chapter9
Dearies kubi labarin nan a hankli its long story u shall expect the unexpected....
BISMILLAHIRAHMANIRAHEEM.
Part1:chapter 9
Destiny At fault.
9.30am:ivy cottage U.S.A.
Hasken ranar da ya hudo windown dakintan ne ya sata bude idon ta a hankali..
ranan da ta gani ne ya sa ta wara yan madaidaitan idanuntan ta dubi karamin agogon dake kan bed side drawer taga har 9:30, da tsalle ta sauko daga kan gadon gashinta mai tsayi da cika da ya barbaje tana bacci ta kama ta hade su in a messy bun sannan ta sauko
toilet ta nufa ta kuskure bakinta da mouth wash tayi maza ta tube kayanta sannan ta kunna shower tana mai sake ma jikintan ruwan sanyi, can ta fito daga wankar bata tsaya yin wata wata ba ta maida kayan jikinta tsaf kamar yadda tasaba Dan dama sukadai ne gareta bata da Wani kaya.
Daga Nan fridge din dakin ta bude ta dauko ruwan sanyi ta sha kadan sai ta mayar da gorar shima ta ajiye,Wani nannauyan Ajiyan zuciya ne ya kufce mata mai alaman dawowa da Ita cikin hayyacinta,Dan juyowa tayi tana shirin komawa bakin gado caraf sai idanunta suka ci Karo da Wani faranti a lullube da farar wrap da alamar abincin ta Aka aje mata kamar dai yadda aka saba yi a kullum
Gaban abincin ta nufa ta bude wrap din a hankli tana kallon abunda ke ciki,normal chips tagani da omaletes saida wani abu kamar sandwiches a dukunkune Agefe
She is very hungry saidai gaba daya abun duniya ya dame zuciyarta sai taji kwata kwata ma kamar bata sha'awar cin komi,yau kwananta 7 kenan da zuwa Nan akoyaushe tana kirgawa Amma Koda sau daya ne ba'a barta tafito ba kuma shima mijin nata baizo mata ba...
Tunda wancan matar ta kawo mata abinci da toiletries a ranar farkon zuwarta daga Nan sai bata kara ganin Wani halitta da idanunta ba,ita dai zama kawai takeyi cikin rasa yadda zatayi da rayuwarta,gashi ita ba son magana takeyi barema tace zata tambayesu Inda Alhajin yake,but now dataji ta a matse she is really feeling ready nd eager to ask Dan zaman kadaicin Nan sosai yafara razanata,she is nearly depressed alone,babu waya babu tv,daga gado sai wardrobe da Dan fridge wanda batama sanin lokacin da ake kulawa dashi,most time saita farka daga bacci ma take ganin an sasaaka mata drinks da ruwa an jona mata Duk Wani abun datake bukata.
For the past 7 days bata San wayake kawo mata abinci ba,and she only get to eat food 2 times a day, da safe da kuma yamma,yanzu haka Da wuya in ba sanda takoma bacci bane aka shigo aka aje mata wannan abincin,Babu mijin nata babu waccan matar sannan bata ganin masu kawo mata abinci.
A Yadda tayi tsammanin gidan mijinta shine daga tazo zataga mata biyu da yara da kuma ango mai dokin amaryan sa
But none of this have happen yet
Abubuwan mamaki ne kawai yaketa faruwa da ita Dan Sam bata gane ina rayuwan ta ya dosa ba,is bcoming clear to her dat she is being treated like a hostage,kamar wacce aka Sato ta za'ayi Wani abu da Ita.
Dan daga tazauna tunani babu abunda take juyawa aranta sai yanayin rayuwarta anan din, komi sounds really odd and strange Abinci sau biyu arana,daki kullum a kulle and no one is visiting her bare ajega bata waya.
Ayanzu Komai mamaki da tsoro yake bata
Haka kuma rayuwanta ya kasance inta gaji da bacci tayi kuka inta gaji da kuka ta bude window tayita kallon waje,gashi da akamar anguwar babu kowa Dan takan fi awa uku tana kallon kasa ta waje Amma bata ganin wulgawar kowa Sai daidaikun motoci...
Idanunta is alwys wet,jikin ta Kullum a nannade yake da hannayenta kamar maijin sanyi,she look so pale and agitated tamkar wacce ciwon depression yake shirin kamawa..
A dan dolenta ta zauna ta Dan taba chips din batama wani ci dayawa ba ta miqe tsaye tayi bathrum ta wanke hannunta da bakinta sann ta fito.
Gadonta ta koma ta dukunkune kanta a gefe guda,addua babu wanda batayi Amma still ji take kamar ta kashe kanta tsaban batajin dadi rayuwa
She is sooo lonely frustrated and depressed at same time,Kullum takan runtse idanun ta tayi shiruuu na tsawon lokaci wai Koda zata danji nitsuwa saidai bata iya bude idon shikansa face zafafan hawaye masu azaban radadi da ciwo sun kassara shi
Babu irin kokarin da batayi danta cimma burinta na ganin mai kawo mata abinci,Wani bin haka zata hana kanta bacci tana gadi Amma Duk abnza so take lallai ta tambayesu shin ina mutanen gidan kuma meyasa ake kulleta Amma Ina haryau dai bata taba cin sa'ar su ba
Bayan kwana biyu da taga abun babu ci saita hakura kawai ta shiga maimaita bitan karatun qur'ani iya wanda tayi hadda ta maidashi daily routine sabida tana tsananin bukatar abunda zai daidaita mata tunani ya kuma kubutar da Ita daga haukacewar da kwakwalta yake so yayi.
Haka Rayuwanta ya kasance harna tsawon sati biyu babu Wani canji,ranar tana bacci kwasam saita somajin Wani irin motsi motsi da kara kara,cikin sauri ta farka tare da bude idanunta a mugun razane saidai bata kwatanta kunna wuta ba Jin kamar ba daga dakinta motsin yakeba saidai tabbas tasan motsin agidan Nan ne..
Wani lumshe idanunta tayi Jin yadda kirjinta yake tsanata bugu,Dada Kasa kunnuwanta tayi nadan wasu lokuta can ta soma juyo muryan mutane da kuka kuka abun dai gashi nan gaba daya bata gane meke faruwa ba,ta dade ahakan,cikin yanayin dauke numfashin ta cak,a hankli ta sauke kafafunta akasa cikin sanda ta iso daf da baqin kofa, tsaye tayi abakin kofar na Dan wasu mintina tanakan jiyo sautin ihun,sai can kafin tafarajin shiru daga Nan saita bata kara Jin motsin komi ba..
A haka ta kwana cikin tsananin tsoro da razana baccin ma gaba daya kasa yinshi tayi,washe gari ma haka ya sake faruwa,haka ta rinka Jin ihun da motsi,hakama next day,har sanda ta soma jin ihun da akeyi ya Dan matso kusa a daf daf da ita kuma tabbas tagane cewa ihun mace ce wanda take cikin tsananin bukatar taimako
Tunda take arayuwarta bata taba sanin cewa tsoro da razana kan iya saka mutum fadawa ciwo ba sai akanta,Dan tunda wannan ihun ihun ya farayin tsanani sai ta somajin kamar zazzafar zazzabi ne yake ta shiganta, aranta gani take kamar gidan yankan kai kawai aka kawota za a yankata ne sai ayi kudi da Ita.
Kukan datayi a satin nan Allah ne kawai yasan adadin sa
Addua da neman taimakon gaggawa babu wanda batayi shi ba,and each time she tried to open d door sai tajishi gam gam da alamn ta waje ma ake kulleta
After 2 days kwance take akan gadon tan ta dunkule jikinta a waje guda da alaman Wani azaban zazzabine mai tsananin zafi ya shigeta harya yake hanata iya miqewa..
Ga abincin yau da na jiya duk bata samu taci ba,she was soo weak harta sallame barin duniyar kawai Gani take kamar zata mutu,cikin wannn yanayi after like 2hrs ta fara bude idanunta da sukayi jaaa tsaban ruwan dake fita aciki,ji tayi kamar ana taba kofar da alaman motsin mutum cikin axama ta ware idanunta,Jim kadan matar Nan ta shigo wanda hakan yasa ta miqewa zaune batare da ta kula da yanayin zafin ciwon bama,Tun kan matar tayi mata magana Wani rusashiyar kuka ne ya kufce mata..kara fashewa tayi da Wani irin kuka mai tafe da tsantsar razana tace "malama Dan Allah ki fitar da ni daga nan,na hadaki da Allah ki cece ni,pls ni zan koma gidan iyaye na...kallonta matar ta cigaba dayi can ta basar tace "magani akace in kawo miki,"tace waye yasan banda lpya bayan babu nake gani yake shigo min?koke ce kike kawomin abinci?toh meyasa zakuna kulle ni,am scared...please..where I'm i? ihun me nake yawan ji da daddre?ina shi mai gidan Dan Allah,
ihun mace fa nake ji kamar ana yankata,pls who are u ppl...
Da sauri matar ta matso kusa daf da ita cikin toshe mata baki da alamar bataso ta kara furta Wani tambayar
,shhhh ta furta tana kallon cikin kwayar idanun rufaidar da pleading eyes da alaman tanajin tausayinta sosai,but it's seems like thy are being watch in a control room,matar tana sana da cewa Duk Wani motsin su ana kallo.
Cikin sigarr rarrashi ta Dan shafa kanta still bata ce mata uffan game da tambayoyin datayi mata ba,maganin data shigo dashi kawai ta bude ta miqa mata tace mata tasha,a Babu yadda ta iya ta amsa ta sha din, daga Nan ma amai ta dingaji daya tsananta mata sai ta mike ta nufi toilet kafin ta dawo tazo ta tarar da dakin babu kowa alaman har matan ta fice abunta.
cike da sanyin jiki ta karasa zuwa kan gadon,kwanciya tayi a sulale Cikin tsananin rasa abunda ke mata dadi,Wani lumshe idanunta tayi cikin tsananin rudani tabbas yau da Ita ba musulma bace da tuni ta yanke hukuncin kashe kanta kodanma ta huta da azaban rudanin datake ciki
Haka tayi ta zama acikin wannan yanayin,by 7pm ta shiga alwala tazo ta samu har an aje mata abincin ta,kwata kwata bata iya ci ba haka ta dinga kwaxa amai, da misalin 10pm na dare,tsantsar azaba da gajiya ne yasa bacci mai nauyi ya mata bazata bacci ya dauketa,Wani irin juyi take cikin baccin daga Gani kasan ba dadinsa take ji ba,after like 30 mint Wani sabon ihun ya tayar da Ita..
A mugun razane ta farka rike da kirjinta dayaketa bugu kamar zai fita bakinta dauke da kalmar innalillahi wa inna ilaihi rajiun..
"Wayyo Allah na..
Wayyo Allahna
Sai kuma numfashi da uban nishi mai mugun tada hankli da kada ruwan ciki dayake biyo baya.
As usual jikinta na rawa rawa ta iso har bakin door din ta kasa kunnunwanta
Tana dada Jin ihun
Zama tayi abakin kofar ta jingine bayanta kadan tana kkrin cusa kanta a tsakankanun cinyiyonta Jin tsabar yadda zuciyarta yake bugawa da azaban tsoro..
Dan kadan ta motsa jikinta da alamar tana shirin gyara zamanta sai kiiiiiiiiiiii taji alaman budewar kofar a mugun firgice ta miqe tsaye tamkar wacce zatayi tumbul taci da kasa Tabi Ta matsa da mugun sauri tayi can da baya
Wani irin bugun balai kirjinta yake sai diffff difff diff numfashinta yake sauka kamar wanda zai dauke gaba daya,gani tayi kofarta ya Budu kadan Amma har yanzu babu wanda ya shigo ciki,tafi mintina arbain cikin tsananin tsoro tana tsaye tana ta kallon kofar,ganin kamar babu motsin kowa anan kusa yasata tayi mastering courage da kyar ta fara karasowa gaban door din ahankli a hankli...
Tafiya take tanajin yadda bugun kirjinta yake mugun karuwa,tsayuwar cak tayi a bakin door din dan da kyar take iya motsa hannun ta dake famar rawa Kar Kar kamar wacca aka zubawa kankara
Lekawa kadan tayi ganin babu kowa yasata taji relieve,sai ta dubi kofar da kyau, da alamar tun safe da matar Nan tazo fita ne ta manta ta barmata kofar ahaka a bude,she dnt even notice,sai taji Wani irin haushin rashin sanin Hakan ne yakamata,ai da tuni ta ficce waje ta nemawa kanta hanyar guduwa agidan saidai Duk abunda zai faru ya faru...
Kara lekowa tayi ahankli tana famar zaro idanun ta waje Wani zuru zuru tayi da idanun tamkar wata babban barauniya,cikin dabara ta sulalo jikinta ajikin kofar ta fice dama ta dade da burin son sanin me ake aikatawa ma mata agidan Nan kuma Nan din ma ina ne?sai kawai ta yanke hukunci aranta cewa koma menene ma ita guduwa kawai zatayi..
Tafiya ta somayi a sulale tanamai maida hanklinta ga Inda tafiye Jin waccan ihun,Wani irin tsorone yake kassara mata gabobin jiki,ko inanta karkarwa yake Amma Sam bata fasa ba,thank goodness kafafunta babu takalma bare ajiyo Wani motsinta
Kimanin kofuna 5 ta wuce wanda taga dukansu irin nata ne wanda take ciki saidai harta wucen bataji motsin kowa ba,tsayawa tayi cak a kofa na shida Jin yadda gabanta yayi mummunan fadi,daf kofar data tsayan taji Wani abu kamar alamar motsi motsi
Firgita tayi Kamar dai zata je jikin kofar atake sai taji kafafunta sun mata nauyi,ta dade a Hakan sannan tayi mastering courage ta karasa daf da daf,hannun ta dake rawa rawa takai jikin kofar sannan ta aje kunnen akai tana jiyo sautinsu haka ta dinga jiyo me ake cewa
"It's a gang rape"..
"Wayyo Allah, gabanta ne ya wani irin bugawa da tsananin qarfi,take kanta yayi kara kamar wanda aka dandatsa mata shi da katon guduma..
Dauke numfashinta tayi chak ta kuma yi tsitttt tana kan Jin conversation dinsu,wanda sukeyinshi cikin izgili da mugunta can ta shiga girgiza kanta a firgice tuni idanunta suka kawo ruwa cikin ranta tace..."Ciniki?
" siyar da Ita?
Innalillahi Masu siyar da mutane ne
Bata masan lokacin data janye jikinta daga jikin kofar a mugun firgice ba,daga kafafunta tayi alaman zata bar wajen Wani azaban karane ya razanata mai dauke da tsananin ciwo da azaba wanda ya fito daga cikin dakin,tunma kafin ta sauke numfashin ta dake shirin barin jikinta kafartan ta yaja ta da jiri ta fadi tim akasa,tabi ta tashi agigice,...."kuyi min rai". ...Dan Allah ku kyaleni...wayyo Allah na..na shiga uku...mutuwa zanyi
Dan Allah kubarni
Wayyo Allah na shiga uku..Allah ka dauke raina in fita daga wannan azabar
A rikice rufaida ta soma ja da baya idanunta sun wanke fuskarta da uban hawayen tsoro sautin ihun ya gama cike mata kunnenta da kwalwakta,itama ji take kamar ta kurma ihun saidai bazata iyama bude bakinta ba sakamakon barin dayakeyi karkar,da kyar ta miqe tsaye
Cikin tsananin sauri ta juya ta cigaba da tafiyarta gaba cikin neman hanyar da zata tsiratar da kanta gaba daya hayyacinta baya jikinta
Batako yi nisa ba tasoma jin alamar wani motsi,tsayawa tayi cak,zuciyanta na difff difff ji take kamar kurwanta zai fito waje,Jin kamar mutum ne yake shirin tunkarota yasa ta Firgita ta deba a guje saidai bata iya tantance inane kofar dakintan ba,Nan danan ta mannu da bango cikin tsananin razana ta dauke numfashinta gaba daya,ji kawai tayi an finciko ta daga Nan sai bata karasanin meya faru ba sai washe gari data farka ta tsinci kanta awani rufaffen daki a shimfedeta akan gado..
A hankli ta shiga wara idanuntan da suka kumbura sukutum sukayi Wani luiii da su tamkar na wacce take shirin gangarar mutuwa.
Gabobin jikinta da zuciyarta gaba daya sun nakasa da azaban razanar datayi ji take kamar ta dauke numfashinta ace mata batama duniyar..
Saidai ganin matar Nan akanta datayi ne yake shirin daidaita mata hankli,da kyar ta iya bude bakinta sautin maganan ta ya shiga fita a karkarye
,"k .u..yi ha..k..uri
Da..n Alla..h kuyi hak...uri,wallhy ban muku komi ba..
Ku kyaleni na tafi gidan mu,wayyo Allah na umma na wayyo umma na shiga uku wallhy kasheni zasuyi..
Matar batace kala ba saima kallonta datakeyi ganin bama a hayyacinta take ba.
Wani irin kukan azaba da tsananin razana takeyi jikinta na tsananin karkawa,da dukkan zuciyarta take kukan tana magiya tana mai rokon amata rai..
Can matar ta taho kusa da ita,batare da cewa komi ba ta dagota ta zaunar da Ita,kallon 2 snds ta mata sann..tace
"..Ke, kiyi shiru...ina rufaida bata ma gane me ake furta mata kukan kawai takeyi
"Ki yi shiru mana
Wai so kike akamaki?
Shirun tayi atake sakamakon tsawar da matar ta daka mata
....
Dan shiru tayi sannan ta kara fashewa da Wani irin razanannen kuka mai tsuma zuciya da karya garkuwan jiki,ta cigabayi a hankli,
can sama sama numfashinta yake harbawa kamar wanda zata shide, sheashekarta ma da qarfin sa yake saukowa Dan hatta idanunta bata iya budeshi tsaban yadda ruwan hawaye ke ambaliya akan fuskartan yana gangarowa
,cikin tsananin rawan Murya da azaban razana ta kalle matar da Wani irin salon magiya "Please I want to go home ...
Dan Allah ki fitar Dani anan
Ai..ai...ai naji abunda akeyi acan dakin,sanda ta Wani jaaaa nunfashi ta kara fashewa da kuma sannan ta cigaba wallhy
Bana son ayimin fyade,ni ban taba kwanciya da namiji ba,and
..and..Its asif it's a gang rape,Bayan Nan kuma naji sunce sayar dasu kukeyi Nima kenan Haka za'ayi min?
Na roke ki da girman Allah ki fitar Dani agidan nan
Inkinsan darajar iyayenki ki taimaka min,Ni Wallhy tsoro nakeji,Hala ma mutuwa zanyi ko..kukan ta cigaba da yi asif she is crying her last tabi ta rude gaba daya,kallo daya matar tabita dashi sann ta dauke kanta ta miqe tsaye tana mai cigaba da kallonta cikin Wani yanayi mai wuyar fassara,A hankli Tace ki saurareni yarinya ki fahimce cewa Anan babu mai kubutar dake,saidai inkika bani hadin kai zan iya taimaka miki,Jin Hakan yasa rufaida ta miqe tsaye itama tana bin matar da kallon rudani
Tace.."babu mai kubutar dani?,hawayen da suka makale a idanunta tuni suka gangaro,sai tayi sauri ta sulale kasa kan gwiwarta
,"Dan Allah ki tausaya min,kefa mace ce,ya zakiji in akace ni yarki ce ko kanwarki ko wata yar uwanki?ki duba halin danake ciki,Dan Allah ki fitar Dani a gidan nan na koma gidanmu,"..kiyi min rai ki taimakeni na koma wajen umma na..
Matar ta taso Adan kufule nace
Bakiji menace miki bane? ta tambayeta sounding pissed Rufaida tana shiru bata dagoba tukun ta cigaba da kukanta kanta akasa,a hankli ta shiga kakkame jikinta ta mamaye kanta cikin wani yanayin kunci gwanin ban tausayi,can Matar tace"I'm willing to help u but you have to cooperate..ki dena wannan kukan naki Dan baida amfani, kisa aranki cewa Babu yadda zakiyi ki kubuta anan gidan,Kisani Duk Inda kikayi ana kallonki,ko yanzu ma sunsan Inda muke inma baki sani ba..Kuma yanzu haka ina mai tunasar dake cewa kin jefa kanki ne acikin babban barazana, meya fitar dake a dakinki?
Anan Rufaida ta dago kanta da kyar cikin shesheekar kuka tana famar girgiza kai tace
...NI fa Guduwa zanyi..
Wani Dogon numfashi matar taja tana kan kallon ta very closely...
Ganin yanayin ta da abun tausayi,d girl is absolutly terified ita haka kawai taji aranta tana son taimaka mata
Kofar fita ta nufa ta dan leka waje kadan,tafi 5 mints awajen abkin kofar sannan ta kulle kofar da keys sai ta dawo ciki cikin sauri,zama tayi a Inda rufaidar ta kife kanta da gwiwa babu abunda yake tashi sai sautin kukan ta da saukar numfashin ta mai qarfi.
A hankli ta shiga shafa mata kai sannan ta soma peting bayanta tanamai rarrashinta batare da tace mata uffan ba..sunfi minti goma haka Amma babu abunda ya sauya a bangaren rufaida kuka kawai take zuciyarta cike da ambaton Allah
"Wani Huhhhhhm matar ta sauke Ajiyar zuciya da kamar bazatayi magana ba cen kuma sai tayi
Tace
Yarinya mai sunanki
Da kyar rufaida ta Dan dago tace
Sunana rufaidah
Idonta taf da ruwa Tace Allah sarki rufaida..
Toh ke Meya ya hadaki da Mutum kamar alhaji bature
Har kika yadda kika aure sa wato Kinga kudi ko?rufaida tace.."A'a...ta dakatar da ita cikin sauri da iya gaskiyar dake cikin kwyar idanunta,"nifa ban sanshi ba,ko ganin sa bantabayi ba,wallahy mahaifina ne yayi min auren dole,kuma haka yay ma sauran yayu na..
Runtse Ido matar tayi sannan ta bude a hankli
"Auren dole?
Kina nufin bada son ranki kika zonan ba?..gyada mata kai Rufaida tayi, da sauri"..I'm sorry..matar tace muryanta dauke da tsananin tausayin ta
Nan ta gyara zamanta tana duban ta very closely,.."Tace,
Yawancin matan da kikejin ihun su anan gidan mafi akasari kwadayin su Dana iyayensu ne ya jefo su...To ke maisa iyayenki basuyi bincike akan alhaji ba?kinsan shi waye kuwa?...cikin karajin mummunan fargaba rufaida ta girgiza kanta tace A'a,ai shi baba babu ruwansa,baiya bincike,cikin jinjina kai matar tace tabb
"Toh Alhaj bature da kike gani shi asalin tsohon Dan safara ne.,rufaida ta dago a rude "bangane ba?safarar me,matar tace ina nufin Baida Wani sana'a a rayuwansa daya wuce saida mata da yara kanana,wanda za'a na sana'ar karuwanci da su Dan ana kawo masa kudi,Duk wanda ya kawota Nan to sana'ar da zaa dorata kenan,kuma babu mai kufcewa Hakan,in harma jininku ya hadune ya turaki aikin bauta agidan wasu ko kasuwa ko kamfani depending on wanda zai siyekin..
A mugun firgice rufaida ta miqe tsaya Jin abunda matar ta furta wanda yake barazanar buga mata kwakwala
Magana zata furta matar ta miqe tsaye cikin dakatar da ita da Wani irin yanayin warning a muryanta
Tace" don't even try it,He is very wealthy and well connected,har cikin jamian tsaron kasar nan yana da ido da kunne,a Duk Inda kika shiga saiya sa an kamoki,shiyasa ma nake gargadin ki daki kama kanki ki nitsu tun kafin ki jawo ma rayuwanki kisan wulakanci da axaba
Dafa kafafunta tayi ta juya da Ita Suna fuskantar juna
"Ai kinji irin ihun da sauran matan sukeyi ko?If u dare try to run away,zai saka kattin maza su dagargaza gindinki till ure numb,inkina da rashin kunya da taurin kai kuma su kara maki da duka in most cases thy will use electric shock on ur vagina inbaki iya riqe azabar ba ahaka zaki mutu aje abawa karnuka namanki suyi bidiri.
So now will u cooperate or no?
No votes nd coments?aradu nima na tafi hutu..
Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top