Fourteen
On the authority of Sahl bin Saad Al-Saedi, who said : A man came to the prophet and said: "O Messenger of Allah, direct me to an act which, if I do it, [will cause] Allah to love me and people to love me." He said: "Renounce the world and Allah will love you, and renounce what people possess and people will love you." A fine Hadith related by Ibn Majah and others with good chains of authorities
*********
Yanda yaga rana haka yaga dare, tsaye yake gaban agogon bango. Kallon kur yayi mashi yana kallon sauran awanni nawa a daura mashi aure da ‘Bad luck’ wanda shi bai taɓa kiranta da sunan taba.
Duk jijiyoyin fuskarshi ya mimik’e, idanunshi sunyi jazur daga bacin rai da kuma rashin barci.
“Wai tsakani da Allah a ina aka taɓa yima namiji auren dole?” ya faɗa da karfin gaske tareda naushin bango.
Hura iska ya rinka yi ta baki da hanci.
Rabon daya kwana a gidansu kwana huɗu kenan tun kafin zuwan ‘yan biki. Da akayi mashi magana saiya wayance wai bai so ya takura ma mutane ne.
Mama taji daɗin abin sosai saboda ya nuna yanada hangen nesa. Shi kuma abinda yasa ya bar gidan baifi rashin san yaga yanda ake shige da fice kuma daya ci karo da mutum zai iya sanya alheri a lamarin kuma abinda baya so kenan.
Baisan gaibu ba amma baya jin akwai alheri a tareda lamarin.
11:09am abinda ke rubuce akan agogo, “Saura awa uku a kaini makisa na”
Bayi ya shiga yayi wanka saboda ya mance rabon dasu haɗu da ruwa saboda tashin hankali, yana fitowa ya nema inda wayarsa na handset yake. “20 missed calls” ya gani.
Shiru yayi daya lura da wanda yayi Most Call ɗin. Abbanshi ne tareda Anty Saudah kuma indai abu daya jiɓance bukin ne toh basa raga mashi, yanzu yanzu sai suyi balangu da namanshi.
Shi abinda yafi bak’anta mashi rai bai wuce yanda Fadeela ta saka soyayya ɗinta a zukanta yan uwanshi. Wai tun ma kafin ta shiga kenan!
Mutum ɗaya ce ya lura bata san abin, watau Amatullah amma tana aure a Gombe balle su taru su musguna ma Fadeela.
Daga ɗayan ɓangaren Fadeela ta saka bala’i baza ayi mata kowane gyaran amare ba. Tun ana binta da lallami da ɗadin baki saida Mommy ta shiga jikinta da duka, farfasa mata jiki tayi sosai saboda hanger ta ciro a drawer ta rinka auna mata.
Hajia Rabi matar big Daddy ta shiga tsakaninSu, Mommy ta rinka sababi duk takaici ya isheta.
“Ke bahun ubanki, yar tselan uwa! ” mommy tayi ashar bata masan tayi ba.
Ita dai Fadeela kuka takeyi kamar ranta zai fita, wai akan Naufal aka taɓa lafiya jikinta. Abinka da farar mace duk ta kumbura tayi jazur, kana ganinta saita baka tausayi. Idanunta sunyi k’anana saboda kuka da rashin isharshen barci.
Ta hakura za ayi mata auren dole amma babu wanda zai mata wani gyaran jiki, ko kitso bata so kawai a kyale ta.
A daki Hajia Rabi ke mata nasiha akan rashin bin maganar iyaye amma abin baya shigan Fadeela, sai kawai tace mata, “Wannan rashin kunyan da fitsara da kikeyi halan wani yace ki kashe auren ki ne zai aure ki?”
Sai a locacin abin ya dake ta, Sam bata so tayi zawarta da wuri kuma ita batada wanda ke jiran ta. Nan take tayi ma kanta karatun ta natsu, bcs ga yanmata birjik a gari babu mazajen aure ita ta samu tana yanga.
Tun daga lokacin aka samu kanta, har kitso da kunshi ta yarda anyi mata. Da aka yi mata maganar tsimi da maganin mata sai kawai ta taɓe baki tareda kawar da fuska.
Nan aka kyaleta ba’a kuma takura mata ba. Ta ɗanyi fara’a sosai ba kamar jiya ba, Mommy itama taji daɗin yanda ta sauya tana harka cikin ‘yan uwanta.
Koda Mommy tayima Naufal magana ko yanada events ne dayake so Fadeela tayi attending, sai yace mata shi bazai yi komai ba. Amma kuma ya tambayeta idan akwai wani abu daga nasu ɓangaren, uku uku zuciyar shi ke bugawa saboda baiso wani abu ya haɗashi da ita.
Gaskiya bazai iya zama waje ɗaya da ita ba, ai saiya rasu!
Kaddara ta riga fata saboda Mommy tayi assuring dinshi suma ba zasuyi komai ba. Kuɗi sosai ya aika ma Fadeela wai kada tayi lacking saboda sha’anin biki.
Har cikin ran Mommy taji daɗin abin, ita kuma Fadeela da farko taso tak’i amfani da kuɗin amma sai ta tuna bahaushe yace ‘Raba mugu da makami ibada ne’ nan take ta soma fachaka tana spending anyhow.
2:30pm......
Hausawa sunce ranar wanka ba’a ɓoye cibi, an daura auren Naufal Hussain Beli tareda Amaryarsa Fadeela Abbas Bello akan sadaki naira na gugan naira har Dubu dari ɗaya.
Mutane daga kowane ɓangaren Bauchi har Nigeria baki ɗaya duk sun hallara. Kowa yazo ya tayasu murnar wannan haɗin tunda duk gidan mutunci ne aka haɗa.
Walima mai rai da lafiya akayi wajen ɗaurin auren, kowa ya goge wuyansa da abinci yanda ya dace.
Suma daga cikin gida kawai shige da fice na abinci akeyi, kowa fuskarshi a washe kamar gonar auduga anata raha. Mommy ranta fari sol ta aurad da yarta. Ita Fadeela fuskantar babu yabo babu fallasa take abinta. Kowa ya yaba da yanda ta sake jiki tana komai.
Su Samɗa, Sadiya da Mansura sune kan gaba a k’awayenta. Dayake Sadiya taje Makeup school ita ta tsala ma Fadeela kwalliya mai rikitarwa. Tayi kyau sosai babu kama hannun yaro, ko Fadeela tayi mamakin yanda kimanin ta ya sauya farad daya.
Ta tabbata idan Naufal ya ganta sai zuciyar shi ya sosu ya rage tsanarta, dama itama saboda ya tsaneta shine take mayar mashi da martani.
Basai ta faɗa ba amma kowa yasan zaman doya da manja zasuyi dashi, ita kawai adduar daidaituwan tsakanin Su zatayi saboda Sam bata saba da faɗa ba kokuma a zauna a gida ɗaya ba’a ma mutum magana ba.
Tarbiyan da akayi masu shine bayan ka faɗa ma mutum laifin shi toh komai ya wuce an rufe babin amma ba wai ayita jan magana ana haɗuwa ana banka ma juna harara ba.
Shikuma Naufal ya saka wani dakarkiyar farin shadda wanda akayi mashi dinkin zaren hannu kuma babban rigane tareda yar ciki da wando. Farin hula da agogo duk ya haɗa dashi. Thou yana san saka fararen kaya but still Abba ya gargaɗe shi akan kada ya kuskura yazo wajen ɗaurin auren kamar rainbow.
Fara’ar dole ya rinka yi yana shan hannu dasu, ana sanya mashi alheri shikuma yana amsawa ciki ciki. Haka yayi tayi har taro ya watse.
8:30pm....
Kuka babu kama hannu yaro Fadeela keyi a yayin da ake mata nasiha. Duk ‘yanuwa an taru anyi mata nasiha mai tsuma rai. Mommy kasa cewa komai tayi tanata sharban kuka, fyace majina take da haɓan zaninta. Kowa tausaya masu yakeyi saboda an san yana yin shakuwan su. Duk inda akaga Fadeela zaaga Mommy, barci kawai ke rabasu kamar k’awaye.
Ajiyar zuciya Mommy tayi tareda gyaran murya “ Dan Allah idan ankai ki inaso ki nuna mashi cewa daga gidan mutunci kike. Yi nayi, bari na bari a koda yaushe”
“Ba yau aka fara karatun zaman aure ba, ke mai ilimi ce kuma kinsan right and wrong. Please show him how well trained you are, kada Kiyi abinda za’a ce waye mahaifiyar ki da batayi maki tarbiyya ba.”
“Kinsan cewa aure ibada ne kuma idan kikayi da kyau zai iya sanadin shigar ki aljanna, nima nan da kika ganni nawa ibadar nakeyi kuma bana fatan denawa sai ranar mutuwa na”
Haka Mommy tayi ta mata nasiha daga nan tace, “Duk abinda kikayi min wanda na sani da wanda bansani ba duk na yafe maki da fatan Allah Mahaliccin ya yafe mana baki daya.
A haka Fadeela ta faɗa jikin Mommy tana kuka wiwi kamar wanda za’a kai makisa. Dakyar aka rabasu, Anty Saudah da sauran yanuwan Naufal sunji tausayinta ainun saboda rabuwa da mahaifa bashida dadi.
Haka aka kaita gidanta wanda daga ita sai halinta da zai kwaceta. Anty Saudah ta sallami duk k’awayen amarya wai babu wanda zai kwana a gidan saboda dole ta fara neman aljannarta from the first day.
An sake fashe gidan dasu turaren wuta da room freshener komai sai san barka.
As expected, babu Naufal babu dalilinsa. Tun Fadeela na kallon wucewar agogo daga 11, 12pm, 1am. Hakura tayi taje tayi azkar ta rufe Ko’ina tareda kwantawa. Dan tsoro da kayanta na lace da alkyabba ta kwana bcs bata san stories that touch.
Shi kuma gogan jin kansa yayi kamar ɗan tasha, bayan su ABBA da Mama sunyi mashi nasiha mai shiga jiki, sumi sumi yayi kamar komai ya shige shi ashe banan gizo ke sak’a ba. Shi ya riga yayi planning ɗin zaman aurenshi.
Bayan isha’i sai yayi hanyar Club domin ya huce takaicin shi, ya ɗauki alwashin gwara ya kwana a club daya kwana gida ɗaya da Bad luck. Dayake baya shan Barasa ko wani kayan maye, VIP table ya kama aka kawo mashi fresh peppersoup na kifi ya fara bi takai.
Daga bisani aka kawo mashi zafafan tsire yana taci yana shan Smoove hankali kwance, shi dama idan yana matsakancin ɓacin rai to kawai yaci abinci komai zaizo mashi da sauki.
Bayan nan ya rinka kallon masu rawa kafin barci ɓarawo ya sace shi, “Abeg Oga wake up its 4:30 am and we want to close” Wata mai aiki a club ɗin da kayanta iya cinya take tadashi taga barci.
“Innalillahi wa inna ilayhi rajiun!” ya faɗa a tsorace tareda ja da baya saboda ta firgita shi da kamininta.
‘yan kunnaye wajen shida shak’e a kunnuwanta, ga kuma ta huda k’asan bakinta wajen gemunta kuma shima ta bishi da ɗan kunne round babba. Eye shadow ne blue ɗampare a idonta ga green jan baki ta mulka a baki, sai kuma gashin kanta ɗan guntu, shiba dreadlocks ba.... Wani k’azamin abu haka babu fasali.
Tsaki yayi, “Amma dai bariki bai yiba Wallahi!” ya wuce motarshi. Wani waje chan nesa da gidan shi yayi parking motarsa, baya ya koma ya hau barci, da kyar wajen 6:30am ya samu yayi sallah a wani masjid saiya koma barci.
7:45am....
Locacin ne aka kawo ma Fadeela abinci, Abla aka tura tareda Miemie. Ba k’aramin jin daɗin ganin Fadeela Miemie tayiba, kuma wai ance idan sun huta da buki zata koma wajen su da zama.
Itama Fadeela taso Miemie, nan take Sister’s ɗin Naufal suka burgeta. Bata barsu suka tafi ba saida ta basu kyautar underskirt, vest, eye shadow, body spray tareda lipstick.
Bayan tafiyar su tayi wanka tareda fesu kwalliyar kamar zata buki, duk wani kusurwa na gidan inda akwai switch sai ta saka burner ɗin turaren wuta, kafin 10mins gidan ya gane Amaryar ba kuchaka bace.
Abba ne ya shigo cikin falon yanata sallama tareda Alhaji Sulaiman, Shi kuma Naufal bai shiga da motarsa cikin gidan ba, yazo ne kawai a gurguje don ya canza kaya saiya ware. Baima lura da motarsu a parking lot ba hankalin shi yana abinda ya kawo shi.
Fadeela ta sauko daga upstairs kuma idonta ya kumbura saboda kukan data kwana tana yi, saiga Naufal ya shigo cikin falon tareda turesu Abba saboda labule ya ɓoye su.
Charko Charko Naufal yayi saboda ga babban rigar shi a hannu duk ta chukurkuɗe kamar ya fito daga bakin kada sannan yasan meAbba yace akan aurenshi da Fadeela.
Tsuru tsuru yayi yana adduar daya dace da wanda bai dace ba. Abba ne ya kalle Fadeela saiya kalle Naufal kafin yace, “Daga ina kake?”
#NiDaDiyata
*All Rights Reserved*
Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top