Thirty-seven
On the authority of Abu Dhar Jundub bin Junadah, and Muadh bin Jabal that the messenger of Allah said : "Fear Allah wherever you are, and follow up a bad deed with a good one and it will wipe it out, and behave well towards people." Tirmithi narrated the Hadith and said it was fine, and in another version, said ture and fine.
**********
Ikon Allah Abla ta tsaya gani, duk ya ruɗe babu gaira babu dalili, though ranta yana bata cewa kila shima yana ganin gizon da akace tanayida Miemie. Sai dai ba wani big deal bane dazai rude haka kamar yayi gamo.
Bata hanashi taɓa fuskarta ba saida itama ta kafa mashi ido kamar yadda ya kafa mata. Yana taɓata yaji mutum ne saiya sake baya ya rufe idonsa. Rufa ke keto masa duk ya firgita, saiga Naufal ya shigo.
“Yauwa Abla dama ke nake nema”
Kallon Khattab yayi yaga ya sukurkuce, Cikin damuwa ya soma masa magana.
“Lafiya kake zufa duk Ac dakin cikin nan?”
“I think shima yana ganin Miemie a fuskata ne” ta amsa a sanyaye
“Ohhh! Of course Abla ne, yes im not running mad” Khattab ya faɗa yana ajiyar zuciya a hankali, handkerchief fari ya ciro daga cikin aljihunsa ya share zufan Fuskarsa.
Da farko ya dauka yayi gamo ne, sai kuma ya sha hauka ya somayi. Zuwan Naufal ba karamin relief ya bashi ba. Ita kuma mikewa tayi ta bar wajen tana matse kwalla.
Abin ya fara isanta, hala mutane basu lura itama tana missn Miemie bane, duk inda taje sai an firgita kuma ba’a lura itama tana jin ciwon abun cikin ranta.
Shi kuma fasa cin abincin yayi saiya tafi gida kawai, kwanciyar rub da ciki yayi akan gadonsa. Kawai tunanin yanda Abla batada bambanci da Miemie ne yakeyi. Magrib aka kira saiya tashi ya wuce masjid.
A hanyar gate ya haɗu da Lili tana dawowa daga anguwa, da gudu ta karasa inda yake ta rungume sa. Dama rabon data haɗu dashi tun shekaran jiya.
“YaKhattab naji daɗin ganinka Wallahi”
“Na hanaki rikeni, wai meyasa bakya jine?”
“Toh fah ji wani sanabe, wallahi iyayi da kakeyi kamar baka jin dadi idan na rike ka bani mamaki yakeyi”
“Eh naji nidai sakeni kawai kinga masallaci zani kafin na makara”
“Anaso ana kaiwa kasuwa” tace saita sake shi. Harya soma tafiya wajen taku biyar haka saiya juya, “Lili” ya kirata.
Itama waigowa tayi tana rarraba idanu, “ya akayi ne Yaya?”
“Am mani mutuwa amma bakiyi min gaisuwa ba, mutuwa fa ba abin wasa ne!”
“Toh ni ina ruwana dan budurwa ka ta mutu? Wallahi banki ba duk wanda ta ganka tace tana so ko cikin ranta ne toh ta gangara lahira” ta faɗa tana hura hanci.
Murmushi yayi mai bayyana bakin ciki, cikin gadara ya bata amsa. “toh saiki zauna gadin duniya idan kina tunanin bazaki mutu ba, kuma mutuwar nan yana kan kowa balle kice banda ke”
“chan ta matse maka” saita barshi wajen ta nufa cikin gida. Shikuma girgiza kai yayi yana murmushi, nan ya tuna da Miemie daya kirata a waya sunsha dariya. “Allahu Musta’an” ya furta a fili saiya nufa Masjid.
*****
Yasmeenah ta rinka hura ma Naufal wuta akan su tafi, ko sallar Magrib da kyar ta bari sukayi. Ita bama zata yiba saboda ana binta bashin azahar da la’asar kuma da kunya kaje gidan mutane kana jero salloli.
Yana dawowa ta mike wai a dole sai ta tafi, kamar kyamar gidansu takeyi taki sakin jikinta, bata lura cewa Deela bata haɗa komai dashi ba amma ta mayar da gidansu kamar nata.
Yaune ake sadakan bakwai amma Abba ya umarce shi akan yayi zamansa, da wata matar arziki ne da tun safe ta tilasta suje.
Haka sukayi sallama da yan gida suka tafi, tun bayan da akayi masu nasiha bai sake ganin Deela ba. Koda ya aika Bilqees ta kirata bata ko kalleta ba.
A Vanilla joints suka tsaya ya siyan masu shawarma, burger da milkshake. Daga nan ya tsaya a Chuchu Stores ya siya bread, milo, Madara, Indomie, sardines da sauran su.
Ita hakima ta hakince cikin mota tana duba Instagram, hotunan celebrities take kallo musamman ma maza tana jindadi hankali kwance. Ya dawo shake da kaya amma ko ta taimaka masa, asalima yi tayi kamar bata san yana jiran ta tayashi buɗe kujerar baya ba.
Haka ya ajiye kayan a kasa saiya buɗe da kansa kana ya sake dauka daya bayan daya ya rinka sakawa ciki. Bayan na saiya zaga ya shiga ya soma tuki. Ko irin ‘Sannu da kokari Maigida’ bata ce ba. Tuki ya soma yana tunainin ko ta daina sanshi ne kokuma kawai iya shege ne...
“Bazaki taimaka min bane kin ganni sai wahala nakeyi” tana yatsina fuska ta dauki ledar Shawarma da burger kawai tayi shegiwarta ciki.
Daki ta shiga ta ajiye, saita buɗe shawarma tana ci. Tanayi tana kallo ko bin kan Naufal batayi ba. Shima ya watsar da zancenta ya nufa Masjid domin yayi sallah isha.
Saida taci tayi nat kana ta wuce hanyar ɗakinta, a locacin tayi wanka tareda daura alwala.Jero train ɗin sallolinta ta soma yi. Ita bata kwana batayi sallah ba amma bata fiye sallah akan lokaci ba, duk dare zatayi abinta.
Wani pink nightgown mai laushin gaske gashida sansti ta saka. Saita saka palms din barci ta nufa hanyar ɗakinsa.
Shikuma ya dawo daga Masjid yaga falo duk burbushin abinci wanda taci ta bari, daukan nasa yayi ya tafi ɗakinsa. Baici ba saida ya kintsa.
Ya gama ci yana shan ruwa daga bedside fridge ɗinsa saita shigon tana masa murmushi, dakewa yayi amma bata damu ba.
Shagwaba ta soma masa, daya mata maganar behaviour ɗinta na ranar saita bashi hakuri wai kawai she is overwhelmed by everything ne. Ba laifi ya sauko daga fushin sa daga nan sukayi kwanta.
After six weeks...
Fadeela ta soma samun sauki sosai, har yanzu bata magana amma ta rage yawan kuka kamar yanda ta mayar ibada. Kuma tana ɗan murmushi koda sau ɗaya ne a rana.
Kullum cikin addu’a take a zuciyarta Allah ya bayyana mata ɗiyarta. Har tayi arba’in ta soma sallah da kanta tana rok’on fita daga cikin matsalan.
Naufal da kanshi ya dauko mata donkey, paints dasu sauran kayan masu painting. Taji daɗin abin sosai saboda yanzu batada wani sana’a sai shi.
Kowa yana murna yadda ta fara mayar ma Allah komai ta dauki dangana. Yakan zo dubata sau biyu, da safe idan zashi office sai kuma da yamma idan ya dawo kafin ya wuce gida.
Ta ɓangaren aurenshi da Yasmeenah kuwa babu abinda ya canza. True colour dinta ya bayyana sosai, samsam bata da kunya ko kadan. Gatada tsiwa yana cewa kule zata ce chas.
Abinda ke bashi haushi shine rashin iya girkinta. Kwata kwata bata san yadda ake sarrafa ɗanyen abinci a mayar daffafe ba. Kawai managing yakeyi saboda bayaso ya tsinka ta wajen iyayen shi ya rinka cin abincinsu har su gane.
Sau da dama yakan kira Abla ko Bilqees suzo tayata aiki duk a zatonsa hannunka mai sanda yake mata, ita kuma bata san wannan ba suna zuwa take naɗe kafa ta fara kallon Korean series ta barsu su kadai cikin kitchen din.
Gajiya yayi da ɗabiarta ya hanasu zuwa , dama suma basa santa at all. Ta rinka daka masu ihu kenan kamar yaranta, abin yafi bama Abla haushi ita dake sa’a da ita.
Ita Abla ta gama Nysc ta soma aiki a Ministry for Women affairs, ita kuma Bilqees za'a shiga 300l.
******
Shikuma Huzaifah baya kwana uku cikarkiya baije ya duba Yasmeenah ba, shakuwa ne sosai ya shiga tsakanin su. Kullum cikin tambayarta yake ko tanada wani matsala wala na kuɗi kona Naufal.
Tun tana ɗari-ɗari dashi harta sake mashi sosai. Musamman yanda idan zaizo yakan kawo su shawarma da chocolate wata rana harda ice cream da kasarshiyar kaza.
Sukan sha hira sosai tana jin daɗin company ɗinsa, Hilal dai bai taɓa zuwa ba amma sauran yan uwanta duk sunje wasu sau daya wasu kuma biyu.
Naufal ya nuna bacij ransa a fili amma bataji ba, sau da dama abin ya jawo masu tashin hankali amma tace bazata daina sake mashi ba.
Thou bai taɓa shiga ɗakinta ba amma bata kiba idan tayi wanka sanye da towel tazo falo suna hira tayi shafa da kwalliya...
Sau da dama tana ba shi kanshi Huzaifah labarin irin faɗan da sukayi da Naufal akanshi, ‘sis kina wuta fah, wallahi bakida dama’ yake cewa.
Wata rana suna cikin hira ya ce, ‘yanzu kina samun ciki kika haihu kema za’a maki kishiya’
“Akan me za’a min kishiya”
“Konine matana ta dauki ciki cikin early years ɗin auren mu to zan mata kishiya dole”
“Kai daban mijina daban!””
“We are all guys, kuma tunanin mu daya ne. Idan zan baki shawara ki dauka toh ki bari nan gaba saiki haihu”
Ajiyar zuciya yayi yana kallonta,yana ganin kamar maganar shi ya fara tasiri cikin ranta saiya soma magana da full confidence babu inda inda, “nifa dan uwanki ne bazan cutar dake ba, mufa maza bama son takura kuma kinsan tara yara ba karamin takura bane”
“Shikenan zanyi tunani” ta faɗa a sanyaye.
“Da yafi maki Lil Sis”
Murna fal cikin ranshi saboda hakkunsa ya kusan fara cinma ruwa, wani smug kallo kawai yake mata ta gefen ido kuma yana kara ma jikinta kallo.
Yau sanye take da blue crazy jens wanda yasha yanka ta wurin cinya da gwiwa, saita haɗashi da chiffon top mara hannu. Yana kallonta yana haɗiye miyau saboda kwanan nan bashida wani katabus sai tunanin ta. Ko barci yanzu gagaranshi yakeyi saboda yanda take masa yawo cikin rai.
Yasa saiya zo ya ganta yake jin daɗi, saidai inda abin yake zuwa mashi da sauke tana bashi free show din jikinta koba duka ba amma yana samun banza. A hankali zai koya mata sanshi harta rabu da mijinta ta koma mashi.
Ita kuma abinda Huzaifah ya faɗa mata ya soma mata yawo a cikin kanta, tabbas akwai kamshin gaskiya a tareda zancen saboda gashi Fadeela bata gida kuma ta lura tun kanta haihu take chan gidan. Ita yanzu duk wani hanya da zata bi ta malleke Naufal take nema, idan rashin haihuwa zai zame mata mafi saukin toh shi zata bi.
Yanzu idan Naufal ya dawo zata faɗa mashi suyi tsarin iyali, sai wani zuciya ya raya mata cewa gwara tayi abinta ita kaɗai babu wanda ya sani.
Chuchu Stores and Pharmacy taje ta siyo contraceptives kala kala na kamfani daban daban. Haka ta rinka shan abinta bada sanin Naufal ba.
Three months later........
Koda Naufal yaga batada ciki bai damu ba saboda Fadeela itama haka tayi kafin komai ya daidaitu mata. Bashida wani buri daya wuce ya tara iyali sosai, gashi har yanzu ba’a ga Pha’eexah ba.
Saidai IG baban Khattab yace har yanzu suna kan case din baza’a huta ba sai anga karshen abin. Shikuma Khattab ya koma bakin aikinsa yanayi sosai.
Sunyi kacha kacha da Lili har yayi sanadiyar barinta gidan su, yaji dadi sosai saboda yanzu yana samun ya wataya.
Saidai har yanzu zancen wata budurwa kuma baiyi ba. Bayada lokacin kallon wata ‘yamace kuma. Soyayyar Miemie yana nan fal cikin ransa kamar basu rabu ba, ya rasa inda zaiyi da irin abun.
Wata rana yana zaune cikin office ɗinsa, wayarsa ya dauka yana kallon screensaver ɗinsa wanda hoton Miemie ne bai cire ba. Kawai daukar mukullin motarsa yayi saiya nufa gidan gona.
Ya shiga anyi gaisuwan mutunci da Anty da kuma Deela, yanzu ta murmure ta soma magana sama sama tunda dama surutu ba ɗabi’arta bane.
Shiru yayi baice komai ba, ya rasa Dalilin zuwan shi gidan.
“Lafiya dai koda wani matsala ne?”
“Lafia lau Mommy” ya amma yana inda inda.
Suna cikin haka saiga Abla ta shigo cikin falon tareda sallama. Deela da fara’arta ta daga ta kalleta “Wata sabon gani, Abla kin share ni”
“Ba haka bane Momyn Pha’eexah, Boss dina tayi tafiya zuwa Abuja yasa nike komai a office. Wallhi Yanzu banida wani isarshen time”
Zama tayi akan Couch na 2 seater Kusa da Fadeela, “Ina wuni Anty?”
“ina gajiya Abla ya aiki?”
“lafiya ya gida?”
“Alhamdulillah, yasu Mamanki?”
“Duk kalau suke”
Suna gaisuwa amma attention ɗin Khattab yana kanta, tabbas itace ke masa sukuku cikin rai kuma dalilinta yazo gidan nan. Soyayyarsa da Miemie yayi zurfi yanda bazai iya maye gurbinta da wata mace ba amma ya rasa gane dalilin da yana jin wani iri idan yayi tunanin Abla.
“Ina wuni Khattab” Abla tace, dayake yayi zurfi wajen tunani saida ta sake maimaitawa kafin ya amsa.
“Lafia lau” ya iya cewa saboda yadda zuciyar sa yake gudu da sauri. Mikewa yayi ya tafi.
Kai tsaye ɗakinsa ya wuce, kanshi ya soma mashi zafi gashi zuciyar sa yana mashi wani irin barazana. Sam baya so ya yarda cewa yana san ta ne, amma ya kasa daina tunaninsa.
Saida ya ganta ya lura ba Miemie yake tunawa ba illa ita. Tirkashi! Yanzu ya zaiyi? Haka yake tunanin yadda zaiyi over coming problem ɗinsa.
Ya yanke shawarar yaje ya sameta saboda zuciyarsa yana mashi barazana bugawa idan bai samu abinda yake so ba.
Bayan Isha ya tafi gidan gona, a bakin gate Mai gadi ya faɗa mashi cewa ta tafi gidansu. Dayake ya taba kai Miemie gidan sanda take raye so bai wahala ba.
Ya aika ayi mashi iso da ita, shikuma yana zaune cikin motarsa yana addu’a saboda gabansa yanata faɗi na rashin dalili. Ita kuma tana kwance akan gado ta gama rubuta wani proposal haka.
Whatsapp ta shiga tana ɗan karance karance littafin hausa mai suna “A Dalilin Mene” wanda UmmieeJafar ta rubuta. Maigadi yayi sallama wai ana nemanta a bakin kofa.
Koda ta tambaya wanene yace gaskiya cikin dare ne kuma baiga fuskarshi ba,saidai ya ce ai mashi iso da Abla. Dayake ta riga tayi shirin kwanciya, saita daura dogon riga da kuma Hijab wanda ya wuce gwiwanta da kadan.
Sallama tayi data isa wajen motarsa, ya fito yana jingine. Saida ya amsa ta gane Khattab. Nan taji gabanta ya faɗi saboda idan abinda take tunani yake so yayi zata tsayar dashi tun kafin komai yayi nisa.
Na farko dai ita ba Miemie bace, saboda haka babu gurbin dazata maye mashi. Bayan sunyi gaisuwa sai sukayi shuru na kusan minti biyar , kana ganinsu kasan akwai tension tsakanin su.
Kawai nazarinta yakey, tabbas wannan ba Miemie bace, koh ɗabi’un su ya bambanta sosai. Miemie bazata taɓa ganinsa tayi shiru ba, saidai kuma Miemie tana sanshi, wannan babu wani abu datake ji mashi a ranta.
Haka suka gama tsayuwa ya kasa cewa komai sai kawai yayi mata sallama ya tafi. Itama sallama tayi ta wuce cikin ɗaki.
Abla irin matan nanne masu kwarjini da ba kasafai zaka iya gaya masu aininhin abinda ke ranka ba. Ita ma taji dadi bai kawo mata wani shirmeba.
Bawai tanada wani tsayayye bane amma bata tunanin zata iya soyayya dashi, ita tana ganin cin amana ne wajen mai rasuwa Miemie.Babu abinda bata sani na Khattab daga abincinsa, kayansa, colors da sauran abinda ya dace wani ya sani akan ka. Miemie idan ta dawo daga taɗi takan bata labarin shi sosai.
So wannan amanar yasa bazata iya betraying trust ɗinta ba even in death. Kawai Khattab ya dauki na damu ya nema wata chan daban.
Shikuma yanzu duk bayan kwana biyu sai yaje dubata, sometimes ya kanyi siyayya ya kai mata. Bai taɓa faɗa mata dalilinsa na zuwa ba, asalima basa hira daga gaisuwa sai bayan wajen 20mins haka ko 30 sai ya tafi shikenan kuma sai gobe ko jibi. Infact ko number dinta bashida shi itama haka batada nasa.
Duk sanda ya zo ya tafi abu ɗaya take faɗi a ranta, ‘Iska na wahalar da me kayan kara”
Shikuma yasan cewa every disappointment is a blessing in disguise, baisan abinda zai faru nan gaba but he is optimistic about everything. Yasan cewa Allah baya baka abinda bazaka iya handling ba.
Komai rabo ne da kuma lokaci, idan babu rabonka a cikin abu duk yanda kaso bazaka samu ba, dama zabin Allah yake nema a koda yaushe.
#NiDaDiyata
_Yarinya Mai DIMPLΣS_
Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top