THE SCORNED:samarin shaho
*🅱RILLIANT WRITERS ASSO🖊*
_{Pens of freedom,home of exceptional and magnificient writers}_
™/FRID4/1/2019🔞
🍒🍒
*SAMARIN SHAHO*
_The scorned_
🍒🍒
_A TRUE SENSATIONAL STORY_
*From the writer of*
*ARNE🔥*
*MAKAUNIYAR HANYA*
*ALFAH🎀*
*SO MAKAMIN CUTA💔*
*SAKAMAKO🌺*
*SAMARIN SHAHO🍒*
~_Story written by_~
*SURAYYAHMS🔥*
*OFFICIAL CATTY🐈*
*FOLLOWWATTPAD @SURAYYAHMS*
*#Lovestory2018/19*
*#romance#purefiction*
*#Destiny at fault#lovethriller*
*Any resemblence of life style or story should be considered as a coencidence,i give no permission for any comparison 'All my stories are strickly mine,beware copycats!.*
_this page is Dedicated to all honourable members brilliant writers asso._
_And my dear,dear maryam sa'id ko wani shafin farko kyauta ce a gare ki Allah ya sauke ki lpya ya saukaka miki nauyi,ameen_
*TSOKACI!*
*duk abunda yake cikin labarin nan daga farkon sa har karshe ya faru ne a gaske,im full aware of y'an bani na iya'so calm down this isnt a fiction🤗*
*#goldenrules SURATUL HUJURAT*
*1. "Fa Tabayyanu":* Investigate: when you receive an information,lest you harm people out of ignorance.
_Bismillahir-rahmani raheem_
_PAGE1_
Kallon ta take cike da tashin hankali tana cewa" __SARAH!!!!!Stop it sarah, ure overeacting ki ajiye kwalban nan haka ya ishe ki" ,sarahn na tsaye bata ce komai ba sai dai tayi yunkuri ta yi wurgi da kwalban giyan data sha daga sama har kasan benen da suke zaune akai_ .
_hawayen da ke bibiyan kuncin ta ta share ta mike straight ta kama hanya zata bar wajen_ "
Anan Catherine ta tsare ta _c'mon stop!ena zaki je kuma? Look dare yayi fa, its to 1.00 see? Tayi nuni da wrist din ta 'a dame amma kuma still sarahn bata ce koma ba don layi take sosai ta kame kanta dake bugawa tana maida nunfashi_ ..
_A dame catherine tace tunda bazaki ce komi ba zo nan kawai na kai ki daki ki kwanta ure stressed..Bata damu da shirun nata ba anymore sai ta dan jawo hannun ta da niyyar kaita dakin kamar yaddaa tace amma sai sarahn taki motsawa kuma gaba daya ta sa iya karfin ta ta fincike hannun ta ta dan ja baya kadan ta daure fuskan idanun ta sunyi jajir sun kumburo_ "
Kallon kallon suka maida ma juna _cikin muryan layi wanda daga ji kasan bakuwa ce a shan giya tace'ki bar ni haka,just shut up cath' juya wa tayi a hargitse da alaman zata bar wajen tana yi tana magana cikin i'i na' tana cewa "ina zuwa cath relax, kar ki damu emmm? i wll be back ..n..iii bana jin da..ddi ne,daga nan ta wuce tayi gaba abun ta.._
mota ta fincike tana tafiya tana tuno da gawar vashika da kuma maganganun mahaifiyar vashikan yau a motuary da suke je da yamma ita da mahfud da team din ta
listening to all the sobby voices na matar a kwakwalwar ta ya sa ta slow down sosai da tukin data keyi tana jin bugun zuciyan ta cikin radadin jimamin tuno da rayuwar ta a baya.
bata tsaya ko ina ba sai "rai walia hotel india room56 ta hauro,ta tsaya bakin kofar kusan minti 10 sannan ta sa hannu ta shiga knocking.
_Yes! Ya fada da calm and sweet voice dinsa a lokacin da ya bude kofar tare da sauke idanun sa akan nata da suke cike da maye da rudewan tunani"_
Cikin tsananin mamaki ya daskare a tsaye yana kallon ikon Allah "innanallhi wa inna ilahi rajiun SARAH? What happen meye ki keyi haka?"bata ce komai ta wuce shi ta shigo ciki, tana zama kan gadon nasa ta fashe da wani irin sassanyar kuka tare da kife kanta akan gwiwan ta"
hankalin sa ya tashi sosai so ko juya wa baiyi ya sake kallon ta ba,jikin sa har wani rawa yake a ranshi he just wonder if ba sarahn sa bane a gaban sa yau acikin maye,don ba tantama data wuce shin yaji warin giyan hernessy mai karfi na tashi.tsaban ya rasa abun yi ya sa ya dada leko waje gefe da gefen door dinsa don yaga ko gizo yake gani,sannan ya juyo ya dube ta cikin rashin jin dadi yace "kin bani mamaki heroine,can you just stop this nonsense and explain to me yaushe kika fara shan giya kuma akan me? Are alright at all?.
Sai ta dago ta dube sa tare da yatsune bakin ta kamar karaman yarinya mai shirin kuka..kallon ta a hakan yasa ranshi ya dada baci har yana shirin daka mata tsawa"tuni itama ta mike cikin rudani tace "i dont know,ni ban san komai ba mahfud zaka saurare ni ne ko na yi tafiya ta?.
mamaki ya sa ya kasa magana yana binta da ido, yasan sarah tana da yawan daga hankalin ta akan cases din da suke facing musamman kwana biyun nan don kullum bata cikin hankalin ta,shi kansa yasan shes personally attached amma yau shine har da shan giya?
'Bai taba kawo tunanin haka game da ita ba,kai dole ne ma akwai wani muhimmin al'amarin da sarah ta gano ko take boyewa a case din vashika..
ya raya a ransa ayayin da yake kallon ta.
"yunkuri tayi zata sake tashi ta fice jin yayi shiru bai amsa ba,kuma ta lura yana observing dinta ne.
"da hanzari ya sa hannu ya jawo ta ya zaunar da ita akan gadon calmly gefe da ita shima ya zo ya zauna yace "toh im all ears sarah,wa ya baki giyan toh?..tayi shiru ta sunkuyar da kai..cikin muryan lallabi ya kuma cewa.. sarah na,meyasa kika sha toh?ko baki san haramun bane ? baki san zai yi affecting career ki ba Ko?ure a public figure sarah kin manta ne? baza fa ki cimma burin ki a haka ba sarah you will....
Da wuri Ta katse sa da sssssssshhh,ai bani nasha giyan ba,nima bani akayi ka gane?
kuma ai da gaskiyan ta baka ga da dd..nana sssssha najjji sauki, sauki ba?
"baice komai ba don sai yanzu ya dada lura bata hankalin ta kwata kwata but shes in pain and now stammering heavily.
..itama sai ta yi shiru kadan,..daga bisani sai ta nitsu kamar yadda shima ya nitsu yana binta da ido cikin kukan da already ta dade tana yin sa a hankali ta furta cewa"im so scared mahfud please help me
Gaban ta ya tsugona yana mata kallo mai cike da kauna da kuma tausayi"
duk dama yau yaga tabbatacen rashin hankalin ta amma he still feel like tana cikin tashin hankalin da bazata iya rikewa ita kadai ba'
yace "duk laifi na ne sarah, i knew ure not ok da case din nan tun farko, gashi na kyale ki kin tafi ke kadai toh bari na hada miki ruwan wanka i wil get you some milk sai kishah kiyi bacci ure stressed.
ya mike zai tashi ta jawo hannun sa da karfi sai da suka karkace, kadan ya rage ya fada kanta gaba daya" wani dum yaji aran sa ita kuwa dan takaitaccen murmushi tayi ta dube sa tace am sorry.
baice komai ba ya kuma mikewa zai tafi ta kamo hannun sa tare da binsa da lallausan kallo tace"hey listen to me,nasan zaka saurare ni.ni bana son nayi wanka yanzu so nake na fitar da wannan abun dake damuna na huta tayi nuni da zuciyan ta,
yayi saurin tsugono yace
Ya dade yana damun ki ko sarah?Abun da kika dade kina jin shi aranki Ur pain right, Talk to me sarah shi ne?
Kallon sa kawai tayi don bata san lokacin da ta dada sauke wani hawayen ba
Kawai sai ta gyada kai a hankali sannan tayi shiru bata ce uffan ba.
"shima shirun da yayi yana tunani ya sa ta sake tashi ta haura gadon ba tare da ta cire takalman ta ba ta rungume pillow tayi shiru hawaye na kan sauko mata
Kallo ya bita da shi"nasan sarah tsawon shekaru amma ban taba sanin wannan hidden pain din nata ba.
Ko hala shine yau take so ta gaya min"but why?
tana cikin maye idan na saurare ta banyi kuskure ba?wont i be taking advantage of her sub consiousness?
ance wanda yasha giya hardly yake iya yin karya musamman idan abun yana matukar damun zuciyan sa.
"gefe da ita ya dawo ya zauna jiki asanyaye sai ta kawo kanta ta daura kan cinyar sa ta kuma sake hawaye cos jikin ta har ya fara daukar zafi.."
shiru ne ya dan ratsa wajen kafin nan ya sauke ajiyan zuciya"a ransa yace ina matukar kaunar ki sarah ure my life
...koma miye ne yau zanji kuma zan tsaya miki har rayuwar mu ta kare"i promise you..
nan ya shiga shafo gefen fuskan ta a hankali cikin sigar rarrashi har ya jawo ta jikin sa yana zaune ta dan lafe kan kirjin sa
A sanyaye yace "heroine,please tell me now kar ki boye min komai'lets share ur pain together,kina bukatar hakan don bazan taba iya sake ganin ki a wannan halin ba"
shiga jikin sa tayi kadan ta dada lafewa akan kirjin sa tana maida numfashi a hankali alaman taji meyace din'hannu ta sa ta goge sauran tears din ta sannan ta shiga bashi labarin kanta.
_At exactly 5years 10months ago_
_✍🏻 Alkaleri unguwan kurwala_
'Saratu..saratu..ke saratu!! Ke tashi...da Allah tashi kiyi gidan ku mayyah kawai..shegiya!
Baba laure ne akai na cikin masifa kamar zata wanka min Mari
"Sum sum na dago a kasale na shiga watseke wa tare da mutsuka ido Daga lungun da na rakube ena gyan gyada wa a hankali na daddafe na mike a ladabce nace"
"Ena wuni baba Laure"
..ban amsawa. yi maza ki wuce gidan ku tun da ke kunnen kashi ne dake ...maza wuce ,fitinanniya kawai.
Nace"Baba dan Allah kiyi hakuri ki barni na dan kara lokaci anan walhy bazan dade ba zan tafi...
Bata kula ni ba ta shiga zabga kira cikin gida dan dama daga gefen zauren su muke
"Dan asabe ,kai dan asabe... Maza kawo min dorinanan nan yar fiskan wa kawai
Jin haka ya sa Tuni Na matsa gefe a tsorace
Ido na suna neman cikowa da ruwa amma sam naki tafiya na tsaya ko zata tausaya min
"aniyar ki ta biki saratu tirrrrr da irin hali naki..wai ace mace kamar ki da girman ta sai tabi ta gallabe mutane da rakube rakube a gida kamar kyanwa,..saratu anya ba wani abu kike boyewa ba kuwa?"
"A'a, baba laure walhy babu komai ni bana boye miki komai ..kawai na idan gaji ne daga makaranta sai na kan huta anan kafin umma ta dawo sai naje gida.
Harara ta watsa min tace"Da Allah yi min shiru yo mani zaki yi ma shariah saratu? kai ungo naki ta zungure ni da karfi..."surfe kuke yi ko nika a makarantar da zakice min kin gaji kina hutawa?,ta daura hannu a kugu tana bina da mugayen harara cikin masifn ta kuma cewa
"hmm toh waye ma bai gano ki ba a kauyen nan yanzu..
Ke fa tun da ubanki malam bukar ya rasu kika soma neman hanyar tozarta uwarki gambo"
"Kai amma albasa batayi hannun ruwa ba sam. gambo dai ita ce ta soma aure acikin matan marigayi malam bukar duk don ta kare mutuncin kanta da naki amma gaki nan kina yawon jawo mata masifa a gari ai ena ji sarai a makwabta jiya a na cewa har kwana kin tabayi a zauren gidan su bintu diyar malam buba.
A take na sunkuyar da kai na kasa.
"to bari kiji saratu .. nikam dai nafi karfin ki ba dani ba sai ki canza lale.
Kuma kinsan Allah? kawancen ki da yata hansatau ma yau din nan na soke shi ,Bafa zanje wanjen gambo kai kara ba, wannan karon har wajen kawun naki dan goggoji zanje na kai ki,wallhhy in baki fita a tsabga ta ba zaki san kuwa kin tsukano tsuliyan dodo.. maza zo ki fice ayi gaba chan Allah ya tura keya.
"har yanzu Kaina a kasa yake bance komai ba Hawaye na sun taru suna son su sauko kasa amma na hana su, cikin taushin murya mai ban tausayi nace.
Ayi hakuri dai baba laure Allah ya huci zuciyar ki duk abunda kika ce naji
Insha Allah...
dakata.. Ta katse ni azafafe yi waje!!
Ban motsa ba "ta dan tura ni da karfi, A sanyaye na kalle ta kalar tausayi na juya na gyara jelar makaranta na na soma tafiya akan layi
Tsaki mai kauri ta watsa daga nesa enaji tana kan zagi na
Gabanin magrib ne don haka waje ya soma rufewa da duhu
Tunanin me zanje na tarar a dakin umma ya sa ni fashewa da cun kusashen Kukan takaici
"Shekara na goma sha hudu ne kacal a lokacin nika dai umma na ta haifa
A yanzu ena aji na biyu a makarantar gaba da primary a nan bayan tashan kurwala
Yau kuma rasuwar baba na malam bukar wata goma sha uku kenan cas..
Baba ya bar mata uku mama na ne amarya
Ina da yayu biyu maza yaya hamza da yaya mati da yayu mata manya guda shida guda huda daga cikin su duk an aurar da su bisa al'adan mu na fulani tun suna shekaru 11,12 13 yanzu saura laraba ne da lami yan shekara 12 suma duk an sa ranar bikin su
Gida daya muke har Yanzu da yan uwa na da kishiyoyin mama na'
"kawu babaji ne,bayan ya auri ummah na ya ba ta izinin ta zauna tare dani a kan daki na na gado don baba na baida dukiya sosai dama makeri ne abakin kasuwan garin mu
daki daya na samu a gadon sa daya barma na kuma shine wanda mahaifiya ta take ciki yanzu
"makarantan boko da na keyi har yanzu shine Babban wutar fitinan dake cin ummah a gidan mu .
Don kowa ya zuba mana ido ne yana jira yaga madakatan tarbiya na
Umma ita kadai tace bazan yi auren wuri ba sai nayi karatun bature tun baba na raye.
Tun Bayan auren ummah da kawu babaji nake cikin fitina da tashin hankali.
Don kuwa nika dai nasan mummunan halin da nake ciki a hannun kawu babaji wato wanda ya maye dakin mahaifiya ta a yanzu.
dan iska ne maci amana azzalumi..gashi mugun gaske ne don ko ni nan ena matukar tsoron sa
Kawu babaji irin kasurkurmin jahilin dattajo ne masu sa ido da kahun zuqa ma kowa musamman yan mata da samari..
kai kawu bai bar kowa ba wajen tada zanne tsaye tsegumi da hade haden magana a gari..
Amma dai yana da rufin asiri manomi ne kuma Shima yana da mata biyu sai dai suna chan gidan sa a bayan layi enda ya kafa babban majalisan gulma da bare deden sirrin mutane,
Yanzu haka Bana ganin sa sosai
Don sai ranakun kwanan sa da ummah yake zuwa dakin mu
Tunda na cika sha uku dama yayi mummunan samin ido,amma yanzu daya auro ummu na wani abu daban nake ganewa tattare da shi
wato a duk lokacin da nayi laifi idan zai buge ni sai ya rika cahkumo min nonuwa na yana hayagi da jiki na a nasa yana mammatse ni cikin wani irin kokuwan da bana gane kansa,.don ko na tsaya waje guda ya bige nin baya bari na sai ya rika jana yana fizgo ni jikin azzakarin sa wanda ban taba jin ya kwanta lumui ba in yana duka nan .
Shiyasa duk randa zai zo kwana gidan mu kwana da umma sai na dau lokaci a wani wajen sosai in na fakanci anyi bacci sai na zo gida na kwanta a soro baki alekum
Na dan dauki lokaci ina haka ba wanda ya sani.. Badon ma korafin mutane ba da Umma na bazata san ena zuwa gidajen kawaye na ena rakubewa don naja lokaci ba
Ummah Tayi fadan tayi fushin amma babu mafita waje na don sam na Kasa samun sauki kuma tsoron abun da zaije ya dawo ya hana ni kawo wannan maganan wa ummah.
gashi sam bana so na hada ta fada da sauran matan gidan don ba sa kaunar ta tun da ma bare yanzu data riga su aure.
shiyasa ban taba gaya mata sukan kore ni a Wulakan ce daga dakunan yayan su da daddare ba,yanzu duk tunanin ta idan baba babaji yazo mata,ni ina chan tare da sauran yan uwa ina kwana.
"Allah sa ummah na ta dawo".na fada tare da sauke Ajiyan zuciya na shige cikin babban gidan namu
Banyi magana ma kowa ba na isa shashin namu
a gefe na ajiye jakata na shiga bayi ganin babu kowa ya sa na dauro alwala kawai na shiga sallahn magribh.
Zan iya cewa Bani da ilimin addini dan Ban wani iya nagartacen sallah ba sabida islamiya daya ne damu a garin mu wato islamiyan zauren malam shehu.
Anan kuma daga karatun sallah ba abunda ake tsinta amma naso ace nayi karatun addini sosai saboda baba na yana da ilimin addini dai dai kwarkwado shiyasa nakan ce tarbiyan sa daban take da kowa.
Ina zaune har wajen isha ba wanda ya shigo abun ya bani mamaki
Riga na da zani na kwama na dan hingine akan tabarma a dakin ummah ena tunanin rayuwa.
Assalam Alaikum
Dum kirji na ya buga na leko mukayi ido hudu da aziza yar makwabtar mu
"Waslm ya dai aziza?
"Uhmmm Yawwa Addayo dama wai ana
Kiran ki ne a waje
Nace Ni kuma aziza Waye wannan din ?.
Tace "Sageer ne mai shagon askin hayin nan.. ta washe baki zatayi dariya..
Na ce"Shhhhhh ke da Allah yi magana a hankali mana na dan leko gefe da gefe ena lura.
Nace"Jeki kice bazan zo ba yayi maza ya tafi
""Ah 'ahhhh amma amma Adda..adda... yoo
Cikin bude ido nace "ki wuce kawai kiyi abunda nace miki aziza bana son wani bayani
"Babu sallama sai buuut mu kaji mutum akan mu
"in....a i...n...a wuni baba babaji'"sum sum aziza ta tafada a rakube tana do tabi gefen sa zata wuce waje don tsoro muryan ta har na rawa
nima firgit na mike kirji na na bugu .nace sannu da shigowa baba
Ya wani daka tsawa
Ke aziza!! Zo nan
Kuka ta soma yi don karama ce yar shekara 9
ya jawo ta Zafff ya wanka mata tafi a kafadan ta..zatayi kuka yace" yimin shiru Munafuka,bana hanaku shigowa lungun nan ba? Wato kune iyalan kai gulma waje ko..yanzun
Me kika zo yi anan
"tsut ta kame bakin ta dake bari tana jimami "Uhmmm uhmmm baba ,dama na zo gayan aika ne.
"eh ..ehh baba kayi hakuri aika ta zo
Yace "Aika? wajen wa kenan.
Ya juya ya tsula mana razanananun idanun sa
Tace" Dama goggo rabi ne tace addayo ta zo ta debe kwanukan ummah..
Nasha mamakin karyan da aziza ta yi yanzun sai na sake baki ena kallon ta
na kasa cewa komai
"kuka ta fashe da shi tana bashi hakuri..daga bisani yace wuce ki bani waje
da gudu ta fincike tayi waje. sai binta da ido nake bayan ko sake kallo na batayi ba..
harara ya watsa min sannan ya shiga ciki
bance uffan ba sabida komai ajere na bari daga abun da nasan zai ce yana bukata na miko masa .
tsaki ya ja bayan ya ga hakan.
kenan baida dalilin da zaisa nayi masa wani kwakkaran aiki bare ya sake samun daman gaya min maganganun batsa dana cin zarafi kamar yadda ya saba.
Ina ganin ya zauna yana waya na sabule nayi waje din nasan zama ni da shi inuwa daya ba alheri bane tunda aziza tayi min hanya sai na bari akan shine makara ta
Fita na ke da wuya Ashe ranshi yayi mugun baci dana fuce din ,a ganin sa ya samu wani damar baza min halin sa tunda umma bata dawo ba tukun.
Ko cin abinci baiyi ba ya rufe ya biyo baya na
Cikin rashin sa'a kuwa
Ina fita na ci karo da sageer a bakin kofar gida
tsayawa nayi ena rokon sa ya tafi don kirjina har bugu yake min kar baba babaji ya fito ya riske ni da shi a tsaye.
Mun kai kusan minti 10 muna sa'in san magana amma da kyar sageer ya amince ya tafi a dole wai shi da gaske yake zai aure ni..
Bayan tafiyar sa Juyawa da zanyi sai cahraf muka hada ido da baba babaji gani nayi yana leko bayan sageer daya kusa lumewa daga lungun gidan mu..
na sunkuyar da kai na kirji na na bugu wani irin mugun kallo yamin ya kada kai ya wuce abunsa
ni kuwa ganin baice komai ba ya sa na bari a hala baiga komai bane sai na sullebe na shiga gida.
Akan hanyar sa Dariyar mugun ta yayi sosai har cikin ransa yace " yarinya kenan,ai dama yaro yaro ne,ni babaji bazan taba rainon dan damisa na bar ma na dawa ba wannan karya ne..
Dama chan ena ta farautar sarahtu Amma daga yau ena ga komai ya kare
Wannan ai Sageer ne dan gidan halliru mai nama hmm"dan gidan wanda nake bi bashin filin gona ta daya gina gidan sa ya kasa bina dan jaraban talauci..kayyah!!!
...ya karashe da wani shu'umin murmushi
Nikuwa Hankali na kwance na zauna a daki,
Sai wajen 8 saura suka kuma shigowa da umma na
A ladabce na sake gaida su
Na kimtsa ma ummah kayan sana'ar ta don dama masa take siyar wa a babban kasuwar kan tudu itake da babban rumfa don ummah na akwai azama da hikima irin na matar karkara.
Hiran su suke yi irin wanda na tsana don sosai kawu babaji yake soka ma umma maganan banza kuma bata isa ta rama ba..
wani bin har yakan ce mata yar bariki goyon farar hula wato karuwa kenan
Umma na bata da hayaniya sabida bata da ilimin komai amma a ladabce take mayar masa da suka in abun ya ishe ta....
abu daya ke bani haushi yadda yake saurin wasa da hankalin ta ta wajen juya magana..
in har yace abu kaza ne bata isa tayi musu da shi ba yafi so ma tabi bayan sa ko kuma tayi shiru kawai
Duk randa ta haura ko akan gaskiyar ta ne sai ya soma dukan ta yana zagin ta ta uwa ta uba,umma na kuwa tunda akayi hakan sau biyu sai ta dena bashi daman haka kwata kwata duk abunda yace yanzu sai dai ta hau kai itama ta dada zuga shi ba don son ranta ba.
Ni kaina nan na sha deban jibga a hannun sa akan samarin dake biyo ni kofar gida
a hakan ma wata rana na san karya yake min amma ban isa na tanka ba haka zasu min lisss
sai dai daga baya umma tabani hakuri
Suna na zaune Wayar sa yayi kara ya dauka
Yace"Wai yaya ne kam zulai?
dan shiru yayi daga bisani ya kwaroro salati
Yace"Hmmmm duniya kenan tabbas anyi mana rashi kai kai kai bari to zan neme ki kawai...
Ai Wannnan maganan ma ku barshi haka zan zo da kaina ma gobe
Yana kaiwa nan ya katse wayar yana jimami,.
Ummah tace "Me gida lpya kuwa...?
bari kawai gambo..ya ya mutsa fuskan kalar jimami yace"ai zama bata kama ki ba Gobe zaki je chan dindima inna wuro ne ta rasu yau din nan da dare.
"Innalihhi wa inna ilaihi rajiun,. Allah ya ji kan innna.. Allah ya sa ta huta amma babaji ciwo tayi ne haka?Sai naga kamar jiya jiyan nan yafendo ta gaya min inna wuro garau take tana ma filin roron gyada.
Ni dai ina daga gefe ta bakin kofa Ina shiru uffan bance ba
"nan baba ya hatsala"Ke da Allah rufe mun baki gambo,da
Cahn mutuwar sai ya zaba wanda zai dauka ne? bana son shashanci da neman tsugudidi fa"
Ummah ta tabe baki tace "ahhhhh toh Allah ya baka hakuri
Mai gida Nace ba?
Goben da su zulai kenan Za muje ko?
"ban sani ba ..ya mike a fusace kamar zai mare ta
wanda hakan ya sani sulalewa chan nesa da bakin kofar kadan na rakube.
Ke kadai nace zaki je, da daban aure ki ba ai su nake turawa..wai nikam rashin kunya zakimin ne gambo?
Uhmm uhmmm..umma tace kamar bata damu ba
Tace Allah ya kaimu goben..daga nan taja bakin ta tayi shiru
Shiru ne ya ratsa wajen ban sake jin motsin su ba..
nima bacci ne yayi nasaran dauka na a gefen bakin kofar ban sani ba
gurnani da sambaton baba babaji ya sa na firgita. cikin sanda da tsananin kunya na mike na kama hanyar soro ba wanda ya sani kamar kullum naje na kwanta kan dakali.
Bayan sallah asubah
Wanke wanke na ke yi ayayin da dai dai kun mutanen gidan mu ke fitowa .
Yanzu kam babu wanda yake kulani sosai a gidan..
su yayu na ma kamar tsine min sukayi ..ai idan mace takai haka a gidan uban ta ba aure to karuwa ce"().
"'yawwwa Gambo ya kamata ki fa hanzarta ki kama hanya maza maza ayi wankan inna dake.
cewar baba babaji.
"toh me gida ummah ta amsa..Nan ta shiga shirin ta tsaf.
Bayan na kammala dumame na rusuna na gaida su" tsaban kallon da baba babaji yake aika min a sace ya sa na kasa cewa komai na daure fuska.
umma duk tana lura da yanayi na amma sam na kasa gaya mata tafiyar tan ne bana so kwata kwata sam hankali na ni bai kwanta ba.
Gashi ya sa ma na ido ko tari umma tayi sai ya amsa"
hakan mukayi rabuwa da kaikayin magana a zucin mu umma ta kama hanyar dindima.
Tun tafiyar ta komai ya sauya Acikin nishadi baba babaji yake, don sosai fuskan sa ya nuna hakan duk dama yana yi yana fuskewa yana shan qamshi..
tunda umma ta tafi ko hutawa banyi ba don tamkar baiwa haka ya maida ni
Yau da safen har wanke masa aswaki da kasar takalmi sai da nayi
"karfe 11 saura ne,sai na dan jinguna kadan ena jiran lokacin makarantar rana yayi,nan naji an kwalla min kira...
gani baba,na shigo na rusuna gaban sa.
je ki bakin kasuwa wajen mai shayi zai baki aika ki kawo min..
Nace toh azuciya naa ina tunani"Tabbb yanzu fa ya ci dumame jibgi guda ko mai zaiyi da aikan mai shayi oho"
Nan na mike ina kokarin ficewa .
Ya dada hade rai Yace saura kuma nazo na kama ki a inda kika saba lafewa kina iskan ci da yan iskan nan marasa tarbiya irin ki,..
madallah ma kinsan yanzu nine aka bar min ke agidan na ko?to ki kiyaye kan ki da ni saratu.
A ladabce nace to ,sai ya juya kansa ya ce
Kuma layin mai goro zakii bi kar ki sake kibi bakin titi kinji na gaya miki kenan.
Gyada kai kawai nayi
Bance uffan ba na sabule nayi waje na kama hanyar kasuwa...
Ina fita Ihu ya sake ya soma rawa yana kirari makan sa adakin shi kadai
" Kiriiiiiii baram bam bam bam bam kaii kai,..sai ni babaji dan gidan goggoji sara dai a hankali.... dawa sai maza,, .. duk wanda yayi jiran tasha dani da shi zamuyi kwanan mota.
Yiiihuhu sai ni babajii dan goggoji yau ango kake tartil babu hafsin.
Kikiki ya fashe da dariyar kuruciyan zuci Mai shake da jahilci da tsananin mugun ta.
hahahaha yarinya yau naki taka kare kwanan ki sai agadon babaji dama chan nagaji da cin durin uwaki...
Ya koma kan gado ya kwanta galala cikin tunani yace"Ga nan rabi bazaura na jira na alayi kwana nan zan yaga ku na auri ta na huta.. Na gaji.
Haba,itama tabi duk ta hanani sakat babu dama nace zan ci nata durin agaban gambo dan nasan munafurcin mata sarai.
Cikin shakekken nishadi yake maganan sa'yanzu duk sai sun gane kuran su.
Ya koma ya dada juyi cikin maganan zuci wanda zai tabbatar maka da ya kullace ummahn ya ke cewa"hnmmmmm Kina wasa dani ne gambo,yo ni me zanyi da saiwar jikin ki da yaya bukar ya gama shanye wa?dama chan dan kuruciyar ki na gani.
dukan ku ai akan tarko na kuke lokacin ku ne yayi,kinga kafin ki dawo daga gaisuwan mutuwar karyan dana miki.
Lokacin har wannan shashar yar nakin ta san ni waye,
itama da sannu zata haura kan qayar dana daura mata shi yanzu....
kai bari ma na fita saboda naji dadin ganin komai ya tafi min dai dai idan kuwa sageer yamin kuskure nasu ya kare agarin nan.
dariya ce akan fuskan sa ya dau hular sa ya fice hanyar kasuwa.
_FIRST CHAPTER REVIEWS I NEED SOME MOTIVATION_ 🙄🙄, _yana ji na gaji ne_ 🥺
*Follow Wattpad@ SURAYYAHMS*
Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top