace bani SONKA wallahi yanzu shi nake so!
Murmushi yayi yace zo muje. Suna fita suka ga mus yana musu murmushi da gudu ta rungume shi tana fadin mus mus Dina shine zaka bari a bani tsoro ace min ka mutu ? Ta fadi haka tana dukan kirjinsa.

Dariya take yace laifinki ne AI muna dawowa muka jiki kina ihu wai baki sona zaki haifamin da shine oga aliyu yace zai gwadaki ashe de kina so na? Tace bana son tsokanan nan Dan Allah karka barni kneeldown yayi ya rungume jikinta yana dariya yace kai Dan samari kace daddy.

Dariya aliyu yayi daidai lokacin luba ta kwalla kara nan akayi hospital da ita bayan awanni 6 ta haifo yaranta maza 3 cas.

Bayan an gyarasu ne su ladidi suka shigo kowa yadau daya sai lokacin aka tuno da wasu aunty maryam aka sanar musu luba tace kai gaskiya nan gaba Allah yasa na haifi mace. Ladidi ta dungure mata kai tace oh su luba ande ji kunya..

Kwaikwayanta ta soma yi tana fadin waiyo Allah na aliyu ka cuceni bazan sake haihuwa ba wallahi ko yatsa na ka sake rikewa saina yanke ma hannu... yanzu kuma fadi take Allah yasa ta haifi mace.

Da shike a jingina luban take tayi Muryan ladidi tace "na shiga uku lubabatu innalillah wa inna ilaihi raji'un wallahi Allah banason mus kawai zama nake dashi yanzu kuma saina Haifa masa da?"
Sai kuma muka ga mutuniyar na fadin "karya ne wallahi karyane musa na bai mutu ba ko a Nemo min shi ko nayi tashin hankali kace masa ya tashi, bai isa ya mutu ya barni ba."
Dariya suka kyalkyale dashi dukansu aliyu yace toh ku jera muyi selfie! Yace cheese! Take da daukan hoton CLICK!

ALHAMDULILLAH! ALLAH YAYI KAMAR YADDA NA FARA A SA'A GASHI NA KARKARE MUKU WANNAN LABARI NAWA. INA MATUKAR GODIYA GAREKU MASOYA NA. FATAN ZAKU DUBA SABON LABARI NA MAI SUNA (YAJI TA MATA)

Sabon labari na me suna YAJI TA MATA shine littafina na uku....

Labarin wani saurayi ne Wanda bashida aiki sai zina, a cewar sa ba laifinsa bane Allah ne yayi sa hariji. Toh hakan ne yasa iyayen sa suka rufe ido sai yayi aure amma fa an gudu ba'a tsira ba domin kuwa babu wacce take iya zaman sati biyu dashi tsanani kwana 10 sai su gudu. Toh fa an Sami matsala domin reshe ta juye da mujiya inda Allah ya hadosa da Wanda ta fisa jaraba toh yanzu kuma shi ke gudu.

Wai ya za'a kwashe ne a lokacin da iyayen sa sukace bai isa ya saketa ba kamar yadda ya dafa kur'ani cewa bazai saketa ba?

KU BIYONI CIKIN WANNAN LABARI NAWA DAN JIN YADDA ZA'A KAYA.

GA LINK NAN https://my.w.tt/EMbqkgIeh8

TAKUCE KARAMARSU BABBARSU WATO

Miss untichlobanty 💕

17th July,2020.

Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top