Seventeen
Jabir bin 'Abdullah, may Allah be pleased with them, narrated that Allah's Messenger said: "The key to Paradise is Salat, and the key to Salat is Wudu'." (Hasan)
It was narrated from Abu Hurairah that The Messenger of Allah said: "When it is very hot, then wait for it to cool down before you pray, for intense heat is from the flaring up of the Hell-fire." (Sahih)
**********
Six months later.....
Hakuri shine gishirin zaman duniya, kuma ainun Fadeela tayi exhibiting ɗin wannan abu. Babu abinda Naufal baiyi mata ba na cin zarafi kuma duk ta shanye.
Ko sau ɗaya bata taɓa tunanin zata faɗa ma Mommy ba ko Jawahir, ita kawai tasan nata jarabtan kenan. Sau biyu taje gidansu kuma shima sallah babba da karama ne.
Saidai kuma bai takura mata akan karatu, ya kyaleta ta cigaba amma koda wasa bai taɓa rage mata hanya ba. Idan kuma tanada 8am class toh tun wajen 4am take tashi tayi breakfast and lunch duk ta saka a cooler.
Azumi kuwa na Monday and Thursday baya wuceta Muddin tana cikin lafiya, ma’ana idan tana sallah.
Daga ɗayan ɓangaren ana nan ana fafutukan neman ma Miemie magani, Shidai Khattab har yanzu babu zancensa babu dalilin sa.
Sau da dama idan ciwon Miemie ya tashi Naufal ya rasa tudun dafawa sai kawai yaje gidansu Khattab ko office ɗin babansa ya zauna yayita rusa kuka.
The last time dayaje Sai Abban Khattab ya rantse mashi da girman Alkuran akan baisan inda yaronshi yake ba, shima rabon dasu haɗu tun text msg daya aika mashi akan ya tafi kuma daga nan yayi disconnecting layin, koda akayi tracing ɗakin Khattab ne last location.
Anan fa hankalin Naufal ya tashi sosai saboda ciwon Miemie sai gaba yakeyi. Akwai wani rana haka, Anty Saudah takaita bayan gida domin ta zaga, unfortunately ta cire mata hand cuff sai kawai Miemie ta naushe window da hannunta. Nan take jini ya soma gangaro wa kuma sai ta dauki broken glass tayi slitting wrist ɗinta.
Tashin hankali Anty Saudah ta gani mara misaltuwa saboda nan take Miemie ta sume, sau dama Miemie tayi abubuwa da zai janyo mata asarar ranta.
Akwai wani lokaci tafi One week bata kira sunar Khattab ba, kowa hamdala yakeyi ta fara samun sauki sai Naufal ya cire mata hand cuff ɗinta. Aiko basu suka ganta ba sai bayan kwana biyu.
Shima wajen data fara haduwada Khattab ne, ta zauna a gefen da ake gasa masara tanata rusa kuka, babu wanda yabi ta kanta saboda kana ganinta kasan babu hankali, gashi batada takalmi ga kai a tsefe yayi sama duk kacha kacha.
Tunda daga lokacin sukayi taka tsantsan da ita, yanzu dai basu saka mata Handcuffs akwai wani igiya haka mai yanayin beat. Shi ake saka mata kuma tana wani ɗaki ne wanda babu komai ciki sai carpet.
Wata rana tayita ihu tana buga kanta a kasa amma saboda laushin carpet bata jin ciwo. Wata rana kuma tayita kiran sunan shi a hankali tana hawaye, haka rayuwa ya kasance mata!
Duk Safe da yamma sai Naufal yaje ya dubata, da farko bata san ganinsa. Dayazo ta window inda ake lak’enta saita rinka ihu tana rufe idonta. Kullum kalmar “Ka cuce ni take furtawa”
Ba karamin tashin hankali ya shiga ba, ya kan rufe kanshi sau da dama a ɗaki yayita rusa kuka, tabbas yasan shine sila but yanzu da zai iya maida hannun agogo baya daya yi.
Amma yanzu ta rage mishi haka, tana zuwa har wajen window ta tsaya, Thou bata cewa komai but tana murmushi jefi jefi. Idan kuma time ɗin abinci da magani yayi yana shiga yayi feeding ɗinta.
Ita kuma Fadeela bata wuce One week bataje ta duba taba, abin yana burgeshi sosai amma baya nunawa, kuma ko sau ɗaya bai taɓa tunanin yabar ɗiban albarkan dayake mata ba.
Shi dama yace aurenshi zai zame mata ɓakin canji a rayuwarta, kuma daidai gwargwado yana kokarin ya nuna haka. Dukta susuce tayi fari kamar fatalwa, yasa bataso taje gidansu kafin hankalin Mommy ya tashi.
Ko Jawahir baifi sau biyar taje nata gidan ba kuma shima a gurguje ne. Kullum tana cikin waya da Mommy, “babu abinda kike nema? Lafiyan ki kalau? Me za’a yi maki?” shine tambayar datake mata kuma ko sau ɗaya bata taɓa furta abinda zai jawo ma mijinta kaskanci ba ko bakin jini.
Idan ta gama aikace aikace ɗinta saita je wani empty room haka wanda kayan art work ɗinta suke tayita painting hankali kwance. Shi kaɗai ne abinda takeyi mai kawo mata solace, idan tana yi saita mance da bakin cikin gidan aure.
******
Yau Juma’a kuma kamar kowane sati inada 8am class. Tun wajen 4am alarm ɗina ya tashe ni but ban samu daman saukowa daga kan gado ba sai wajen 4:30am.
A daddafe na sauko inayi ina murje ido bcs barci bai isheni ba. Wajen karfe sha biyu da rabi na kwanta sanadiyar projet dana farayi kasancewar mune final year student.
Kitchen naje na fara kama aiki watau breakfast kuma shima Soyayyar dankali ne wanda tun jiya da daddare na fere na ajiye abina a fridge domin na samu sauki yau.
Daga nan sai nayi jollof Rice na saka ma Naufal abinsa na rana a cooler saboda bazan samu daman dawowa da wuri ba bcs ina Missing Miemie.
Kafin na gama aiki Asbah ta danno kai gadan gadan tunda sai karfe shida akeyi. Pausing girkin nayi na mayar da komai on low heat saina wuce ɗaki.
Alwala na dauro tareda nafilar raka’atanil fijr, ina cikin azkar sai aka kira sallar karshe which nima na tashi nayi. Adduar safe nayi wanda kowane ɗan Adam ya kamata yayi sai kuma na haɗa da neman ma kaina, mijina,iyayena da al’umma baki daya tsari daga sharrin masharranta watau mutum ko aljani.
Kai tsaye kitchen na koma na cigaba daga inda na tsaya, ina ciki naji Ya Naufal ya dawo daga masallaci, murmushi nayi k’arara saboda My other half yasan darajan sallah, at all Baya wasa dashi. Saboda haka ni bana cire ran wata rana zai soni.
Nasan cewa wata rana zai gane nice other half ɗinsa Kuma nasan zaiyi alfahari dani kamar yadda nakeyi dashi. Kwata kwata yanzu bana jin haushin cin kashin dayake mun, I’m not making excuses for his actions but nasan cewa yana cikin damuwa akan ciwon Miemie, fatana kullum Allah ya bata lafiya kila nima na samu lambar zuciyar sa.
12 pm.....
Locacin ne na gama lectures ɗina, kasancewar yau Friday kuma short working day so banyi tunanin zuwa wajen project supervisor ɗina ba.
Tafe nake da Samɗa,Jumaimah da kuma Mansura k’awayena. Muna tafe muna hira hankali kwance. Samɗa ce tayi hanyar parking lot inda motarta yake.
Ihsan Baby ɗin Samɗa na dauka wanda ke tareda mai aikin ta, wasa nakeyi sosai tunda ina san yara, kallona samɗa tayi cikin tuhuma kuma kana ganinta kasan da magana a bakin ta.
“Faɗa karya kasheki” nace ita kuma dariya tayi kafin tace, “Kinsan cewa ke zaki rinka nuna masa salo da zai janyo maki hankalin shi? ”
“Wallahi kin bani dariya, meye banyi ma bawan Allah ɗinnan ba amma banza yake dauka na. Ke ni na gaji wlh”
“Ah ah Karki ce Haka, da lallami da kissa zaki sameshi. Dama Wayace maki shiga Aljanna cin tuwo ne, ai sai kin nuna juriya da hakuri tukun”
“Allah dai yasa mu dace” nace sai mukayi shiru.
A al’ada yanda ake gane matar aure a cikin makaranta mu shi ne ta hanyar mota, sau da dama idan mijinki yanada k’umban susa zai siyan miki mota amma dai banda nawa mijin. Idan na shiga motarshi to naje gaida Miemie kuma yamma yayi kuma shima ya gargaɗe ni da na daina kaiwa dare tunda shi ba driver ɗina bane.
Samɗa kawai kallon kawarta takeyi, yanda abin duniya bai dameta ba. At all bata jin kunyar hawa bus ko napep Thou kana ganinta kasan babban mace ce, idan ba wai kayi mata sanin da bane toh bazaka gane ta lalace ba.
Naufal yafi mijin Samɗa arziki nesa ba kusa ba, bazama ka haɗa ba esp yanzu dasu Mr Sutter suke ji dashi sosai.
Kudi mara misaltuwa suke sakin mashi sosai yasa indai batun maganin Miemie ne to baya damuwa, but dama sauki na Allah ne!
As usual wajen roundabout ɗin Yelwa Samɗa take ajiye Deela sai kowa ya kama gabansa.
Direct gidan gona na wuce tareda tsaraban masara a hannuna bcs of Miemie.
“Assalamu Alaikum” Na faɗa yayin dana shiga cikin falo, Anty Saudah Nagani da kuma Abba harda Mama duk ana zaune.
Nan take fara’arsu ta karo sosai which dama haka sukeyi idan sun ganni.
“Ina wuni? Ina gajiya?” na Faɗa tareda duk’awa kasa.
“Lafiya lau, ya kike?” Suka amsa
“Lafiya lau” nace.
“Bari na shiga daga cikin wajen Miemie”
Ba Abba ba har Mama akwai tuhuma a yanayin Fadeela, indai ba ciki gareta toh tabbas ana musguna mata ne, shi dai Abba saiya tsareta Thou yasan bazata ce komai ba but he wants to assure her yana side ɗinta.
Ita dama Anty Saudah tayi tambayar harta gaji but Deela batace komai ba. Tana ankare da yanda Naufal ke mata wani mugun kallo. Sau da dama tana tsare shi akan yaji tsoron Allah, “Inba dai ita tace ina mata wani abu ba, toh ni ba wani abu dake hadani da ita” abinda yake faɗa kenan.
“Hello Miemie!” Deela ta faɗa tareda shiga cikin ɗakin. Ita kadai Miemie takeso ta rinka shiga unless abinci zaka bata, toh kayi tsayuwar ka a waje.
Murmushi Miemie tayi batace komai ba, Fadeela ta karasa inda take zaune chan kurya saita zauna kusa da ita. Riko hannunta tayi tana mata murmushi tareda murzawa a hankali.
Magana tayi ciki ciki saika saka Mind ɗinka da kunnuwa kafin kaji.
“My Miemie please come back, Ya Naufal really needs you” ta faɗa tana kuka. Miemie na jinta batace komai ba sai daga bisani tace, “NI kin cika min kunne"
“Oh sorry!” ta faɗa tareda share hawayenta. Kakalo murmushi tayi saita mika ma Miemie masara, nan take ta karba ta soma cabza.
“Kema zaki biye masu ne bazaki kaini wajen Ya Khattab ba?”
“kina tunanin banida hankali ne koh?”
Fadeela batace komai ba illa kallonta, ita kuma ta cigaba da cin masara bata ɗaga idonta ba.
“Idan an kai ki wajen Khattab ɗin mai zakiyi masa?”
“Kawai ina son ganinsa ne bcs I have a bad feeling”
“Dan kina son ganinsa sai kin kashe kanki ?”
“Eh, har saina samu abin nakeso” ta faɗa kana ganin fuskantar babu wasa.
Shiru sukayi for some minutes Har Miemie ta cinye masara guda uku, Magana Miemie ta somayi.
“Ya Yaya Naufal yake? Nasan he is not alright but Kema haka. Yana miki wani abu ne?”
Ta tambaya tareda kama mata haɓan fuskanta. Hawaye kawai ya soma gangaro ma Fadeela saboda ko Miemie da bata da lafiya ta gane komai balle sauran mutane.
Da sauri ta goge tareda cewa, “Just try and be alright Naufal Shima zai zama daidai” ta faɗa cikin muryar kuka.
Tashi Fadeela tayi tsaye zata tafi sai kawai Miemie itama ta mik’e wai zata bita, “Please Anty Karki tafi ki barni, bakiga yanda suke treating ɗina ba. Please don’t leave me here”
“Miemie dont worry, zan dawo next week kinji koh!”
“Please ki tafi dani, Anty kada kiyi min haka. I promise to behave myself. Insha Allah Bazan k’ara jima kaina ciwo ba”
Hawaye ke malala a fuskar Fadeela, karasa wa tayi dab da ita tana shafa mata kumatu tareda da share mata nata hawayen.
“My sweet Miemie I’m sorry but ban yarda ba, jibe hannunki da bandage ga wani a cinyar ki. Tuntuni kike min alkawari kin daina amma last week kikayi wannan. Ko totuwan masara da zai illanta ki da kinyi dashi”
“Anty bazan kara ba Please”
Murmushi Fadeela tayi na takaici tareda sumbatar goshinta saita juya tana kuka ta tafi, muryan Miemie kawai take ji yana echoing.
“Dan Allah Anty Karki tafi ki barni, wallahi na tuba. Bazan kara ba, please kiyi min rai”
Haka ta rinka maimaitawa tana fizge fizge ta karfin tsiya, rusa kuka takeyi gwanin ban tausayi but babu yanda Fadeela zatayi.
Haka Miemie ta rinka fizgo hannunta tana kokarin kwance kanta saita kasa. Kawai zubewa tayi a kasa ta fara ihu, “Yaya Khattab kana ina ne” ta faɗa sai kuma ta fara buga kanta akan carpet tana kuka, Anty Saudah tana falo tareda Fadeela suna rusa kuka.
Itama Mama tana matse hawaye saboda Miemie abin ban tausayi ne, shiko Abba tuni ya tafi Masallaci kafin yayi missing huɗuba.
Sallah Fadeela tayi saita wuce gida, hankalin duk ya tashi. Tana isa gida saida tayi kuka ma’ishi saboda yanzu kuka shine latest hobby dinta bcs bata 3 days bata yiba.
6:30pm....
Wani dabara ya faɗo min akan nabi shawarar samɗa, bayi na shiga nayi wanka tareda ɗauro alwala. Akan dressing mirror na zauna na Fara shafa mai, Saida na lura ina kyali sosai tukun.
Body spray ɗin Victoria secrets na saka tareda turaren J’adore sai nayi light make up almost nude a fuskata. Jumpsuit ɗin Naeem Khan nasa sai na saka wani Gladiators na Giuseppe Zanotti.
Nayi kyau ainun kamar zani Red carpet, kitchen naje na haɗa ma other half ɗina White Macaroni da sauce ɗin kwai.
Na sake gyara falo tareda kunna turaren wuta da kuma spraying room freshner, tafiya nakeyi ina rangwaɗa duk practice yanda zanyi idan ya dawo.
Shikuma Naufal bayan ya tashi daga aiki as usual wajen Miemie yaje, kuka takeyi haryanzu amma bata burgima, a hankali takeyi saboda duk ta galabaita.
Sunar Khattab take faɗi kawai repeatedly, bai samu yayi mata mata ba bcs baya so yaje gabanta ya barke da kuka, ko yau a office bayan sun gama conference call dasu Mr Sutter Sai kuma sukaje wani site tareda Aminu.
Yana komawa office ɗinshi ya garke yana hawaye, duk ya gaji komai yayi masa yawa. Gashi duk abinda yakema Fadeela amma maiyar yarinya tak’i zuciya ta tafi gidansu. Ita a dole ta samu wajen zama, shi yaso ya wulakanta ta to the extend da zata tafi gidansu saiya koma wajen Miemie full time.
Saida yayi sallar isha ya koma gida, yana tafe yana tunanin salon cin fuskar da zaiyi mata yau kowama ya huta.
Shiga falo yayi tareda sallama a matsayinshi na musulmi, but to his surprise Sai yaga wutan falo a kashe amma TV yana aikinsa.
Haushi ya kamashi saiya fara sababi, “Meye aka kashe wuta salan na faɗi” saiya kunna. Zaune ya ganta akan 3 seater ta daura kafa ɗaya kan ɗaya tana mashi murmushi.
“I’m sorry! Bansan Yanzu zaka dawo ba yasa na kashe” yanda ta faɗa cikin siririn murya da kissa dole saika sosu. Da sauri ta tashi zataje ta karba briefcase ɗinsa kuma tana tafe tana rangwaɗa.
“Sannu da zuwa” ta faɗa data karasa dab dashi. Ja da baya yayi saiya ce a fusace, “keh meye haka” saiya ratsata ya wuce abinshi. Ko kaɗan bataji haushin abinda yayi ba, Infact tanaji yanzu ta fara.
Daki ya wuce domin ya kimtsa kafin yaci abinci, jallabiya ya zura bayan yayi wanka. A kan dinning table ya ganta zaune tana jiran shi fuskanta dauke da annuri.
Rai a bace ya haɗa girar sama dana kasa yana wani mazurai ya zauna akan kujera Which tun kafin ya iso ta jawo mashi, harara ya doka mata amma ta mayar masa da murmushi. Haushi yaji sosai saboda ya lura ta bala’in rainashi bata jin tsoron sa again.
Tanayi tanata baɗa mashi kamshin turarenta harta gama serving, maimakon ta tafi kamar yadda ta saba sai ta zuba ma kanta itama tana ci. A cikin yanayinta na sanya sanya ta rinka ci kamar bata so taci, shikuma jefi daya, biyu yakan kalle ɓangaren ta.
Haka har suka gama cin abinci ta kwashe ta kai kitchen shi kuma ya wuce kan couch domin ya kalle 9 o clock news na NTA.
Itama taje ta zauna akan One seater, baice komai shiru yayi mata kamar baisan tana wajen ba. Yana ankare da ita sai gyangyaɗi takeyi kanta yana rawa amma dan jaraba tana forcing kanta a wajen.
Dariya abin ya bashi kuma yau ne rana na farko da wani abu nata yasashi dariya. Data gaji dan kanta ta tashi tana tangal tangal kamar yar k’waya.
“Yaya saida safe” ta faɗa muryanta yayi kasa saboda barci.
“uhm” yace yana kallonta ta gefen ido.
Sannu a hankali ta rinka layi harta kai cikin ɗakinta, takalmi kawai ta cire ta shiga bayi domin ta kama ruwa, ta fito tana cikin tafiya sai raguwan ruwa tareda santsi na tiles ya ɗibe ta.
Tim ta faɗi a kasa, salati ta somayi kuma idonta yanzu yayi ras saboda barcin ya tafi. A hankali ta dafa gado tareda mikewa tsaye, amma sai me? Kafa yace tsaya mugani mana..... Ashe ta turguɗe ne.
#NiDaDiYata
*All Rights Reserved*
Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top