Thirteen
On the authority of Anas, who said: I heard the messenger of Allah say: Allah the Almighty has said: "O son of Adam, so long as you call upon Me and ask of Me, I shall forgive you for what you have done, and I shall not mind. O son of Adam, were your sins to reach the clouds of the sky and were you then to ask forgiveness of Me, I would forgive you. O son of Adam, were you to come to Me with sins nearly as great as the earth and were you then to face Me, ascribing no partner to Me, I would bring you forgiveness nearly as great as its." Related by Al-Tirmithi, who said that it was a good and sound Hadith.
******
Muddin an tsayar da lokacin abu toh inda rai da lafiya sai anyi. Yau Asabar kuma yazo daidai da ranar tarban lefen Fadeela.
Lefe yana daga cikin al’ada na Mallam Bahaushe idan zaayi aure, ya jiɓanci kawo kayan sawa dana amfani daga dangin miji zuwa ga amaryarsa. A al’adan daya gabata ana kaiwa a cikin kwalla ko makamancin haka, amma yanzu zamani yazo da su akwati seti seti.
Toh dayake Fadeela yar zamani ce itama akwati aka kai mata, akwatuna guda goma sha huɗu watau seti kala uku wasu ‘yan huɗu wani mai shida.
Kamar yanda al’ada ya nuna, ana taruwa a gidan Amarya tareda yanuwa, makwabta da abokan arziki. Ana tanajin su kayan motsa baki kamarsu Sambousah(Samosa), Meatpie, spring rolls, peppered chicken or meat etc Wanda za’a bama dangin miji as tukwici.
Mommy itama ta tsaya a tsaye saida taga an tanaji komai na bak’in. Anty Saudah itace a gaba wajen ganin komai ya kankama daga ɓangaren su, mota uku sukayi aka dunguma GRA inda gidansu Fadeela yake.
Kowa ya hallara a babban falon Grand Kadi ana zaune, Anty Uwani ta buɗe taro da addu’a sai aka fara. Gwaggo Mahaifiyar Grand Kadi aka mik’a ma trinket box.
Ran Anty Saudah fari sol saboda bataji kunya ba, itama Mommy ta yaba da kaya saboda komai yaji Tabarakta Masha Allah.
“Wai banga Amaryar bane?” Anty Saudah ta Faɗa
“Eh nima inaso na ganta” Miemie ta chapke.
“Kunsan ta da kunya, wallahi tun jiya ta dawo gidana kada ku riske ta” Hajia Rabi matar big Daddy ta amsa.
“Babu komai muda zata dawo cikin mu da zama” Anty Saudah ta faɗa tana dariya.
“Allah ya Kaimu lokacin, yasa ɗakinta ne ya kuma basu zuri’a ɗaiyiba” Maman Humairah makwabciyar su Fadeela ta faɗa.
“Amin summa Amin” kowa ya faɗa.
Daga nan sai aka basu tukwicin kuɗi tareda na abinci aka watse.
In ran Miemie yayi dubu to ya ɓaci, taso taga amaryar amma bata samu dama ba. Dayake da Abla akaje sai tayi mata raɗa ko suje gidan Hajia Rabi don suga Fadeela. Harara ta daka mata wanda ya natsar da ita.
Ita kuma Fadeela tun jiya take kuka data lura abin da gaske ne. Yanzu saura sati biyu cur a daura mata aure da wanda baya santa. Ko sau ɗaya bata taɓa tunanin haka zai faru ba.
Ita irin Telemundo gal ce, batada wani buri daya wuce tayi zaman soyayya da mijinta thou bawai ta taɓa yin shi Soyayyar bane, but still!
Kuka tayi babu k’akkautawa tana k’okarin ta tattara tunaninta waje ɗaya ta gano dalilin da Naufal ya tsaneta amma ta kasa ganewa, ita dai ba wai ta sanshi bane daga wani waje balle ace wani abu. Kawai dai ta lura idan ya ganta har wani jijjiga yake saboda bala’i.
Tashi tayi tsam ta wuce bayi ta daura alwala, sallah raka’a biyu tayi tareda mayar ma Allah komai. Tasan cewa nata jarabawar kenan kuma tana fatan taci da flying colours.
Bayan la’asar sakaliya Hajia ta dawo daga wajen tarban lefe, washe baki kawai takeyi tana murna.
“Amma ‘yannan kinyi tagomashi. Lefe sai kace na yaran sarakuna kokuma masu gwamnati” Hajia Rabi ta faɗa
Murmushi kawai Fadeela tayi ta cigaba da kallon wani reality program a ‘E’ mai suna The Rich Kids of Beverly Hills. Hajia Babba sai kawo mata maganar lefen takeyi amma bata sakar mata fuska ba, dolenta ta hakura da hirar.
******
Kullum sai Khattab yaje k’ofar gidansu Naufal sau biyu ko uku amma baya samun damar yaga Miemie.
Sau biyu yana riske Naufal amma baya bashi dama ya shiga. Babu irin magiyan da rok’o da bai yiba amma ko kulashi baiyi ba. Ita kuma Miemie tafiya Naufal ya faɗa mata Khattab yayi, harda karyan cewa ai randa yazo sallama yayi mata saidai bata lura ba.
“Allah ya dawo dashi lafiya” abinda kawai ta iya faɗi kenan saboda tasani sarai k’arya yakeyi.
Sau da dama Khattab yana zuwa makaranta Miemie amma Naufal har cikin school yake shiga da motarsa ya dauko ta. Da abin ya isheshi saiya mayar da ita gidansu wajen Mama wai tayi mata hutu tunda yasan Khattab baisan wajen ba.
Shi kuma Khattab abubuwa sun cunkushe mashi, na farko an hanashi ganin Miemie. Na biyu kuma jarabar Lili, tariga ta raina shi kamar mijinta ko sa’anta. Kullum suna cikin bala’i kamar kaji kuma koda yaushe Mommy tana mara mata baya.
Fatan shi ɗaya next week Mommy Zata tafi Ummarah kuma gashi Daddy ba mai zama bane, Lili tana mashi yayi mata ɗan iskan duka da saita raina kanta. Ya ɗauki alwashin saiya saisaita mata duk wani rawar kan datake tak’ama dashi kuma gashi mai cecenta bata nan.
Sam Khattab bai iya tashin hankali ba sai sanda ya dawo gida bayan yayi graduating Masters ɗinshi a Almadina University dake Shah Alam Malaysia. Ya karanta Information Technology kuma yanzu haka yana serving a wani ICT center haka Thou ba kullum yake zuwa ba.
Khattab dai fari dogo ne, yanada cikar halitta kuma fuskar shi akwai saje wanda ya kara k’awata wajen.
Shi cikakken bakano ne a wani gari da ake kira Danbatta. Mahaifin shi IG Hamza Aminu Danbatta ya aure mahaifiyarsa Hajia Shatu kumaAllah ya albarka cesu da yaro ɗaya tilo watau Khattab.
Bayan wasu shekaru sai k’anin IG watau Alhaji Ibrahim ya aure k’anwar Hajia Shatu. Sun haifi yara uku, Usman, Halima wanda ake cema Lili sai auta Lubna.
Lili shekarunta 19 a duniya kuma tana School of Nursing and midwifery dake ATBU a garin Bauchi. Yanzu haka tana 3rd year ɗinta.
Kyakyawan yarinya san kowa k’in wanda ya rasa saboda Allah bai rageta da komai ba wajen fannin halitta, in hasken ne tana dashi, tsawon gashin shima kazo wajen, shape kamar an zana number ‘8’, zak’in murya ka samu.... In fact everything.
Saidai dama ɗan adam tara yake bai kai goma ba, kyau kawai gareta babu halin kirki. Yanda kasan empty vessel ko fanko to haka take. Kwata kwata batada daɗin sha’ani. Bata iya magana ba at all, duk abinda ya fito daga bakinta zata yaɓa maka kuma ko taji kunya saidai na gefenta su ji. Ga tsiwa ga rashin kunya ga kuma bala’i koda yaushe kamar dage.
Tun kafin Khattab ya dawo daga school Mommy ta dauko Lili ta dawo da ita gidan saboda yana dawowa yayi arba da ita su fara soyayya. Duk mugun halin Lili Mommy bata gani, ko tana mayar da abin yarinta ne ko kuma menene dalilinta Oho?
Sau da dama Lili na chaba ma Mommy magana amma sai Mommy ta kauda kanta. Sanda Khattab ya dawo yaga Lili yayi Na’am da batun Soyayyar su saboda yar gaban mota ne, but daga baya daya lura da halinta saiya fara ja da baya da ita but yanzu dai it’s too late saboda Har Iyaye maza sun shiga maganar.
Shi Khattab mutum ne mai san girma kamar gyambo ita kuma Lili akwai k’ask’anci, yasa idan suka fara gardama basa tsayawa. Tun yana kyaleta amma yanzu ya dauki alwashin tana mashi zai rama, when it comes to Lili to bayada hakuri kamar zawo.
Shidai ya gwammace ya zauna da wanda rashin hankalinta ciwo ne kuma idan sauki yazo mata tanada daɗin sha’ani da yazauna da Lili, Wannan kenan!
#NiDaDiyata
Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top