34:don't

*♡TUNTUBEN HARSHE🌺*
_Voyage within the hearts!_

        *WATTPAD*
  *@SURAYYAHMS*
_Brilliant writers   Association_

_Any resemblence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence!_

_34..resonance_

Cike da taurin kai yace oho nide zan bita ko bazan iya ce mata komi din ba..yes im confused..me zanyi in ji sauki araina to?carmilla said alot to me i feel sooo stupid bro..ajiyan zxiya yaja me zafi Sanann ya sulale ya zauna bakin gadon ya dafe kansa"slowly nd painfully ya soma mayar ma dan uwan sa furucin carmilla na karshe babu batan kalma har ya ja nunfashi azad be motsa ba..wani shiru ne ya mamaye wajen bayan kaman minti uku Azad din sai ya taho ya zauna daf dashi yace"..Asad..,matsalar ka shine baka nitsuwa kayi tunani,inda kayi tunani da zaka gane abunda ya dace kayi tin farko...ni zanje in duba mama..jiya naga kamar bata jin dadi,stay here nd think,in kuma tafiyan zakayi fine..daga nan sai ya barshi a zaune awajen

Asad Fuskan sa ya shafa da tafukan hannun sa sannan ya sace ajiyan zucia yana me neman nitsuwa ma kwakwalwar sa.

Dayaga Ya kasa samun nitsuwar komawa yy kan gadon ya dunkule waje guda,kan kace wani abu bacci ya dauke sa..

Anan babu yadda azaad beyi da mama tayi ma asad magana ba amma haka taki firr farkawan asad sai ya tashi da ciwon kai me tsanani hawaye ne me zafi kebin kuncin sa,he is calm now..farko shiga tolet yy ya watsa ruwa ya doro alwala ya rakaa biu,anan ma sanda ya karanta shafuka dayawa a qur'ani sannan ya soma jin kansa a dede yyi tunani,sunyi zaman egypt kuma suna jin labarci sosai,yau aransa ji yake kamar qur'anin ma fada yake masa akan halayyar sa

Da kyar ya kawo tunanin mafarin matsalar sa,wato rashin jituwar sa da kawu"..yasan inda ace komi xai wuce tsakanin su 80% of his worries wll be gone,kuma nadra ma zata iya yafe masa."just like carmilla said go home nd aprciate ur dad,yanzu ne ya dace ya dakatar da komi dan ya fahince mahaifin sa,bayan ya samu nitsuwa kadan ya saka sleepers din sa ya nufo main house mama da azad suna zaune sai gashi ya shigo musu a bazata,adan dole yake ma mama magana tana kaucewa mama tun bata iya ansawa da kyau har tausayin sa yaci karfin ta,"a kasa agaban ta ya xauna ya rike gwiwan ta kamar zautacce..yace mama kema inkika rabu dani bansan ya zanyi ba,ki daure ki sake tausaya min wannan karon namiki alkwari wallh bazan yi judging din kowa ba bare na sake jefa ki a kuskure nasan baba Yana fushi dani,in be daina ba nadra ma baxata yafe min abunda nayi ta mata ba...mama tace Asad kaje ka samar ma kanka mafita ni bazan iya ba,bakajin maganan kowa Asad,da kanajii da ba haka ba,yace mama zanji..walhy zanji nide kar ki barni wallhy bana jin dadin rayuwata mama tace a hakan?shi soyayyar iyaye yakanzo a siga biu ne Asad,ko subi raayin ka na yaranta su faranta maka rai ka lalace ko su kika duniya ta so ka..asad rashin nitsuwar ka ne ya sa ka kasa ganin soyayyar mahaifinka nikuma na biye maka sabida ina matukar kaunar ka,sau daywa naki gaskia sabida tsoron damuwar da zaka shiga ciki tabbas nima na dauka hka kawai baban ka yake matsa maka amma da wautar mu y sanya ni jefa mareniyar Allah a gidan yari nan ne na dawo hayyaci na

To inbaka sani ba mahaifin ka yana sane da duk abunda kakeyi na shan taba,da yawan zuwa party amma be taba yunkurin ya hanaka ba duk sabida tsoron kar kafi haka lalata rayuwan ka shi kuma ya shiga uku...mahaifin ka yana kaunar ka sosai Asad shiyasa Abubuwa dayawa game da kai yake masa ciwo,duk da haka taurin kanka ne yake bashi tsoro matuka..

A duk sanda yaje maka fada wallhy yana huce takaicin sa ne yea sometimes he is wrong,anma yanzu nikaina na fahimce sa, zuciyar sa ne ke deban sa yayi maka fada ko yaji baxai iya saka maka albarkan sa ba..."love hurts Asad.. Ranar da ka haifi abunda kake matukar so sannan kagan sa yana kaucewa baka da kuma halin da zaka cece shi nan ne zaka fahinci girnan damuwar da ka dasa a zuciar mahaifin ka...

All he want is for u to be responsible

Kana da ilimi na baiwa wanda bakowa yake da shi ba,awajen ka hakan rahmar ubangiji ne amma a wajen  mutane babban kalubale ne,a rayuwa ba kowani dan adam yake son zama da genious irin ka ba sabida komin ka zaizo daban ne..alot of evil eyes wll be on u.

Kuma Tunda kazo dunia baban ka yake cikin damuwa akan haka,shiyasa y zabi ya tarbiyan tar daku cikin tsauri koda zaku gane alqiblar rayuwan ku,Ga dan uwan ka shi Azaad ya fahince hakan shiyasa yay biyayya ya zamto me hakri,..amma Asad menene laifi in an tsaya akan ka dan aga an nuna maka hanya me bullewa?

Azaad a egypt yake rayuwan sa batare da mu ba,shi kataba tunanin cewa in takuri baban ka yake soo zai kyale sa shikadai muzo nan?..to kasani daga hankalin ku yake aunawa baka taba nuna nasa kai me hankali bane inda ace baka da taurin kai wajen bida rayuwan ka dede da tuni ya dauke ido akanka kaima....but ure still his son bazai iya zama yana gani kana dada baudewa ba,even when i try to reason with u,sai gashi sabida kai nadra ta sha bakar azaba a awaje na

Na taba gaya maka cewa na tuhume da laifin hada tsakanin ka da mahaifin ka?

I dint want to blame u or ur dad,so i blamed her,nadra tayi hakri dani sosai..sau dayawa nakan mata furuci me kuna mesa ta tuno da marecin ta

Nabi bayan ka akan case din nan,ko dan son ingane me gaskia a tsakanin ka da mahaifin ka.
Sai gashi na gane nayi kuskure me girma..dan me gaskiya baya fada akan gaskiar sa shirun da mahaifin ka ya mana ya jefa ni tunani..nazo nasan cewa akanka
Ne mahaifin ka yake fama da tozarci da cusgunawa a wajen aikin sa,sabida yarinyar can,anan yazo ya maka fadan ka rabu da ita amma se nabi bayan ka,nadra ma taki ta sai muka bige muka ce kishi ne,ban lura ba ashe tsoro ne ..Asad ka sani,duk inda ka rike amana da arne a kullum a son kansa yake..

Nide banda abunda zan yi maka yanzu sai kaje kayi tunani duk abunda ka yanke shikenan.

Amma kasani,jiki yakan gyaru ne in zuciyata ta gyaru,a hankali tasa hannayn ta ta dafo kafadun sa,tace u need to start over...kaji dana?ya dago ya kalle ta jikin sa a mugun muce yace ok ma..sai y mike tsaye ya juya ya bar musu dakin

Mama taji tausayin asad amma gani take in ta sake kula sa zata iya sake shiga rudani,sai ta ce ma azzad ya tsaya akan dan uwan sa..kar ya barshi,dan Asad baya bukatar yayi tunanin rayuwar sa shikadai"hakan kuwa akai,lokaci lokaci azad yakan je ya duba yanayin sa a dakin sa,karshe ma kayan sa ya tattara ya dawo anan ya kwana tare da shi batare da ya matsa masa akan maganan ba ..a washe garin ranar kawu ya dawo,Asad ya gama naxarin sa aransa amma koda yau suka shugo gaishe da kawun sai yaji bazai iya tunkarar sa da komai ba,tunda suka gaisa anan sai yayi shiru yana jin su mama suna ta tanbayar sa lpyar nadra yana ansawa

Kawu yace azad zaije kotu gobe a madadin nadra dan a gobe ne za aka kawo carmila gaban kotun akan sauran maganan da aka dakatar sabida rashin samun ta akan lokaci.

Kawu be ce ma asad komai ba sai akan jarabawan su,nan ma cewa yy Allah ya temaka.

Da azad zaije kotun ji yy kamar ya bisa suje yaga faduwar campbells ko hankalin sa zai kwanta,amma sanin carmilla tana wajen sai ya ji tsoron kar yaje ta sake gaya masa abunda zai dame sa

Daga ranar sai ya dawo shiru shiru sosai,yana ta so shima ya sake kamar azad ko dan ya nemi gafarar kawu anma zuciar sa na mugun masa nauyi sau dayawa ko yazo gaban sa da niyyar magana sai yaga baya iyawa.

Kullum tunanin kalman da zai fara da shi yake,ya saka wannan y warware har kawun dakansa ya gane damuwar sa,yana exams ne amna da wuri yakanje ya dawo sabida yanzu baya kula kowa,har yau fatima bata dena fushin ta da shi ba a gida kullum zai je sallan asubahi tare da su kawu kuma dik wani abu da akeyi yakan sa kansa yayi har suyita mamakin sa
Gashi By now labarin fake death in carmilla ya karade makaranta,kowa ynzu yasan sister ta tana prison uwa uba da labarin yadda asirin baban ta ya tonu shima daurin rai da rai,ance kotu ta tsare carmilla na watanni sabida lalata min suna duk dama lawyern ta ya proving cewa tursasa ta campbells yay,a dalilin bata sunan da sukayin ne kotu tasa su sun bada kudi kimanin 10million diyya ma nadran ita kadai,to aranan da kudin ya fito kawu ya aike azad yaje yola domin sanar da mu komii

Yau sati na uku da tafiya yola,ayaune kuma ake rubuta paper na karshe a school ma asad
Shikadai,Yaune azad zai dawo daga yola bayan yakai mana aikan.

Kwana uku sukayi min amma Be fada ma kawu cewa ya zo da fatima bugaje inda nake ba,su suka shirya abun su dan tasan a gidan su in tace waje na zataje baxa a hana ta ba,nikam nayi matukar jin dadin zuwan nasu dan har yanzu da damuwa araina bangama warwewa ba,su axad dake basu taba zuwa nan yola ba,mamaki ne ya cika su da suga irin tarin gatan dana ke ciki a wajen familyn mahaifiyata,kawu na nan sunan sa kawu alhj ibrahim bankudi shi aslin cikin birnin yolan yake sauran ne suke can cikin kauye,shi arzikin sa na gado ne,kudi kamar kwarkwata haka suke yanyame da shi,a 480million worthh mansion muke zaune shine ya nema min aikin da kawu yamin magana akai,dansa daya dayayi aure yana zama a abuja,anan yola daga matar kawu sai ni,babu gatan da babu anan gidan azad yanzu ne ya ke dada fahimtar behaviur dinsu akan kawu game da rike ni awajen su,babu tantama sun fi kawu arziki,shi kawu ibrahim yanzu haka ma yana daf da zama daya daga cikin manyan kasa wato stakeholders wanda inbabu su kasan ma bazata juya ba.

But i still felt alone witou mama nd kawu xain,damuwar har yakan nuna a fuskata hakan ya dada sawa axad be same daman gaya min full jist din abunda ke faruwa ba,but im happy to knw that asad gafarar kawu ya soma nema a a rayuwar sa...hakan yana daya daga cikin burina duk dama bana jin sa araina yanzu

Bayan sun dawo kano azad be wuce gida ba sai ya kai fatima gida inda ta nace sai ya gana da mahaifiyarta hjiya salma

Shikuma Asad be dawo ba sabida cike exams din semestern da carmilla ta bata mashi a baya,so shi exams biu dama ya shirya ma,shiyasa kowa ya gama ya tafi amma shi sai yau ne yake graduating dinsa

azad yaji ddin yadda mahaifiyar fatima tabi da shi so diplomatic komu a mutunce,koda suka fito shaukin ya furta mata yana son fatima shi ya debe sa,so babu wani bata lokaci ya bayyana mata sirrin zuciyar sa yana me kafa hujjar sa mafi akasari akan dabiun ta,direct ya sanar da ita auren kawai yake muradi..
Tunda dama ta gama schl ynxu,fatima was more than hpy to hear that amma kuma sai fargaba ya hana ta amsa shi fa eh ko a'ah..bayan la'akari da soyayyar nasu kwata kwata befi wata guda  da satikai ba,ga shi har yau in tagan sa bata iya dena tunanin yadda dan uwansa Asad yyi wasa da zuciar nadra,..haka suka rabu ya dawo gida yana fama da tunanin yadda fatima zata fahince shi,for him it was love at first sight,mata fayawa sun bishi a egypt amma be taba jin shaukin yy soyayya ba sanda ya soma ganin fatima,horn yy abakin gate aka bude masa ya shiga tare da sauke ajiyan zucia yace anyways
Its fair if fatima is scared,babu lefin ta intayi tunani dan kare zuciarta shikansa yasan bakowa bane zai iya hkrin nadra akan Asad ..aransa sai yy mata uzuri

Kafin ya shiga wajen su mama sanda yaje dakin sa yay wanka y refreshing kansa,bayan ya shirya tsaf sai yy dialing number fatima dan ya jadadda mata yayi mata uzurin ta dauki duk lokacin daya dace don yin tunani akan maganan auren su shi yana nan zai jira amsar ta..yana cikin wayar sai ga Asad ya shigo ce masa yy ya fito suci abinci dake shima ya sa kansa dawowa cin abinci da su a main hous a dining table.

Asad yanajin yadda sukayi sallama da fatiman so romantic aransa sai ya kyabe baki be de ce komai ba,Tare suka sauko kasa in ka gansu komin su iri daya gwanin sha'awa

Azad ya zauna gefen kawu yana masa bayanin tafiyar sa wajen nady asad kuma yana gefen mama yy shiru,anan ana daf da kammala cin abuncin sai ga kirar nadra,bayan sun gaisa da kawu take dada masa godia tana kan basa hakuri akan duka abubuwan da suka wuce kawu yana faman sa mata albarka,mama aje spoon tayi tana ta bin sa da kallo cikin Allah Allah wayar ya iso hannun ta..

Aikuwa yana bata nadra ta soma mata magana tana  kukan tsaban kewar
Su datakeji aranta,gaba daya hnklin mama sai ya dada tashi,a rude ma take maganan sai lallashin ta yake kamar zatayi kukan itaman,azad yana kallon su duka yana murmusawa Asad kuwa ko abincin bakinsa sa  bai iya hadiye wa ba sai yyi lumui kamar maraya ya maida kansa kan plate din a slow yana juya fork aciki...mama sai ta shiga da wayar daki suna kan magana,da alama bata so aga hawayen tane wannan karon

kawu ya soma tambayar azad ko akwai matsala ne nadra take kuka,sai yace da kawu babu komai kawai kewar ku takeyi da wutsiyar ido Kawu ya dan kalle yanayin yadda asad din yake fighting da numfashin sa duk yabi ya rude agaban su batare da ya sani ba,kawu sai ya ruko hannun azad yana me masa alama da idanun sa akan duk abunda zai fada kar yace A'a"tare da sauke gyaran murya yace azad da alama Nadra bazata iya zaman can ba,amma ba damuwa ni zan kira ta inji ra'ayin ta,inta amince kai saika aure ta in yaso ko a ina take ai bazata taba jin mun rabu da ita ba ko?..saurin dauke idanun su sukayi akan yadda asad ya firgito idanun sa akan su,azad yace aaa baba ai bakomai ba amma ka tanbaye ta din,in hakan ya mata shikenan nima zanyi tunani.

Kawu ya murmusa yace ah'a kaima kaje kay tunani kam kaji shin kana son ta?nasan nadra baxata kimin ba,yarinyace me biyayya da sanin darajar iyaye...ni zanje ciki kuce da maman ku ta kawo min wayata yanzu..

Azad yy murmushi yace toh sai ya mike ya je kiran mama shikuma kawu ya nufi dakin sa,azaune durus kamar kungi suka bar asad yama kasa kai maganan kwakwalsa.

Ai yana jin saukowar Mama da azad ya tashi a hujajan yabi bayan su zuwa site din kawu,mama tace ga wayar kuyi sallama kawu yace aaa tsaya magana me muhimmnci zamuyi,"dakin sa shima ya nufa da wayar sanda ya gamma fahimtar da nadra sannan ya dawo..ya sa a handsfree,yace yawwa yata nadra,nan ya shiga wa'azi cike da salo irn na manya yana nuna musu faida da  darajar dake cikin kulla zununci,yace me zai hana mu hada auren ki da dan uwanki azad kwanan nan xai koma egypt kinga aikin ki ma xai fi miki sauki daga can,duk sanda xaki zo ai nan gida zaku sauka ko?,ai kuwa babu tantama nadra
Ta ansa tana cewa ta amince ai kawu yafi karfin hakan awajen ta,Kawu yy hamdala ya sake  nitsuwa yace yata ba dole bane fa sugestion ne,in akwai wani kiyi tunani akai,atake nadra tace a'a yanzu kam babu kowa a zuciarta
...Yace to xamu de baku dama ku dadayin tunani,nadra tace itakam ta gama amma zasu jita azad ya yanke hukunci"aka tambaye azad yaji ko?yace eh...daga nan maganan ya tsaya sabida yanayin yadda asad ya fice a dakin a firgice kamar me aljanu

Mama ta mike tsaye cikin damuwa tace ban fahince ku ba azad xaa hada da nadra?,alhaj kasan yana son ta,itama tana son shi,koda yaki auren yyi hakan ne sabida atunanin sa kai kace mata ta aure sa ba araayinkan ta ba..dan Allah a sassauta masa asad yana cikin halin nadama baxe iya rasa nadra

Kawu yace zai iya mana tunda har yau ya ksa budan baki ya fadi abunda ke zuciar sa,inde wai akan haka ne karki damu shirya shi mukayi dan yy saurin cire kansa a wannan danuwar dake cinsa,ki duba kiga yadda ya rame
Ya lalace,abincin arziki bai iya kaiwa bakin sa,wai sai yaushe zai dawo mutum? Mama tace kayi gaskia inde haka ne nima zan tayaku..anan aka bar maganan duk suka watsa

Asad dakin sa ya nufa yana ta ziriya shika dai yana jeka ka dawo cikin damuwa,ana turo kofar ya dakata ya kure kofar da ido,azad daya gansa gaba sanda yji daria sai ya fuske ya karaso ciki kamar zai zauna sai yace me hakan kake wani diri kamar me ciwon nakuda

A fusace asad ya tunkude sa,yace ashe kau mayaudari ne?Azad yace mayaudari kuma me hakan?,kara ture sa yay a fusace yace meyasa xaka ma ce zaka aure nadra bayan kasan zata iya amince ma masu baba?ita
..fatiman fa?hada su xakayi?mayaudari....azad ya mike tsaye yace karka sake cemin mayaudari,ni ban yaudari kowa ba,nadra ce ta amince zata aure ni,nikuma yanzu haka tunani nake yi...i want to be sure
In zan iya zama da tsaddaitar mace irin ta..u knw she dersv a king..someone better..

Asad ya balla masa harare cike da masifa yace nace fatiman fa?hadasu zakayi ..answer me

Azad yace wai ina ruwanka ne?yace akwai,nadra is mine
Kasani...in banda walaknci mesa bazakace baka son ta ba

Azad yace nina ce maka banson ta?

Yace eh ai nasan fatima kake so ko in kira ne atambaya, mayaudari..

Azad yace eh ka kira,ka kira ma ko zakaji dankunnen ka cewa fatima ta ki ta amince da batun aure na ne sabida tana tsoron abunda kayi ma nadra,she still feel we r the same,i wll hurt her zanyi wasa da feelings din ta kamar yadda kayi da na nadra,so i lost fatima bcos of you..

Asad Yace karya ne,dama ba sonka take ba,bata san mu yan biu bane?..ai tasan kai dani ba daya bane...What nonsense excuse kawai tace bata son ka amma bawai ta kafa hujja dani ba

Axad yace akan me bazata kafa hujja dakai ba?nide banga lefin ta ba,ai kaima kafa hujja kayi da baba ka bata maganan auren ka da nadra,so dont u dare blame my fatima..bcos i still love her,amma hakan zan yi hkri nayi tunani akan auren nadra kuma in Allah ya yarda nadra zan aura...i cant force fatima to marry me if she feels i wll hurt her like u hurt nadra,kaine silar lalacewan komai da kaso da kar kaso hakan ne..so wl u excuse me?i hav alot of thinking to do

Wani tsawan bacin rai da tashin hankli asad ya daka masa kamar wanda xae yi fitsari,amma axad be ko kulasa ba ya nufi bakin door,yace wallahy baxaka aure ta ba..nadra is mine..i love her..u cant take her away from me sede in kashe ni zakayi..

Azzzad ya share shi ya rufe door ya bat sa anan yana ta fade fade kamar mahaukaci sabon kamu

Haka Asad ya dau fushi da kowa,azad ma sai yaki ya bisa a hankli duk sanda suka gamo da juna sai anyi zaxxafan muhawara akan nadra,azad da dumi dumi yake tuno masa yadda yayi wasa da damar sa na farko,ta inda yasan ze taba masa zucia,worst part su mama da kawu ana xama cin abinci zasu fara tambayr azad ya yake ciki ne?har yau beyi shawaran bane,wasa wasa asad sai ya fara nuna musu borin sa a fili daga an fara maganan sai ya aje spoon ya bar kan dinning,daga nan kuma husuma ne xai tashi tskanin sa da azad a daki,har yakai ga azaad yace dashi nan da kwana biu zai gaya ma kawu ya amiince da auren nadran tunda abun masifa xai dawo musu shi zai tafi da matar sa egypt,abun duniya yabi ya ishe asad,yayi fadan har kuka sanda yy ma mama amma duk abanza itama ce masa tayi bata da ikon in azaad yace ya amince dama ai shi kawai ake jira.

Sanadiyar firgicin sa mama ta ma san azaad yana son fatima bugaje amma hakan suka cigaba da koya ma asad hankli

Asad dayaga abun bana zucia bane sai yay tunanin ya lallabe azad ko xai fahince sa

Axad yana kwance a dakin sa a mainhouse sai ga shi nan,kamar me iska ya hau kujeran sa ya zaun ya nistu.

Idanu Axad ya zuba masa,yace miye?
Yace azad magana zamuyi fa..yace ok inajin ka amma in akan nady ne kayi hkri mubarsa kawai jefo masa wayar sa yy yace kagani i just called her nagaya mata jibi zanzo yola
Muyi maganan face to face dan mu dada amicewa da juna,bana son na dau abun nan da wasa,"so wannan kenan, any oda thing?wani kuka asad ya fashe masa da shi ya rikito kasa..yace azad dan Allah ka rufa min asiri wallhy zan mutu in na rasa nadra...

Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top