Seven
Abdullah It was narrated that 'Abdullah said: "The Messenger of Allah said to us: 'O young men, whoever among you can afford it, let him get married, for it is more effective in lowering the gaze and guarding chastity, and whoever cannot then he should fast, for it will be a restraint (wija') for him.'"
********************
Sheshek’ar kukanta da sukaji ya dawo dasu hayacinsu, Abba ne ya matsa dab da ita ya fara magana kasa kasa, “kiyi hakuri diyata, insha Allah sai anbin miki hakkinki, nine mahaifinsa”
A hankali na daga ido na kalle dattijon dake magana, kammanninsu ɗaya babu bambanci. Bance komai ba illa rage sautin kukana ina Jan magina a hankali.
Alhaji Sulaiman (mahaifin Sadeeq) wanda yayi shiru kamar wanda ruwa yaci, a sanyaye yaje wajen tubur dinsu inda suka bar Alhaji Musa, shi dama baisan abinda ya faru ba sanadiyar yana waje yana waya.
“Ranka ya daɗe dama wani ɗan matsala ta taso” shikuma Alhaji Musa yace, “Injin dai lafiya?” tare suka koma inda su Naufal suke. Gaban Egnr faɗuwa yayi daya lura da Fuskarshi yayi kama dana Fadeela. Nan kowa yayi tsuru tsuru ana inda inda.
A gurguje mahaifin Sadeeq yayi mashi bayanin abinda ya faru, shiru yayi kafin yace, “Yarinya tashi ki faɗa sunan ki dana gidan ku?” ita kuma Fadeela tana daga ido ta ganshi saita barke da sabon kuka kai zaka zata locacin ake marinta.
“Big Daddy kasheni yakeso yayi wallahi” ta faɗa cikin sigar kuka.
“yi min shiru please, ni shiririta ne bana so” ya fada mata. Tsit tayi bata kara cewa komai ba,
“Ai abin yazo da sauki tunda na gida ne kuma ba matsala sai mu tafi gidan Grand Kadi, though ni banga abin tashin hankali anan ba, tayi rashin kunya kuma ya hukunta ta”
“ Ah ah gwara aje ayi abu cikin mutunci”, shi Abba abinda yasa ya nace su tafi a warware komai baifi akan iyayen Fadeela ba bcs yanzu sai a hana mutum sakat. Yanzu yanzu yaji tace kasheta akeso ayi.
Fadeela ta shiga motar Daddy babba(Alhaji Musa) shi kuma Abba da baban sadeeq suna mota daya, sai Naufal dake baya yana bin su. Yana tafe zuciyar shi yana mashi k’una, wai fisabilillah gidan Bad Luck zaije ya bada hakuri, tun dayake bai taba jiba.
Daddy babba yana tuk’i murna fal a zuciyarshi, shi kaɗai yasan dalilin haka. Sun isa gidansu Fadeela wanda ke GRA, katon gidan wanda komai akwai. Daga su Garden, swimming pool da kuma karamin basket ball court wanda yake da double function as tennis saboda Grand Kadi yana san motsa jiki.
Daga Naufal, baban Sadeeq da kuma Abba saida suka jinjina tsarin gidan, sum sum suka bi bayan Alhaji Sani. Ita kuma Fadeela tun kafin mai gadi ya buɗe kofa ta fito daga cikin mota tabi k’aramin gate ta shiga “Ho sarkin shagwaba” Daddy babba ya faɗa.
Bata iske kowa a falo ba sai motsi dataji a kitchen, da sauri ta haye upstairs kafin a risketa a fara mata tambaya. Su kuma su Naufal da Abbanshi sannu a hankali suka rinka bin Daddy babba har cikin Main parlour. Suna isa ciki sunyi Sallama sau wajen uku saiga Mommy ta fito tana gyara zaman gyalenta tareda amsawa.
“Abbansu Fadeela Kaine tafe?” ta fada fuskanta dauke da fara’a. Shi kuma ya murmusa sai yace, “Eh nine Hajia, kuma tafe da manyan baki nake” sai a lokacin ta mayar da hankalinta wajen su Naufal, fuskanta a sake tace masu sannu da zuwa. Wucewa tayi kitchen ta jero abinci akan tray saita kawo masu suci. “Bismillah mana” Daddy babba ya faɗa, su kuma Naufal mutuwar zaune sukayi saboda sun tuna idan mutum zai cuce ka saiya bari kun sake kafin ya ɗana maka tarko.
Upstairs mommy ta wuce domin ta kira Daddy, basuyi minti 5 ba sai gashi sun dawo tare. Zama yayi akayi gaisuwan mutunci, shi dai Daddy babba baice komai ba, gabzan abinci ya rinka yi yana santi tareda jinjina ma girkin mommy tunda ta iya sosai a matsayin ta na professional Chef. Daga bisani yace, “Ai tare muke da Diyata” Grand Kadi(Alkalin Alkalai) ne yace, “wanne daga ciki?”
“Auta nake nufi, sarkin shagwaba” yana kaiwa nan ya fara dariya. “Ban masan ta dawo daga bikin ba” Mommy ta fada. Shi dai Big Daddy saida ya cika Gizzard dinshi kafin yayi gyaran murya, gaban Naufal ne yayi mummuna faduwa. Dama tun yau abinda yake samu kenan but na yanzu ya ninka sau dubu.
Gyara babban rigarsa yayi, falo yayi tsit kowa naso yaji mai zai faɗa, “Da Alheri nazo” murmushi yayi wanda shi kadai yasan ma’ana shi, kowa kawai kallonsa yakeyi. Naufal duk ya k’agu yaji mai zai faɗa, “Dama batun auren ɗiyata ne da mijinta gashi kuna kallon shi” ba su Daddy ba har Abban Naufal saida suka mayar da idonsu kanshi.
Shi kuma zare ido yayi yana nuna kansa da ɗan yatsa, da kyar ya iya bude baki yace, “Da ni kuma?” kwarai da gaske, kai muke nufi Alhaji Sulaiman ya chapke. Shi dai Alhaji Hussain baice komai ba, ya bar ma Allah komai. Idan auren zai zame mashi rufin asiri ba’a tozarta shiba to gwara ayi.
“Yanzu dama akwai wanda aka ajiye ma Fadeela ta aura amma shine ba’a sanar dani ba? Kun kyauta min kenan? NI DA DIYATA amma sai ayi abu ba’a shawarce niba. Idanun Mommy fal da hawaye take magana cikin k’aramin murya.
Grand Kadi zaiyi magana sai Big Daddy yace, “bazan canza magana taba, dole ayi bikin nan. Badun ina san Fadeela ba da nasa ayi bikin nanda 6 weeks but zan k’ara mata wani 6 weeks din kunga ya kasance 3 months kenan sai ayi proper gaisuwan iyaye da kuma biyan sadaki”
Shi dai Naufal tunda yake bai taba ganin something that is absurd ba Kamar yau, “ya mare yarinya, maimakon a hukunta shi sai aka bashi ita a matsayin mata. Bai taba ganin inda aka ɓare gyaɗa aka tsinci mota ba.
Daga alamu sun gaji da annoban data ke jawo masu ne shi ne ake so a mak’ala mashi, amma bazai yiwu asha fate ranar sallah ba” Ranshi a bace ya ɗaga green eyes dinshi wanda idan ranshi ya baci yana glimmering, zaiyi magana sai ga Fadeela ta fito tana kuka.
A kasa ta zauna gefen Daddy tana facing Big Daddy, muryanta k’asa k’asa ta soma magana, sai kayi da kyar kafin kaji abinda take faɗi. “Please alfarma nake nema gurin ku, kunsan cewa tun dana ke ban taɓa saɓa maku ba?
Ina kokarin fulfilling all righteousness a matsayina na yarinyar ku. Banida kamar ku a fadin duniya, dama daga Allah, Manzaninsa tareda sahabbai kune next danake bi.” Gyara zamanta tayi tare da durk’usawa, hannunta biyu a harɗe saita sunkuyar da kanta k’asa, “please kada kuce na aure……”
Tas…. Mommy ta dauketa da wawan mari, “halan nan gurin sa’anki ne ke zaune? don raini ina kokarin k’wato maki hakkin ki shine zaki watsa min k’asa a ido wai ga zance ga magana, dan ace nike sangartar dake”
Ya isa haka Hajia, “ai gwara ta faɗi ra’ayinta amma bazai canza komai ba saboda sai anyi” Big Daddy ya chapke. Ita kuma Mommy ranta ya baci saboda da Fadeela bata fito ba data san yanda zatayi ta ruguza abin, amma yanzu tana cewa kule za’a ce sun haɗa baki ne. Amma tabbas yau saita shiga jikinta da duka, tunda ta ruguza mata plan dinta bcs of her stupidity.
Fadeela tana Sheshek’ar kuka ta koma ɗakinta, shi kuma suka mayar da idan su kan shi, wanda baka ganin komai sai green eyes kawai, “Kanada ja ne?” Alhaji Sulaiman ya faɗa. “Gaskiya kuyi min afuwa, ni inada wanda zan aura kuma alamomin munafiki ne idan yayi alkawari ya saɓa” Mallam rufe mana baki, Abba yayi magana a karo na farko tun bayan sun gaisa.
“Nifa bazan aureta ba” ya fada tareda mikewa, kallonsa kowa keyi “Grand Kadi kayi hakuri akan abinda nayi ma yarka which nasan Baka sani ba, but bazan aureta ba saboda wasu dalili nawa”
wucewa yayi ya nufe hanyar kofa, “Naufal karka bar gidan nan batare da na baka izini ba” Abba ya faɗa mashi amma yayi kunnen uwar shegu yayi ficewarsa. Yana tafe yana haki, “wai Bad luck za’a haɗa ni da ita! Ta kashe ni kenan da bak’in jininta. Sam Sam bazai yiwu ba” yana tafe yana faɗa ma kansa har ya kai wajen motarsa.
Haka ya fito daga cikin gidan su Fadeela sai yayi shawara yaje gurin Mamansa ya shawo kanta ta mara masa baya dukda tana fushi dashi akan yawan zuwa wajen Anty Saudah tareda daukar ɗawainiyan Miemie.
Ya hau babban titi yana tsugaga gudu baji ba gani, kuuuu yayi kokarin taka birki yayin daya lura da ɗan ga ruwa yana tura amalanken sa. left Naufal yayi kokarin zuwa cikin tashin hankali tareda rankamo salati but ashe masu Fruits da kuma balangu suna wajen wanda shi baima lura dasu ba. Saisaita steering dinsa yayi a firgice but sai da yayi Karon rago dasu. Nan take ya sume sanadiyar buga kanshi daya yi.....
Su kuma mutanen wajen salati suka rinka jerowa, daɗin abin kowa ya kauce. Gaggawa aka je bashi, anata dambe da mota da kyar aka fito dashi. Tun sanda aka fara cincibarsa ya farka amma baice komai ba saida aka ajiye shi.
A hankali ya ware idonsa ya rinka kallon wanda suka ceceshi. “Ina fatan babu wanda yaji ciwo?”
“Alhamdulillah babu kowa ya kauce” wani dattijo ya amsa shi.
“Amma Mallam kai ɗan rainin wayo ne, dan wulakanci zaka hau titi kayi ta zura gudu kamar na ubanka” Wani matashi ya faɗa
“Toh wallahi ba zanyi asara ba, ko a bayani kuɗin Fruits ɗina kona tada zaune tsaye yanzu yanzu” ya faɗa yana zaro ido tareda lakwansa baki.
Shiru Naufal yayi saboda yasan duk me ya faru dashi laifin shi ne, iyaye ba abin wasa bane. Bazai disrespecting dinsu hankali kwance ba. Gaskiyar Mallam Bahaushe ne daya ce “Rashin bin maganar iyaye hatsari ne” gashi abin ya zama mai hatsari physically ba a baki kawai ba.
Su kuma su Abban Naufal shiru sukayi kunya sai ɗawainiya dasu takeyi. Mommy ce tace, “naji yayi maganar wani abu ya faru, halan lafiya?” Nan Abban Naufal da kanshi ya labarta masu daki daki abinda ya faru.
Mommy shiru tayi kada ta tozarta Daddy ace matarsa batada kintsi yasa bata k’ara cewa komai ba. Amma bazata yarda ayi auren nan ba, bata taɓa jin inda aka ɓare gyaɗa aka tsinci mota ba.
Su Engr bada hakuri suka kara yi kuma fuskar Grand Kadi a sake. Shi kuma Alhaji Musa yace hakuri ɗaya zaiyi idan aka sa Naufal yayi auren nan. “Kar ka damu, nima auren nake so yayi tuntuni amma yaki. Aiko gawarsa ne sai an daura” Engr ya jaddada.
Grand Kadi har mota ya rakasu ana raha. Shi dai bashida abin cewa, duk abinda Big Daddy yace shi za’ayi. Saboda matsayin shi yafi karfin haka a wajen shi, yayi mai hallaci sosai a baya saboda haka bazai watsa mashi k’asa a ido ba. Ita kuma Mommy idanta ya cika fal da hawaye, kullum addu’a take Allah ya ba Fadeela miji mai tausayinta amma gashi za’a haɗata da wannan gwaskar.
Haka Naufal ya wuce wajen motarshi domin ya dauko masu kudi. Dama yayi withdrawing kuɗin dazai lik’i ne. Dubu goma sha biyar yaba mai Fruits su rage asara, sai yaba mai nama dubu goma. Shi kuma mai ga ruwa aka bashi dubu ɗaya da ɗari biyar, sauran mutanen wajen su uku ya basu dubu ɗaya ɗaya.
Haka ya koma motarshi datayi damaging, glass sun farfashe handle din kofa ya lankwashe. Komai dai babu kyan gani, ya shiga ya fara tuk’awa sai motar tanata hayaki tareda k’ara kamar Vespa. Tafiya yakeyi kamar bayayi saboda bashida maraba da kunkuru. Kowa kallonsa yakeyi yana kwafa bcs duk ya ishesu.
Abban Naufal ya kira Anty Saudah a waya yaji ko Naufal na wajenta amma tace rabonta dashi tun kafin yaje dinner. Abba ya rasa a inda Naufal ya koya mugun ɗabi’a amma ya dauki alwashin anyi na farko anyi na karshe. Zuwa gida yayi ya wuce bayi kai tsaye yayi wanka, daya fito saiya saka wani Ash jallabiya haka.
Daukar jaridar Daily Trust yayi ya wuce Varenda yana jiran shigowar Naufal, zama yayi a kujerun wajen saiya ɗaura kafa ɗaya kan ɗaya. Baya ma gane jaridar kawai k’afarshi yana karkarwa.
Sannu a hankali Naufal ya rinka gungura motarsa har gidansu, k’aran ɓararan motan ya sanar dakowa gashi nan zuwa, ga kuma hayaki kamar ana gobara. Yana zuwa mai gadi saida ya leka ta karamin gate yaga waye kafin yagane Naufal ne.
Shikuma Naufal tunanin shi ɗaya yazai yi da annoban ta, wai ace daga zuwa gidansu har ya kusa mutuwa, ina ace inuwar su ɗaya.
Yana isa parking lot ya ajiye motarsa zai wuce BQ inda ɗakinsa yake. Sam baiyi tunanin zaiga kowa war haka daren nan.
“Mallam zo nan” Abba ya faɗa fuskarshi babu wasa. Sum sum Naufal yaje waje, tun yau abubuwa mara misaltuwa ke faruwa dashi, yanzu a gajiye yake yayi likis. Yana isa ya ɗuka kasa alamar girmamawa.
Abba baiyi wata wata ba ya wanka mashi mari kyawawa guda biyu. “Faɗa min daga inda kake ka shigo min gida cikin dare kamar ɓarawo?” kanshi duk’e baice komai ba, shiru kawai yayi yana tunanin irin marin da zai rinka dauke Fadeela dashi. Saboda aurenshi zai zamo mata bak’in canji a rayuwarta.
#NiDaDiyata
Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top