chapter 20

IN BAKU GANNI BA NETWORK NE COS IM NOT IN TOWN PRESENTLY.

BISMILLAHIRAHMANIRAHEEM.

Part1:chapter 20
Fear...


By 7.30am imad ya dawo cikin asibitin hannun sa dauke da ledojin abincin daya siyo yana famar tafiyar sa cikin sauri batare daya kula kowa ba ya wuce direct har cikin dakin datake kwancen samu yay bakowa anan face rufaidan datake kwance ita kadai akan gadonta yau ko respirator ma ba asakaya mata ba da kallo daya yabi lumsashen idanun ta wanda suka bada alamar cewa yanzun Nan aka kullesu,ajiye ledar abincin Yayi  a saman table sannan ya karaso har Gaban ta ya tsaya Daga gefe haka yana ta kallon rufaffen Idanuntan dayake famar shaking Duk ta kasa aje hanklinta waje daya,ko Wani motsin kirki bata son taga tayi hatta numfashinta ma da kyar tabarshi yake fitowa,Wani irin nauyin sa ta soma ji aranta Sanin cewa bata taba sanin sa  arayuwarta ba she is a bit confused about him, kunyarsa da tsoron halin datake ciki shiyake bala'in son ya rikita mata hankli da tunaninta ayanzu

Suna Cikin haka wayarsa yay kara Babu jira ya dauka ya sa akunnen sa ya fara magana, jin ya amsa kamar wasu ne zasu taho yasata Kara Lumshe idonta Dan haka kawai taji aranta kamar bata son hakan ya afku,she wish dat shikadai ne zaina kulawa da Ita basai wasu sunzo ba Duk tunanin ta ko wayanncen polisawan ne zasu Kara dawowa su isheta da tambaya gashi ko kadan bata son jin Sunan Alaji Bature a kusa da ita bare ma aje ga jefa ta cikin halin tuno da kanta acikin mummunar rayuwar datayi a kwanakin Nan.

Sosai take kokarin binne damuwarta
Aranta,tadai San bata cikin hayyacinta Sosai Amma Duk da Haka saida ta kasa ta tsare wajen hana kwakwalnta tuno mata da komi
Gani take kamar inta kuskura ta tuno Alaji Bature to Babu shakka zata farka agaban sa ace mata gamowarta da su imad mafarki ne.

Itadai Bata San meya afku ba bata San ya akayi taxo nan ba Amma tabbas jikin ta na bata cewa tsira tayi,Wani lumshe idanunta tayi cikin gode ma Allah daya kawo ta cikin wannan yanayin da bata taba tsammanin zata ci Karo da shi ba har abada,bata hankara ba taji kamar ana kokrin dagota,cikin  sauri ta bude idanunta wanda suke da haske,Nan take suka hade ido dashi,saurin sauke nata idanun kasa tayi ganin murmushi mai mugun sanyi  a fuskar sa,sirraran yatsun hannun ta ya riko cikin tsareta da sautin muryan sa mai taushi yace "hey..I'm back"..a hnkli ta dan dago kadan ta kalle sa,Kara hade ido sukayi saiya Kara yi mata murmushi yace "bari na shirya miki abincinkin ki ko sweetie?tun bata amsa shi ya juya ya shiga bubbude ledojin daya shigo dasu,nan ya hau ciro abincin komi ya shirya mata su in a clean disposable plates,wanda yasan daga taci zaa iya yarwa hardashi,
awaje daya ya saka mata duka abincin sabida ya fahimce cewa ba lallai ne ta fahimce abunda tafi sha'awar ci ayanzu ba,Dan haka ya debo shinkafar kadan ya xuba ya jejjera ganyen ya Dora chicken wings akai yabi ya zagaye jikinsu da namomin cikin pepper soup din komi daidai misali

Spoon ya Dora akai lokacin harta miqe zaune bayanta jingine da pillow Dan har cikin ranta take balain mararin qamshin abincin daya cikke iskar dakin da Wani nauin qamshn Dadi,a lokcin Idanun ta a lumshe suke Dan bata ma San harya kammala zuba mata abincin ba.

Tahowa yay da abincin har Gaban ta sannan ya zauna,ganin batayi motsi ba yasa shi yin gyaran murya atake ta bude idanun ta ta kalle sa tagan sa yana Murmushi,yace ur food is here,Tashi ki taba kiji..Wani kallo tamai sannan ta sauke idanunta kasa kan abincin ta kalla,ganin namomi ne kaca kaca asaman abincin yasa ta kulle Idanunta agaggauce,Wani zuttttttt Idanunta sukeyi, kanta ya shiga bugawa atake atake,Nan da nan kirjinta shima ya amsa da Wani irin bugu mai tsananin karfi, hotunan naman mutum dataci ranar shine ya soma bijiro mata a cikin kwayar idanuntan,tuni kwakwalta ya shiga maimaita mata Duk abunda ya afku da Ita,hatta ihu da Marin da Alaji Bature ya rinka falla mata a lokacin sanda ya shiga dawowa mata sabo
Wani buff buff kirjinta yake bada sauti,ta shiga tuna yadda ta rinka kwaxa amai tana kwakwale cikin ta tana kuka,gaba daya ta rikice agaban imad akabar sa da binta da kallo cikin tsantsar mamakin yadda ta rikice ta birkiice a lokaci guda,daf yana shirin daga abincin zai aje shi gefe rufaida ta razana ta daka Wani uban tsalle ta bangaje plates din komi ta tarwatse

Wani irin ihu ta fasa ta ja jikinta daga nashi tayi baya sosai...

Raxanar da bai taba ganin tayi ba shiya ya mamayeta atake atake ta sake mai wata matsancin sautin kuka wanda Ko iya Furta magana batayi baya baya kawai takeja akan gadon har sanda ta Gamo da karfen gadon ta dukunkune kanta da pillow tana girgiza kanta cikin rudewar tunani,miqewa tsaye imad yayi kansa a mugun daure yana mai kallon yadda hannunta yake pointing din abincin
Hannun nata yana rawa sosai,shima wajen yabi da kallo ya Kure abincin da Ido ko da zai dago wani abunda take nunawa Gaba daya sai yarasa metagani akan abincin da har yake raxana ta,matsowa kusa da ita yay zai yi magana ta Kara fasa mai ihu wanda yaji karar sa har cikin xuciyarsa
A mugun rikice Muryan ta yake rawa ta soma rokon sa cikin tsananta kuka da daburcewa
"Dan Allah kayi hakuri,Ni bana ci,ni bana ci,.. wayyoo Allah na kayi hakuri wallhy bana cin naman mutum..
Dan Allah karka bani..Tsayuwar chak yay Jin abubuwan datake ta furtawa Wanda bakaramin daure masa Kai sukayi ba ba Aransa yace"..naman mutum?,saiya tuno da cewa jiya fa an sasassamu part part din mutane a Gidan da aka tsince ta ranar, matsowa kusa da ita yay cikin sauri, daf da Ita ya zauna da niyyar janyota jikin sa Koda ma zata dawo hayyacinta,yana dafa ta ta Kara birkicewa ta tsala ihu ta hantsila ta diro kasa ta fado Tim kamar wata tababbiya,gaba daya ta manta da dukan ciwon dake jikin ta da mugun gudu ta miqe a gigice zata falfala da gudu tayi waje,da uban sauri ya tarota ta fado jikin sa ya kankameta cike da azaban damuwa,
shafo kanta yakeyi da dukkan imanin sa,da kyar ta sake jikinta anashi Duk dama yasan bata San metakeyi ba,a hnkli cikin taushin murya ya shiga tambayarta yana cewa meye ne?waye ne?Wani Lumshe Idanun ta karayi tana ta rabza uban kuka a hnkli Tana famar kiciniyar kwacewa daga garesa,hanklin sa ne yay mummunan tashi,Jin jikinta na Wani irin rawa rawa kamar wacce zata shide ta dauke ranta da kanta,a rararrabe  take sauke numfashi.tace."Dan Allah kayi hakuri...a hankli saita kuma kankame sa,shikuwa idanun sa is stiff a kanta yana ta kallon ta yaga dai haryanzu batama iya bude idanunta bare ta kallesa, da Dan karfi ya shiga girgizata yace"...rufaida..?rufaida I'm herefor you...Dan Allah kifadamin meyene?
Shiru tayi bata amsa shi ba,ya Kara jawota jikin sa ya matseta da kirjin sa sosai suka kankame juna tamkar bazasu bambaru ba,kanta ya shiga shafawa ta kwanta asaman kirjinsa,muryn sa na rawa yace cmon Rufaidah waye ne,pla suwaye ne suke razana ki?meya faru ne.
Tanajin yadda yake tambayar cikin tsananin damuwa da tashin hankli iya bakin kokorinta tati ko zata iya amsawa aamma ina Wani sabon kukan ne ma ya Kara barke mata
,...a lokacin Babu abunda kwakwanta yake baiyana mata face abubuwan da suka afku da Ita ba,second by second tasoma Jin kasala gabobinta jikinta Suka hau kakkarye wa,in noo time kwakwalta ya dau zafi yana shirin kuncewa tanajin kanta kamar zai kunce,Zuciyarta taji kamar zai fashe da tsananin axaban tsoro da rikicewa
,Cikin wannan yanayi ta bude rinannun idanun ta a hnkli ta shiga Kai dubanta kasa tana leken jikinta memakon idanta yana nuna mata gaskiya sai take ganin kanta a kewaye da jini jinin Alaji Bature da yadda ya sauko ajikinta yana tsiyaya ayayin data harbesa ga jini ya sauko yana malala akasa kamar ruwa Wani irin karkarwnn da jikinta yke yi yasa shikansa imad razana cikin sauri ya sake ta,a mugun gigice ta tsaya cikin yanayin daburcewar kwakwalwa Duk jikin ta a kakkafe brain dinta yanata faman mata kwarwa akan abun da ta aikata brain dinta nace mata ta aikta kisan Kai...

Ba a cikin hayyacin ta ba ta dago kanta ta kalle imad din idanunta tmkr zasu fito waje dan tsoro,Gani tayi ya kureta da idanun sa da sukayi ja suka sauya kala Dan bai ma san me yake shirin ji daga gareta ba,.
Bude bakinta tayi kamar wacce zatayi magana sai kuma ta Kara cin Karo da plate din abincin da wani katon nama akai Wani luiiii jiri ya kwashe ta zatayi kasa imad ya taho aguje ya tarota ta fado a jikin sa ya damke ta sosai

Tsaban ta gigice sanda bakinta ya karkace yay gefe yana zubda sakakken yawu,tallafota yay ajikinsa ya manne ta a gaggauce ya soma tofa nata addua,atake atake ta shiga sake daukaken nishi babu abunda take cewa sai " Dan Allah karka bani naman mutum,wallhi bana ci..Dan Allah karka bani,ta fadi Hakan yafi sau talatin
,Can imad ya dagata suka koma kan gado tare,Nan ma firr taki ta zauna Dan har yanzu ganin kanta take acikin jini da azaba
"..badon son ransa ba ya fara tursasa ta yana kkrin zafafa tambayar sa yana tambayarta da ihu ihu akn waye ne meya faru da ita
Dan Kwata kwata ya lura cewa bazata taba iya saduda akan lokaci harta dawo cikin hayyacinta ta saurare sa ba,"..
Ganin kamar bazata nitsu ba yasashi ya Kara dauko abincin  dagangan ya Kai gabanta  Babu shiri ta wani ture abincin ta mannu da bango matsowa yakeyi tamkar yadda Alaji Bature yake mata in zaiyi mata mugunta but dis time around ji takeyi kamar ana tambayarta ne meyafaru da Ita so atake atake ta fara confessing tun daga  ranan auren ta har izuwa sanda ta harbesa da Duk wani digon azaban data kwasa cikin kuka mai tsananin tsuma

Cikin ikon Allah bata iya boye masa ko tari ba,Kan ta kammala bada labarin already harta nakasa ta dire kasa kan gwiwonta  cikin yanayin tsananin bakin ciki da dimaucewa,Babu abunda takeyi sai  kuka mai bala'in zafi da taba zuciyar mai saurari..

Yanayin datake ciki is enough ya kassara Duk Wani mai sauran Imani.

Her body is soo weakend, Babu sauran salama ko sanyi acikin ranta face tsananin ciwo da azaba dayake shirin makantar da Ita.

She kept saying dat ta shiga uku rayuwarta ya lalace

Ita kuka imad ma yahau kuka gaba daya aka rasa wanda zai iya fara motsawa acikin su, acikin dakin banda different sound of sheshhekar su babu abunda yake sauka,
Imad Yana da rauni sosai Dan haka ya zage yake kukan tsakanin sa da Allah
Har yana Jan shessheka Cos He can't even control himself when he is soo vulnerabl
Hannu take miqa masa cikin ynyin neman taimako
"Tace dan Allah ka taimaka min in cire wannan jinin aciki na,ni wallhy ban kashe kowa ba,kasa take nunawa tana cewa gashi nan ka tambaye sa,wallhi shine ya kama ni da kokuwa wai zai kwace bindiga yamin irin abunda yakewa sauran matan,Ni ta ban kashe shi ba Dan Allah Kar kace musu nayi kisan Kai
Wayyo Na shigga uku ni me zance ma Allah?Acikin rikitaccen kuka take ta Furta wayannan kalaman yanayinta akwai ban tausayi matuka..
Banda imad daya rufe idanun sa da tafukam hannun sa yanata kuka kamar mahaifyar sa aka aikata wa lefin ba motsin kowa awajen

Ta Kuma cewa
Wallhy Mahaifina yace Kar in kara dawowa gidan mu,yace in na dawo zai kore umma na,Kuma ni gida nake so in koma,,Dan Allah ka taimaka min, karku gaya masa komi kaji?....nide ka taimaka min nabar nan wajen wallahy na gaji dashi,Shirin miqewa takeyi Dan ta iso kusa dashi Dan Duk abunda takeyi ba a cikin hanklin ta take ba,tana dafa bango sai taji ta kasa iya motsi kwata kwata
,...hannun ta dake tsananin rawa ta Mika masa daga wajen datake rakube cikin yanayin daya kara sa shi barkewa da wata sassanyar kukan dayaji koinan sa na masa ciwo da zafi

Da kyar ma yake iya daga kafafun sa tsaban yadda yakejin koinan sa a muce,daurewa yayi cikin sauri ya taho zai tallafota jikin shi niyyarsa ya rungumeta sosai koda zata dawo cikin hayyacinta,sai dai yana riko hannun tan sai kiiii karar bude kofar ya dakatar dashi..

Juyowa yayi atake ganin wayanda suka shigo dakin ayayin da rufaidah  tayi ido bibbiyu da mahaifinta yaa malam, mamaki ne akan fusknsy ganin yadda dakin ya birkice ga abinci a kasa ta barbaxu aga fuskan imad shabe shabe da hawaye rufaida Kuma akan gwiwarta cikin Wani mayuwacin hali..

Doc mehra ne ya taho ya rikosa da sauri yace imad Meyake faruwa?
Bai iya amsawa ba ya shiga kallon fuskar yaa malam,Wani irin numfashi mai mugun hade da zuciya imad ya sauke Jin yadda yaa sheik  da yayi saurin isa gareta ya dagota jikinsa yana cewa "zo rufaida, meyafaru ne? ya jikin naki?kiyi hakuri ga mahaifinki Nan yazo ya ganki..
Imad Ya dada juyowa ya kalle yaaa malam Aransa yace And Who cud her father be inba wannan tsohon da yake Gani agaban sa ba,aransa ya soma jin tamkar ya tarkato wuyar sa ya hallaka sa Da tunanin haka ya fixge jikinshi a mugun zuciye yay waje yabarsu anan...
Gaba dayansu sanda suka bi bayan sa da kallo, kowa kansa adaure yake da yanayin da suka taho suka tsince su Already jikin doc Mehra ya basa Wani abu mai muni ya afku ya lura Rufaida is totally out of her senses bata ma iya gane yaa sheik din har yanzu ba kawai dai maganan su takeji kamar yadda tayi ta Jin na imad ayayin da yake tursasa ta ta gaya masa labarin ta....
Wanda Ita kam haryanzu idanunta bai dena kallon kofar da yabi ba ganin kamar ba dawowa zaiyi ba yasa ta kara runtse idanun ta,Wani sabon Kuka ta Kara fashewa dashi tana yi tana mai girgiza kanta tamkar wata tababbiya,Yaa malam daya rasa gane kan meya ke Gani daga can tsaye yace"..ke rufaidah?..
Wai Meya faru dake ne haka...?Furta Hakan dayay yasa ta dawowa hayyacin ta ta dubesa a Dan birkice tace baba Dan Allah kayi hakuri,baba kayafemin,wllhy ni ban kashe kowa ba,shi yace min Wai kasiyar masa Dani,..,baba wallhy kashe mutane yakeyi,Kullum cikin dare Ina Jin ihun mata ana wani abu dasu,haka ranar ya bani abinci da naman mutum yace inci,daga Nan muryanta ya Sarkafe bata kara iya cewa komi ba,sai can da numfashin ta ya dawo ta fashe musu da kuka mai tsanani,baba wallhy Kullum dukana akeyi,yace zai tura ni sana'ar karuwanci Wai bazaka ci kudinsa abanza ba,sau dayawa ya kulle ni awani daki basa bani abinci,ko nayi ciwo basa bani magani,har anty Fatima ma saida ya kasheta agabana
Da shi da wasu mutune,suk..a suka fasa mata kanta
,,shine da daddare dayazo zaimin fyade saina dauke bindigar sa zan gudu,Ni wallhy ban kashe shi ba,shiya ririkke bindigar dakansa yana ta zagina,nifa jinin sa kawai nagani ajikina..
Tana Kaiwa nan Dan kanta ta ta kwkwalo nitsuwa makana tayi shiru ganin yadda dukan su ukun suka daskare suka shiga mummunan yanayin razana da tsananin kaduwar Jin abubuwan data gama furtawa..

Duk taurin zuciyyar Yaa malam bai hana wannan azaban razana da kaduwar ta bayyana ayanayin sa ba dan
Tuni idanun sa suka kadu sukayi jajjaxir Sam ya dena ma Jin sanyin Ac Jin yadda ko inan sa ya dau turiri

Doc mehra Babu abunda yakeyi sai salati,yaa sheik tuni ya sunkuyar da kansa can kasa sakamakon hawayen sa da suketa zubo masa Babu kakkautawa

Sautin Kukan rufaida ne kawai ya  rikita wajen da azaban saukar numfashin ta mai tattare da tsananin dimaucewar da tayi

Cikin su aka rasa wanda zai iya motsi daga Inda yake, har aka shafi kusan 10 mints ba asamu wanda ya iya bude bakinsa ba,sai can yaa sheik ya shiga share hawayen sa..
You can tell dat it's hard for him to control it cos yana gogewa ruwa na Kara taruwa,cikin dauriya da jarumta irinta maza dakyar ya fixge zafin abn dayakeji a zuciyarsa ya dago idanun sa da sukayi ja ya dube doc Mehra yace "katafi kayi sauri ka dubo shi,..kabi imad Dan Allah karka kyalesa shi kadai,..Babu shiri doc Mehra ya fice daga dakin cikin sauri ya shiga dube dube ganin babu alamar imad acikin asibitin yasa shi ya wuce masaukin su direct, tafiya yake tamkar kafafun sa zasu karye yana kuwa bude bedroom dinsu ya same sa acan dungun daki ya takune kansa akasa Yanata kuka

Da balain sauri doc mehra ya taho kansa yanamai rusunawa agaban sa cikin yanayin damuwa "yace "imad?imad are you alright?shikan sa yasan bazai iya Dora hannu ajikin sa ba, bai taba cin Karo da imad acikin wannan yanayin ba a hnkli ya cigaba da kiran sunan sa jin bai amsa ba ya sa shi yin shahada ya dafasa kadan,Kara fashewa da kuka imad din yayi yanayi acikin tsaddadiyar sautin Muryan sa datake fitowa da mummunan Jan zuciya,lura da fushin sn ya sa doc Mehra ya jawosa da karfi izuwa jikinsa ya fado a sanyaye cikin yanayin sacewar gabobi jikin banda kuka mai sanyi Babu abunda yakeyi...

This is Exactly wat he avoided to hear all his life in his career..

Daga asbiti kuwa yaa sheik ne ya karaso gaban rufaida wacce tuni ta dawo hayyacin ta sanadiyar fitar da maganganun da suka toshe mata kwakwalarta datayi

Tarwal tunanin ta ya wanye ta shigo cikin hayyacin ta tana Jin kanta a a mtsayin rufaidarta,Babu bata lokaci Yaa sheik ya zauna agaban ta yana famar lallabata da kalamai Masu sanyi tare da share mata hawayen ta da suke ta zubowa daga cikin idanunta wanda tamkar tundosu ake dadayi

Yaa malam gaba daya yaji ya rikice ya rude ya rasa fahimtar komi
,tamkar mafarki haka yake ganin komi"wai har ace rufaida yarsa taci naman mutum? Aransa yace
Kai innalillhi WA Inna ilaihi rajiun Amma alai Bature ya cuce ni ya haince rayuwar yata rufaida,kamar zai zubda hawaye haka idanun sa sukayi lufu lufu ya balain dadewa cikin jimamin jin Hakan,xuciyar sa tana Jin tsananin baqin cikin abunda ya jijji,Amma Daga bisani daya kyallara Ido ya kallesu yaga yadda yaa sheik yaketa lallabata yana kwantar mata da hankali yana yagalgalata sai yaji Wani uban girman kai ya turneke sa

Wani muguwar xuciyar ce ta shigeshi wnda ta shiga kulla masa tunani kala kala aransa,Aransan ya shiga rayawa cewa an masa jifa ne da mugayen aljanu Masu jifa da mummunan ukuba

Kuma ai dama baida Wani maqiyi a duniya wanda baison ganin cigaban sa arayuwa face Dan uwansa zaidu da mahaifiyar sa hjy mama,Hala ma so kawai ake arabasa da yarsa rufaida shiyasa aka kawo sa cikin arna ana ta shirya masa wasu xantukan da basa ma kama hankli,yo in har dagaske akeyi toh Ina shi alai baturen?karyan banza karyan wofi in adalci za'ayi ai sai a kirasa shima ya memeta abunda ya afku ko a nuna masa gawarsa tunda ance masa ya mutu,shi ma ata Ina rufaida ta iya harba bindiga?Shifa bazai taba amincewa da xancen kafuran Arna ba.

Yaa sheik ne rungume da rufaida ajikin sa cikin shafo kanta yanata bata haquri yana lallabata harta samu ta nitsu ta dena kukanta a bayyane,..shikuwa yaa malam bai ko motsa daga Inda yake ba,anbarsa ne cikin Wani yanayin duhun jahilci dake zugasa da kuma tsananin tausayin yarsa da baiso ya amsa,..'a hankli ya sheik ya ajiye Kan rufaida a pillow yana mai cewa bari inje in kira likita ya kara dubaki ko yata?rufaida cikin yanayin daburcewar ta riko rigarsa tana girgiza kai cikin kukan tace kawu zaidu Dan Allah karka kirasu, ni gida kawai zan tafi,Dan Allah ka tafi Dani wajen umma na...

a harzuke yaa malam ya karaso cikin hayagagar masifar da take bayyana halin rudewar dayake ciki na Jin tausayin halin da yarsa take ciki wanda baison bayyanawa a fili
Bakin sa harna rawa yace
"Ke dalla kima mutane shiru,akace ki kwanta kijira likita,Mutuniyar banza mutuniyar wofi shashashar yarinyar kawai, ai saiki kashe kanki tunda ke bakki son zaman aure,ina dai dake za'a hada baki da Arna ana xalunta na?...Rufaida menai Miki da zaki tsangwame ni arayuwar ki?Toh alhamdullhi yau gashinan dai kinje kin jefa kanki acikin wata mummunan ukuba,Wai har yar ke din nan kinsan kiyi kisan Kai?
toh dake da Wayanda suke daure miki gindin yau Duk kunga illar bijiremin da kikayi
Wallahy da ke mai biyayyace da Babu mahalukin daya isa ya cutar da ke..
Kin nuna min bakki ji,kin dauko tsana Kin Dora ma mijin Dana zabar maki
Toh wayasan ba asalin gaskiyar kedai kiji tsoron Allah ki Rabu da bin shawarwarin kafurai
Idan kuwa baki daddara ba dake da wahala arayuwanki yanzu kuka kulla..Shasha shar ya kawai,Allah ya wadar naka ya lalace,shiruuu Rufaida tayi tana ta kallon bakin sa kawai Dan bata ma San a wani matsayi zuciyarta ya ajiye sa ba,she wish y'a takan iya tsine ma mahaifinta, da yau din Nan babu tantama ta tsinewa Duk wata alakar datake tsakanin ta da mahaifin ta yaa malam,Murmushin takaicine ya shiga kufce ma yaa sheik yana kallon sa shima yana ta shan azaban mamakin nisar duhun jahilci daya kange rayuwar dan uwan sa wanda ya bayyana masa a matsayin tabon hankli Dan wannan ya wuce ace da shi tsantsar jahilci..

.Da Har ya wuce zai fita daga bisani Kuma ya dawo ransa a tsananin bace yace Na rantse maka da Allah yaa bukar idan na dawo na samu ka matsa kusa da yarinyar Nan bazaka jita da dadi ba..Mudin da kakecewa arna kafurai da muka jefata cikin wannan halin mu zamu cireta,Kai sai kaje kayitayi marar Imani kawai...
Yana Furta Hakan ya fixge jikinshi acikin tsananin fushi yay waje dan baida bukatar Jin mezai ce masa

Wani kallon banza yaa malam yabi kofar dashi,you can tell dat is he is soo worried Amma Ina tsannanin girman kai da mugun kin gaskiya tafi yin masa dabaibayi

a kangare rufaida ta kwanta ayayin da kunnuwanta sukayi jimmm suka dauke ji Babu abunda take maimaitawa aranta face kalmomin da mahaifinta ya gama Furta mata wanda awani bangaren cewa dayay rashin masa biyayyarta ya jawo mata wannan qaddara shiya shiga damun zuciyarta matuka....

Bangaren IMAD kuwa da kyar doc Mehra ya dauko sa daga kasa yayi dashi zuwa kan gado,he was so deep into his emotions hatta tempuretun jikin sa saida ya dau dumi

Ruwa mai sanyi doc ya dauko ya Mika masa,Babu tantama ya amsa tare da miqewa kadan ya zauna yana sauke Ajiyan zuciya,Dan kadan ya kurbi ruwan ya cire a bakin sa jin yadda ruwan ya tokare sa a kirji,da sauri ya ajiye ruwan yana kokarin cusa kansa atsakanin cinyoyon sa doc Mehra yay sauri ya hanashi
Cikin yanayin yin masa fada yace
"Wai meye haka ne imad? are u insane..
"Common Control yourself.." hawaye kawai yakeyi,he look so flabbagasted Dan tamkar ransa aka taba haka yakejin zafin abun a zuciyar sa a hnkli ya dago kansa ya kalle shi muryan sa a Sarkafe yace doc Ina yarinyar?..pls karkace ka barta a asibiti tare da wancan mugun mutumin?I swear to u bazan taba kyalesa ba,I don't think shiya haifeta.
I will sue him and I don't who he is..
A xuciye ya Furta Hakan ganin ma bazai iya banbami haka kawai ya harxuka ya miqe tsaye agaggauce

Da sauri doc ya sha gabansa cikin yanayin da Babu wasa acikinta
Yace"..And where did u think u're going?...xaka shiga tsakanin ya da mahaifinta ne bashi ya kawota duniyar ba?
A hatsale yace doc "Wai danshi ya kawota duniyar bafa shi zaisa ya azabtar da rayuwarta ba
In har Ina numfashi yau din Nan saiya gane kurenshi,I will report him to international human rights Kuma nazan bari ba saina tabbatar da cewa ya walakantu..saiya..

bai karasa ba doc yay saurin daga mai hannu cikin dakatar dashi yace Enough Imad,ya isa haka.
We are talking about family here dakai da alaji zayd bansan Meyake damunku da kuka kasa yayyafa ruwan sanyi ma xuciyarku ba,hurry is this oder imad,karku manta Duk hukuncin da aka yanke sa cikin fushi karshen sa nadama ne.

Dukkan ku kunata fushi,Kun dauka Kuna taimakon yarinyar ne?She hate her life already,this is her stigma,and its need no publicity,babu abunda zai taimaka ma rayuwarta ayanxu kamar rufin asiri,wallhy she cannot handle any more emotional pressure,idan kuka birkice da fushi har maganan yaje ya barbaxu kuna ganin bazata rasa ranta bane? duk Wani abunda zai jawo asirin ta ya bayyana a duniya zai iya kashe ta sabida abunda ya afku da Ita ba kowa bane sai ita dauka ta cikin sauki

Some ppl might only blame her,zasu iya cewa kwadayin mahaifinta ya jawo mata,wasu bazama suyarda cewa she is innocent ba,and wat abt in akaji cewa taci naman mutum?
PLEASE THINK ABOUT THE GIRL FIRST...

A duk fushin da zakuyi yakamata rayuwar yarinyar Nan ta Nan gaba ya zamo muku goal dinku na farko

Shi Kuma saidai muce Allah ya shirye sa,ita kuma qaddararar ta kenan
Allah bai bata mahaifi nagari ba

Doc mehra yana rufe bakin sa imad ya ja tsaki ya bangaje shi yay waje,da sauri ya biyo bayansa yana ta magana Amma bai kulasa ba tsaban ransa a bace yake bai ma jira mota ko cap ba da kafa suka dinga takawa har suka isa cikin asibitin.

Oh god😭duk sanda nakaranta wannan shafin sainayi hawaye,ya Allah ka albarkace mu da iyaye na gari masu jinkanmu..ive witnessed alot of iyayen da kwata kwata basu dauke rayuwar yayansu wasu aba mai daraja ba,tamkar basu suka haifesu ba,duk abunda ya afku dasu marr kyau koya musu zafi aransu,toh a fili madalla ne..iyaye aji tsoron Allah wasu iyayen sukance yayansu tamkar ajiyar maakaho ne dagaa anbar duniya baza a san juna ba,ya subhanll maay Allah deliver us from this kind of tabewa..kuma wallh beign a parent doesnt mean dat bazakayi kuskure ma yayan ka ba,karka dorawa kanka girman kai da jahilci,Allah ya dora musu nauyin maka biyayya kaikuma sai kay adalci ka tsira ka tuna domun yace shida kansa zai karba musu haqqinsu muddin ka tauye musu..Allah ya kyauta.

Please vote...

To subcribe pay ur 300 via 0152983148 mohd sule surayya
Gtb or contact 08060712446.

Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top