Thirty-nine


An-Nawwas bin Sam'an (May Allah be pleased with him) reported: I heard the Messenger of Allah (Sallallahu 'alaihi wa sallam) saying, "The Qur'an and its people who applied it, will be brought on the Day of Resurrection preceded with Surat Al-Baqarah and Surat Al-'Imran arguing on behalf of those who applied them."[Muslim].

*******

Kuka Abla ta fashe dashi ta kasa magana, “Ki fada min wacece mana tunda ke kin ganeta
   “Anty ki kalla da kyau mana, yanzu baki gane wannan Anty Anisa bace?” Ras! Gaban Deela ya faɗi, kara kallon video din tayi kuma lallai babu makawa wannan Anty Anisa ce. Kuka ta barke dashi wiwi saboda bata taɓa tunanin Anty Anisa zatayi haka ba.
      Anty Anisa ta kasance mace ce mai mutunci, batada kyashi ko kadan. Duk cikin asibitin anfison ayi mu’amala da ita. Gata da bala’in fara da tausayi. Ko sanda Fadeela ta haihu haka tayita ɗawainiya da ita. Kowane safe kafin ta tafi aiki saita duba ta. Sun zama kamar yan uwa cikin kwanaki kalilan.
     Video din na cikin playing kanshi sai aka kyallara Anty Anisa da goyo a bayanta. Anan kuma kallo ya koma sama wajen Deela. Kuka tayita rizgawa saboda kowa yasan Anty Anisa shekarar ta goma da aure amma bata taɓa batan wata ba.
      Anty Saudah ne ta shigo domin taji dalilin kukansu, anan Abla ta nuna mata itama. Nan kafarta ya soma rawa saboda tashin hankali. Bakin gado ta samu ta zauna tana jimamin wannan abu.
   Wai yanzu ace mutum bashida tawakkali, idan zata dauki Pha’eexah meye na kashe Miemie kuma. Saidai kuma tasan cewa Miemie bazata bari a dauki Pha’eexah hakanan ba babu wani dambe.
     Fadeela nata kuka bata ma iya cewa komai, babu mamaki idan ciwonta ya tashi ne. Anty ce ta kira Naufal da Abba a waya wai suzo yanzu yanzu.
    Naufal a rude ya tashi duk zaton sa Fadeela ta rasu ne, Yasmeenah tana tambayarsa amma bai kula ta ba. Addu’a yakeyi kawai kada worst nightmare ɗinsa ya zama gaskiya. Shima Abba tunaninsa kenan.
     Nan aka zayyana masu tareda nuna masu video, cikin kuka murya kasa kasa Deela tace bata tuna sanda Anty ta tafi ba saboda kwata kwata basuyi sallama ba. “Dama ni na tsaneta wallahi” Naufal yace
     Anan aka kira baban Khattab aka gaya mashi. Nan take ya kira ma’aikatan shi wanda suke wakiltan case din domin su soma aiki gadan gadan.
      Haka aka kwana ranar cikin kunci sabida bakin ciki sabo fal kamar ranar akayi mutuwar. Naufal bai koma gida sai wajen shadayan dare. Haka Yasmeenah tayita zumbure zumbure kamar zata fashe.

Washe gari wajen karfe 8, Yan sanda Uku ne a bakin Asibitin. Nan aka soma masu tambaya daya bayan daya akan al’amuran Anty Anisa. Kowa ya shaideta akan kyawawan ɗabi’unta. Kuma gashi ba’a faɗa masu dalilin tambayar ba. An tambaya sabon address ɗinta Kokuma number ɗinta amma babu wanda ya sani.
       An kuma tambaya inda mijinta ke aiki amma shima wayam saboda ya canza aiki dab da tafiyarta. Anje tsohon inda yake aiki amma ba’ayi dace ba saidai number ɗinsa.
      Nan take akaje Company ɗin Airtel tareda police report direct wanda IG ya rubuta masu. Daga nan sai akayi tracing number ɗin. Anan aka gane ba Port Harcourt takeba kamar yadda tace.
     Tana cikin Abia state ne a wani gari da ake kira Isiala Ngwa. Anan aka kira police din state ɗin suje su duba asalin zancen.
     Motaci uku ne shake da yan sanda da kuma mobile police akan babura suka nufa hanyar garin. Sun isa sai babban cikin su yayi knocking a kofar gidan. Da kanta ta bude saiya fara mata bayanin yana so ya bincika cikin gidan saboda wani case dayake aiki akai.
     Da sauri tayi kokarin rufewa saboda tasan zancen dayake yin magana akai. Nan take ya hankade kofar kafin ya rufe. Wawan mari ya wanka mata kana wasu yan sanda da bindigogi suka sauko daga cikin Hilux dinsu.
         Wata yar sanda ta hamɓareta da kafa kana tace, “Yeye woman see how you fine reach but you go dey steal pesin child, Ewu(akuya)” Anan yar sandan ta saka mata handcuffs sai sauran suka shiga cikin gidan gadan gadan.
       Mijin Anty Anisa yana kan dinning yana karin kumallo sai kawai yaga yan sanda sun dunkareshi, wani sergent ya wanke fuskar shi da mari.
     “Kaine kake ajiye yar sata koh?”
“Ranka ya dade yar sata kuma?”
“Ina yarinyar take?” kafin su karasa magana saiga Pha’eexah tana rarrafe ta shigo falo. Wasu yan sanda suka maza suka dauke ta.
      Nan take ta tsandara ihu, “Yi shiru Ihsaan ba abinda zai faru dake” Anan aka tasa keyar Anisa da Mijinta Aysar zuwa office din yan sanda.
     Su kuma su Naufal sun hau private plane din office din babban Khattab zasu Abia domin ayi dasu. A cikin jirgin akwai Naufal, Abba, IG, Grand Kadi sai Khattab.
     Ita Deela tace zata amma aka hanata zuwa, dole ta hakura ta zauna a gida. Daren ranar ta kwana tana sallah saboda bataso taji wani labari ko Pha’eexah ta mutu ko wani abu.
        Su Anisa da Aysar suna nan tamke a bayan canta, An kwace ma Anisa dan kwalinta da takalmi haka kanta bude, shima Aysar babu hula kansa da kuma takalmi. 
        Su kuma yan sanda nan suka bude chapter dinsu, ashar suketa watsa masu kowa naji. Har sauran wanda ke cikin cell tareda Anisa saida suka zageta. “Aboki naso u wicked reach, ahhha i no fit kill pesin as u see me so. Na fight i fight with my madam na him i enter here....  I swear you are wicked” saita mauje ma Anisa baki kuma tace idan tayi kuka saita kusan karya ta.
        Shikuma Aysar abin mamaki yake gani wai ance sunyi sata, su dai Ihsaan dinsu watace tayi cikin shege a asibitin su Anisa shine ta basu kyauta. 
       Su Naufal an ajiye su a cikin conference hall zaa fara maganar case gadan gadan. Su Anisa an shigo dasu daure da handcuffs saboda ga Grand kadi basai an shiga Court ba.
     An kawo baby Pha’eexah ta girma sosai tayi wayo. Tun kafin a soma Magana DPO ɗin wajen yasan cewa yarinyar Naufal ce. Ga kalan idanun ga kuma yanayin fuskar.
         Shima Aysar yana haɗa ido da Naufal yaji kunya saboda yasan shine babban Ihsaan dinsu. Shi aka fara tambaya yayi bayani.
      Nan ya zayyana masu cewa Anisa da dadewa tace zatayi masu adopting yaro. Toh sai kuma akayi transferring dinshi. Kiran shi tayi wai ta samu kuma ita zata bar aiki sabida tanaso ta raine yarsu da kyau.
      Shi bai zirgi komai ba saboda har magana yayi da uwar yarinyar sanda aka haifeta, kuma suna waya akai akai.
     Dukda bayanin da yayi saida aka zazzage shi tas kuma aka bashi daurin shekara ɗaya da rabi a gidan yari.
        Shiru akayi sabida anzo wajen gwaskar watau Anisa. Su Naufal basu ce komai ba, shi ko Khattab wasu hawaye suka taru masa cikin ido. Tabbas yasan Anisa saboda sun haɗu a asibiti kuma suna shiri da Miemie sosai. Domin har tana cema Miemie bazata bari tayi aure ba sai tayi masters. Ita kuma Miemie tayita zumbure zumbure daga nan.
      “Ke kuma Anisa fara bayanin ainihin abinda ya faru?”
   “Ranka ya dade babu abinda zance saidai kuyi hakuri”
     “Waye sa’anki anan... Ki fara bayani nace” IG ya zare mata ido. Kuka ta fashe dashi wanda tun dazu takeyi saita ce, “Kuyi hakuri bada gangan naso na kashe ta ba, dama naso na firgitata ne amma saita kamani da dambe wai bazata bani Pha’eexah ba”
    “Ba abinda muka tambaya ba kenan, daga farko zaki fara bayani”
    Shiru tayi batace komai ba, wata Yar Sanda taje ta wanketa da mari, nan take jini ya barke mata ta hanci. Yar sandar tace, “Oga Abeg give me 5mins make i handle dis idiot”
     Wani Dan sanda daban ya nufota tareda hamɓarinta, sai kuma ya shaketa kamar zai cire mata rai. Bata ma iya ihu saboda azaba, hawaye kawai takeyi. Da hannu tayi alama ya daina zatayi magana. Yanka mata mari yayi guda biyu tukun saiya sake ta. Kallon dayan yar sandan yayi kana yace, “see how it is done”
   Dariya tayi saita ce, “you try small” kallon Anisa tayi dake zaune a kasa, harara ta watsa mata saita mike da sauri. Cikin kuka ta soma magana.
     “Banyi niyyar cutar da Fadeela ba, kamar Kanwata na dauketa amma kafin taga Pha’eexah na rigata. A hannuna ta fito. Nan take soyayyarta ya shiga raina. Bana wani tunani sai nata”
       “Toh dama nayi ma mijina magana zanyi adopting amma ban samu ba, shine nace bari na tafi da Pha’eexah garin nan babu wanda ya sani. Toh wata mata makwabciyar mu nake ba kudi ta kira a matsayin mahaifiyar Pha’eexah”
    “Shikuma Aysar nace masa watace tayi cikin shege kuma batada wadata yasa ta bani ita, sai muka ce zamu rinka kiranta Ihsaan.”
      “Saidai kuma Miemie tana bani matsala, koda yaushe tana tareda ita, har labari naji tare ma suke kwana, kwata kwata bata bari ta huta suna tare”   daga nan sai Anty Anisa ta fara magana cikin faɗa faɗa tana zare ido kamar yar daba.
      “Shine kawai nace zanyi maganinta, banyi niyyar kashe ta ba saboda ban iya kisa ba, kawai naso nayi mata shegan dukane kuma naɗan karya mata wani sashe na jikinta”
    Salati kowa keyi saboda idanun Anisa bashida maraba da yan ta’adda. Itama magana takeyi tana zare ido kamar ba mutumiyar kirki mai shakenken murya da suka sani ba.
     “To sai nayi gurizin sledgehammer daga kasuwa abina, na fada ma Deela zan bar gari saboda bana so a zargeni. Naji dadi da Amaryar Naufal tazo sai hankali Fadeela ta fita daga kaina”
     “Sun fita zasu rakata sai naga Miemie zaune da Pha’eexah kamar yarta, shine na sidada na shiga anan muka soma kokawa. Nayi mata alkawari idan bata matsa min zan kwada mata amma taki”
      “Shine na auna mata, amma ba akai naso auna mata ba. Tsautsayi ne wannan. Ina ganin yadda jini ya fara fita daga kanta. Tana rokona nayi hakuri na taimaketa, amma lokacin bana jin kira na kyaleta bansan ko ta mutu ba”
       “Wajen cradle din Pha’eexah naje, kyakkyawa mai shiga rai. Nan take na dauke Diyata na goya a baya. Sai kuma nayi tunanin idan forensic suka shigo zasu ga prints dina a wajen. Saina goge inda na taba, cradle, jikin Miemie etc. Saina fasa turare tareda kyasta ashana”
       “Daga nan saina rufe kofa na tafi da key” kuka ta fashe dashi saita durkusa kasa. “Dan Allah karku rabani da Ihsaan dina, itace farin cikina. I deserve to be a mother, please kada ku raba NI DA DIYATA... Bani na haifeta ba but she is mine”
       Naufal ne yaje ya wanketa da mari, “Bakida hankali, Allah ya isa tsakanin mu dake bazamu taba yafe maki ba. Kuma Allah saiya binma Miemie hakkinta.... Shashasha muguwa azzaluma”
      Saiya dauki Pha’eexah amma taki sakewa dashi, kuka ta fashe dashi saboda bata san shi ba. Kallon Anisa takeyi tana mika mata hannu alamar tazo ta dauketa. Dariya Anisa tayi sosai saita ce, “Kuna ganin kun raba Ni Da Diyata amma abinda baku sani ba shine bazata sake daku ba saboda ni ta sani, kuma sai kun shiga kuncin da kuka saka ni”
        Kallonta ake yi saboda kamar tanada tabun hankali, if not ga iyayen yarinya amma tana kiranta Diyarta. Grand kadi ne yanke mata life in prison, abinda yasa yayi haka bai bata ɗaurin rai da rai ba saboda idan akayi mata wannan nan take zaa wanke mata laifinta wajen Allah, amma idan aka bata wahala a duniya kuma taje lahira ta hadu da Mahaliccinta.
       An kuma barta a Prison din Abia saboda koba komai kabilu zasu ci ubanta sosai, shikuma Aysar Bauchi aka mayar dashi. Nan take yayi ma Anisa Allah ya isa tareda saki uku kyawawa.
     
      ********
Ita ko Fadeela Naufal na gaya mata anga Pha’eexah gatama a hannu sa, kukanta taji ta waya, abin yayi mata ciwo amma tasan idan suka ba yarinyar lokaci zata saba dasu itama.
     Tun daga waya Naufal ya soma ma Fadeela maganar komawa, “Baby we have been through alot, kawai ina tunanin ki dawo dakinki mu raina Pha’eexah tare please”
     “Okay in sha Allah” dama itama abinda suka gama magana da Anty Saudah kenan. Yanzu an saka one week saita koma.
     Sun dawo garin Bauchi kowa sai murna yakeyi, saidai kana ganin Pha’eexah kasan tana jin dadi saboda jikinta yayi fluffy yayi kyau. Deela bata damuba da Pha’eexah bata sake da ita ba, tasan cewa komai lokaci ne. Yarinyar tafi sakewa da Mommyn Deela, ita ke bata abinci da goyata.
  Shikuma Naufal yaje Chuchu Stores ta ɓangaren furnitures yace suzo su canza ma Deela kayan ɗakinta duka. Komai aka canza saidai the same colour ne.
      Yasmeenah ta shiga tashin hankali sosai saboda yanda Naufal yake rawar kai anga Pha’eexah gashi kuma Fadeela zata dawo. Tunaninta daya, saboda bazata iya zamada kishiya ba wallahi musamman yanda ta saba wataya wa ita kadai.
      Dole ta nema yanda zata ruguza abin as soon as possible.




#NiDaDiyata







#AinauMardiyah

Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top