Thirty-eight
Abu Hurairah (May Allah be pleased with him) reported: The Messenger of Allah (Sallallahu 'alaihi wa sallam) said, "There are two statements that are light for the tongue to remember, heavy in the Scales and are dear to the Merciful: 'Subhan-Allahi wa bihamdihi, Subhan-Allahil-Azim [Glory be to Allah and His is the praise, (and) Allah, the Greatest is free from imperfection]'."[Al-Bukhari and Muslim].
********
Wani Laraba haka wajen sha biyun rana, ina zaune cikin Office dina saiga Sadeeq ya shigo. Bayan munyi sallama sai yayi min korafin yunwa.
Nan take gabana ya faɗi saboda gidana ba inda za’a kai bako bane, Aminu shima ya shigo wai a dole sai sunje gidana cin abinci. Babu noke noke da banyi ba amma sukayi burus dani.
Haka na tashi ina Hasbunallahu wa ni’imal wakeel inatayi har muka kai gidana. A parking lot mukaga Motar Huzaifa, nan jikina yayi la’asar. Yanzu Huzaifa bashida timetable na zuwa gidana, baisan safe balle rana. Koda yaushe zuwa yakeyi.
Su kuma su Huzaifa da Yasmeenah sun zama besty 5 and 6. Suna jin daɗin company ɗin junarsu. Babu tashin hankali da batayi dani akan abin kuma na nuna mata bacin raina amma tayi kunnen uwar shegu.
Suna zaune a falo suna kallon sabon India mai suna ‘Dilwale’ wanda Kajol da Sharukhan sukayi acting. An kai wajen wani waka haka sai Yasmeenah tayi rewinding ɗinsa daga farko. Toh dama laptop din Huzaifa suke kallo dashi.
Nan ta soma babbaka rawa, su crip walking takeyi saita haɗa da azonto daga nan sai tayi ending dinshi da dab.
Su kuma su Naufal ana cikin tafiya akaji karar waka, nan take raina ya ɓaci. Gashi kuma nazo da baki. Yau tabbas sai na ji kunya. Dama duk wanda baiji bari yaji hoho!
Fatana ɗaya kada na risketa tana zabga rawa tunda karamin aikinta ne. Aikuwa kaddara ta riga fata saboda babbaka rawa take yi abinta. Sororo muka tsaya bakin kofa muna kallonta.
Huzaifa yana daga kwance ya hakince a 3 seater kai zaka ranste shine mijinta. Amshi yake mata “Go Meenah! Go Meenah!! Go go go Meenah !!!” ita kuma sai dancewa take yi. Dariya ya bushe dashi sannan ya naushi iska tareda tafa hannayensa sai yace “Tirrrrrr yarinyar nan bakida dama wallahi”
Itama dariya tayi saita juya ta ganni tsaye bakin kofa da baki. Da gudu tazo inda nake ta sumbace bakina babu kunyar mutanen dake wajen.
“Mine ka bani mamaki bansan yanzu zaka dawo ba”
“Nida gidana saina tambaya izininki kafin na shigo?”
“No bahaka bane im not expecting you, at least ko waya da kayi min amma bawai kawai ka fado min ba without a warning” ban kulata ba saboda ina dab da marin ta, karyan iskanci takeyi nazo na iske ta tana rawa gaban wannan gwaskar shine zata wayanace.
Sai kuma ta juya ta gaida su Aminu kana tayi introducing Huzaifa as Big bro dinta.
Shikuma Huzaifa ya mika masu hannu suka gaisa, nidai ban mika masa ba saboda na tsane shi. Da baki muka gaisa saiya tafi, har yakai bakin kofa saiya juyo yace, “Lil sis gobe da safe zanzo na karɓa laptop dina saboda munada board meeting”
“okay Yaya Huzzy dont worry yau ba zanyi barci ba zan kwana ina kallo har saina gama”Daga gira yayi daga nan sai ya tafi. Ni yanda yake behaving ban taba zaton yana anything for a living ba saboda baya zuwa aiki at all, kullum yana gidana. Wata rana har Saturday and Sunday.
Shigowa falon muka yi gashi kacha kacha babu gyara, su ledan Oasis ne birjik dasu gwangwani na maltina da pepsi wanda aka sha aka rage. Ga kuma burbushin cake daga kan kujera har kasan carpet.
Da sauri taje ta fara tattara wa, gashi rigar ta doguwa ce amma ya matseta tsam. Duk wani haushi da kunya ya kamani kawai bance komai ba. Itace ta fara magana, “Please kuyi hakuri dama inaso na gama kallo ne tukun kafin nayi shara”
“Karki damu amarya lantarkin gida, ai bakya lefi koda kin kashe dan masu gida” Aminu yace yana kallon fuskar Naufal. Ni kuma haɗa rai nayi saboda nasan iskanci yake min.
Wucewa tayi ta dauko ragowar cake dasu shawarma ta kawo mana, nidai banci ba saboda yadda na tsane Huzaifa bana iya cin abinda ya kawo. Su dai su Sadeeq sunci.
Ta kwashe tarkacen da zata iya tsincewa saita ce, “Kuyi hakuri banyi abinci ba, yanzu sharp sharp zan maku taliya”
“Au bama ki daura ba kenan?” Aminu yace yana dariya.
“Wallahi kuwa, nifa house chores is not my calling, i really hate it... Kawai saboda ina san Mine ne yasa nakeyi”
“Toh fah!” Aminu yace
“Mazaaa kaji ance saboda ana sanka ne ake yi a haka” Sadeeq yace.
Ni kawai ban kula suba banda chanza channel zuwa Aljazeera na soma kallon labarai.
Wucewa tayi kitchen domin ta daura sanwa, wanke wanke ne shake a wajen. Gashi batazo da Dish washer ɗinta saboda kitchen dinta is too small. Wasu daga cikin sun fara yauki saboda tun na jiya dana shekaranjiya ne.
Haka ta matsar da wanda zata iya saita dauraye tukunya ɗaya. Saita daura ruwa akan gas, manja ta saka bata ko soya ba saita saka tomato paste. Bata saka albasa ba saboda bata so hannunta yayi wari sai kuma ta zambada barkono.
Dauko kifi tayi daga fridge mai kankara, dayake akwai sanyi dayawa, da kyar ta wanke. Ko scales din bata cire ba, haka kashin dake ciki ba duka suka samu daman fita ba.
Cikin ruwan dake tafasa ta tsumbula saita saka spaghetti ɗaya ma gardawa uku. Maggi kuwa ta saka kusan goma ma taliya leda daya.
Babu kamshin dake tashi bazaka zata ana girki cikin gidan ba, ko su Naufal mamaki sukeyi har yanzu bata daura ba saiga abinci a cooler ta fito dashi.
Ta ajiye masu akan dinning table saita koma ta cigaba da kallonta. Ta hada masu Ginger drink mai dan karan zafi, Aminu yana sakawa a baki saida ya fito dashi. Hawaye ya soma gangaro masa saboda zafin dayaji.
Sun buɗe cikin cooler sai sukaga taliya kitub ya chabe, gashi mai isheshi ba. Kawai addu’a sukayi kada yayi rashin daɗi. Sun zuba ma kansu amma bazai ishesu ba saidai managing.
Naufal ya fara kaiwa baki, zare ido yayi saiya toshe bakinsa da hannunsa. Da sauri ya dauki zuwa yakai baki tunda bazai iya shan ginger dinba. Tauna yakeyi amma abincin yaki wucewa, saida ya sake korawa da ruwa tukun.
Gaban Sadeeq ya faɗi sosai saboda a duniya abinci mara daɗi ne baya so. Haka suka ci abincin suna zare ido tareda shan ruwa, kuma kowane cokali saika kora da ruwa saboda babu inda zai wuce da kansa. Kwata kwata bashida dadi kamar an wanke kan mahaukaciya!
Sun gamaci sai nishi sukeyi kamar sunyi aikin karfi, “Amarya mun gofe fah, Allah ya saka maki da alheri da duk abinda kikayi mana” Sadeeq yayi mata ba’a.
“Haba dont mention, it’s my pleasure” ta amsa tana yauki, dayake bata ciba so bata san how horrible abincin yake ba. Ba Aminu kawai ba har Naufal saida ya bushe da dariya saboda sun san abinda Sadeeq yayi.
“Amaryar Naufal kina sha’aninki, Allah ya barku tare” Aminu yace yana kyallara ido ma Naufal.
“Amin summa Amin” ta amsa.
A hanyar rakasu sai mashi iskanci sukeyi, “Ashe dama haka kake kwasan dadi, yasa naga kayi fari fat kamar fatalwa. wannan shine kaikayi ya koma kan mashekiya”Sadeeq yace.
“Aikuwa dai, kaso musguna ma Deela babu gaira babu dalili shi ne Allah ya kama ka” Aminu yace.
“Nifa kasan har daina magana yayi min, don kawai ina bashi shawara akan ya bar zancen auren nan. Amma yanzu me gari ya waya ka dawo gida ga wani katon banza ya hakince yana kallon matar ka tana mashi rawa” Sadeeq yace yana kwafa.
“Wallahi na rasa yadda zanyi da ita ne, kamar ta raina nine” Naufal yace a sanyaye.
“Ai babu tantama ta gama rainaka, if not bazata yi haka ba, but ai duk tsuntsun daya kirawo ruwa shi yake duka”Aminu yace.
“Allah dai ya kare” Sadeeq yace. Daga nan suka yi sallama suka wuce.
**********
Soyayyar Abla sai kara zama yake a zuciyar khattab, bata bashi fuska at all. Kullum saidai yazo yayita inda inda baya iya cewa komai. Gashi har yanzu bashida number ɗinta.
Wata rana yana zaune a cikin Office dinsa saiya dauki alwashin yau zai gaya mata abinda ke cikin ransa. Ya tashi bayan yayi Maghreb saiya tafi gidan su Abla.
Maigadi ya fada mashi cewa Abla bata dawowa, dafa kansa yayi yana tunanin inda take sai kawai ya yanke shawara ya tafi gidan gona ya dubata tunda bashida number ɗinta balle ya kira ya tambayeta.
Ita kuma Deela ta samu sauki sosai, ta mayar ma Allah komai saboda yanzu har magana takeyi. Ta murmure sosai har Naufal yana tunanin yayi mata maganar komawa ɗakinta koba komai zai samu abinci sosai.
Tunda yanzu bawai yana samun abinci isarshe bane, Yasmeenah da kanta tace mashi ya rinka cin lunch dinsa a waje saboda bazata dauki nauyi ba.
Missing fadeela yakeyi sosai saboda ko kadan bazata mashi haka ba, dama Hausawa sunce idan baka gode ma alherin da Allah ya baka ba zaka gode ma azabarsa.
Ita Abla daga wajen aiki kai tsaye gidan gona ta wuce saboda Deela tanata mata korafi akan ta watsar da ita. Suna zaune akan gado suna shan fruits salad suna hira cikin dakin Miemie wanda yanzu ya zama na Fadeela.
Fadeela tace mata ta kwana ita kuma tace batada su brush da kayan sawa. “Indai wannan ne matsalar ki karki damu zan baki”
“Allah ya barmin ke matar Yaya”
Wayan Fadeela ya soma ringing sai taga sunar Khattab baro baro akan screen.
“Assallamu alaikum”
“Waalaikumus salam Khattab ya kake ya aiki?”
“Alhamdulillahi” sai kuma sukayi shiru na wasu dakikai kadan.
“Dama Anty ina kofar gidane bansan ko Abla na kusa ba kice mata ta fito”
“Eh gata gefena, babu damuwa” daga nan suka kashe wayar. Deela da fara’arta ta soma magana, “Khattab huh! Gaskiya naji dadi sosai”
Hada rai Abla tayi sosai, bata kula Deela ba kuma batada niyyar fita waje yau saboda zuwansa ba karamin takura bane a wajenta.
“Tashi mana ki fita kin barshi a waje, wulakanci bashida kyau dai”
“Saurayin Miemie ne fah!”
“Wani Miemie kuma? Wanda ta rasu ko wata daban, yarinya na ciki kabari kina lakata da wani saurayi. Koko shi Khattab din katako ne da bazai sake aure ba?”
“Nifa bawai wulakanci nakeso nayi masa bane, kawai banaso mutane su ce na kashe sister dina domin in aure saurayinta”
Deela bushewa da dariya tayi sosai. Ashe Anty tana jinsu, a hasalce ta fara magana, “Bada bakinsu zasuyi magana ba, sufa suke kiɗansu kuma suke rawar su. Fatan Alheri kawai zakiyi ki mance da komai”
“Kuma idan zan baki shawara kiji tofa kiba yaron nan haɗin kai, haba sai kace shi kadai yazo duniya, ya gama wahala da Miemie yanzu kema zaki saka mashi ciwon kai”
“Ai kuwa dai, yana kokarin sosai ga shida kamala” Deela tace. Ita dai Abla bata ce komai ba kawai zata yi nazarin abinda suka ce ne. Anty ne ta cigaba da magana, “Sau nawa kuma sai kiga Miemie bata rasu ba an fasa da ita ayi dake... Idan fa shine mijinki babu yadda zakiyi gwara kisan me kikeyi”
Haka ta tashi rai bai so ba ta saka mayafi ta wuce wajenshi, sallama tayi mashi sai suka gaisa. Daga nan tace masa su wuce cikin Falo amma yace ta barshi cikin motar sa.
Sunyi shiru for like 45mins, ita tana wasa da yatsunta shikuma ya kafa mata ido. Dama yaso ya kureta ne yaga ko zatace wani abu amma batayi ba. Tun dayake zuwa wajenta basa kai 30mins, mostly 20mins saiya tafi.
“Saidai na kashe ki amma bazaki ce komai ba” bata amsa ba kawai kanta yana sunkuye da kasa.
“Abla”
“Na’am”
“Inaso idan zaki min magana ki rinka kallona”
“Toh” saidai kuma bata kalleshi ba.
“Abla me kike min haka? banida wani tunani yanzu banda naki.... Please Abla answer me ko zanji saukin radadin danake ji.
“Ni babu abinda nake maka” ta fada a sanyaye, shikuma kaima steering duka yayi.
“Haba Abla ji yanda kike treating dina kamar nayi maki wani laifi, bafa ni na saka ma kaina ba. Allah ya daura min. Though nasan kina tunanin zanyi replacing Miemie dake ne but Wlh komai dana ke jin maki its different”
Shiru tayi kawai tana nazarin abinda yake faɗi, “Abla tunanin me kike yi? Kin tsane ni koh... Meyasa kike min haka?
“Nifa ban maka komai ba tun dazu kace nayi maka wani abu”
“Kamar ya bakiyi min komai ba, shirun nan is killing me. Nafiso ki saki jiki ki rinka mini magana please”
“Toh ai kaima baka magana”
Dariya ya soma, “Haba baiwar Allah ta ina kikeso nayi magana bayan kin haɗa rai....salan ki wanka min mari. Please oooo i like life” Murmushi kawai tayi daga nan saita soma hamma alamun barci.
Wayarshi ya fitoda akan ta karanta mashi lambarta, ita kuma sai ta amsa zata saka da kanta amma yaki, dole ta rinka kiran masa yana yi da kanshi. Saidai kuma idan tace 7 sai yace 5, haka taketa gyara masa har suka gama.
Da gangan yayi mata haka duk salon bata lokaci da ita kuma tace wani abu ko babu dadi. Yayi alkawarin kiranta anjima yaji amsar da zata bashi akan batun su.
Nan yayi flashing number dinsa sai yace tayi saving ya gani, Khattab ta rubuta mashi.
“Haba mana, Khattab kawai zaki rubuta. Babu dan Baby ko Sweetie yanda yan mata keyi” dariya kawai tayi tana mamakin yanda he is free and very fun.
“Okay ni bari nayi saving ki ga naki” ‘Haskena’ yayi storing dashi. Nan fuskanta ya canza saboda kowa yasan Miemie ce Haskensa. Dariya yayi saiya ce, “Allah ya bani Haske da farko sai kuma ya dauke mani ita. Nayi dangana shine ya sake bani wata”
Daga masa kai tayi alamun ta gane. Itadai kawai tana tunanin irin amsar dazata bashi anjima ne.
Tana isa daki taga Deela tana gyara drawer, kayan suna ne take sake jerawa da kyau. Daga nan sai suka ga Cd plate da aka yi video covering amma basu kalla ba. Fadeela nata ninke kaya daga gefe ita kuma Abla ta dukufa tana kallo a laptop.
An nuna Miemie sosai saboda ko ina tana wajen kamar MTN, ga shi little One itama sai dariya takeyi. Video din yana kunshe da happy moments sosai.
Ita kuma Deela cin karo da kayan Anty Anisa tayi, “Allah sarki baiwar Allah tana chan port Harcourt” Deela tace cikin ranta. Haka ta gama ninke kayan ta ajiye cikin drawer. Saidai kuma wani abin mamaki bazata tuna sanda sukayi sallama da itaba.
Though kuma dai akwai jama’a gashi kuma ya dade da faruwa saboda kusan wata shida kenan idan baima fiba.
Abla na cikin kallo saita tsandara ihu saboda sledgehammer din da akayi amfani wajen kashe Miemie ta gani cikin video.
‘Haba Abla meye na ihu kamar ba musulma ba, ni duk kin firgita ni”
Hawaye na gangaro mata tace, “Nasan wanda ya kashe Miemie”
Da gudu Fadeela ta karasa wajen domin ta gani itama, Abla tayi rewinding amma Deela bayan mutum take kallo. Gashi kuma bata gane ko wacece ba.
“Abla nifa bangane ba.... Wai waye wannan? Kin ganta ranar suna ne?”
“Eh mana Anty, baki gane.......”
#NiDaDiyata
#AinauMardiyah
Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top