Eighteen

On the authority of Abu Hurairah, who said : The messenger of Allah said : "Part of someone's being a good Muslim is his leaving alone that which does not concern him." fine Hadith narrated by Termithi and others.

On the authority of Abu Dhar Jundub bin Junadah, and Muadh bin Jabal that the messenger of Allah said : "Fear Allah wherever you are, and follow up a bad deed with a good one and it will wipe it out, and behave well towards people." Tirmithi narrated the Hadith and said it was fine, and in another version, said ture and fine.

*******

K’ara kokarin daura kafar tayi a kasa amma ta kasa. Wani azabataccen zafi taji har cikin birnin kwakwalwarta.
Nan take zafafan hawaye suka fara  malalo mata. Changala kafarta tayi har cikin bayi ta kunna mashi ruwan zafi but still babu wani improvement.

Haka ta koma cikin ɗaki ta hau kan gado tana tunanin duk yanda zata rinka ma ‘Other half’ ɗinta hidima. Bata gano answer ɗinba har barci ya fara fizgarta, gashi bata kashe wuta ba amma bazata iya tashi ba saboda azaba.

Shikuma Other Half ɗin Fadeela Kawai tunanin abinda ya faru tsakanin shida ita Few minutes ago yake.
‘Kardai ace yarinyar nan ta fara sona ne?’ wani zuciya ya raya masa.
‘No no no... Allah ya kiyaye, it’s not even possible. Haba duk wulakanci danake mata!’ wani zuciyar ta sake raya mashi.
‘Maybe kuma kuɗi takeso’
‘Yes I’m very sure, dama mata idan suna san kuɗinka sai su ta maka iyayi’
Yayi concluding Kudi takeso sai yayi tunanin ajiye mata check ɗin 50k kafin ta takura masa.
Haka ya gama kallonsa saiya kashe kayan kallon tareda lantarki sanda zai tafi.


3 days....

Ciwon Fadeela sai gaba yakeyi saboda ko Makaranta ta daina zuwa. Dakyar take komai gashi ko kauɗin girki kala kala ta daina, dayake tanada stew dayawa a fridge sai ta rinka dafa white rice or Macaroni ta ajiye mashi.

Drink kuma saita ajiye mashi Fanta ko Pepsi kawai, idan kuma breakfast ne Tea and bread Zata ajiye.
Kuma rabon daya ganta tun ranar data turguɗe.

‘Dingisa kafarta from upstairs to downstairs and vice versa Yana bata wahala saboda tana tafe tana kwalla gashi ya kumbura sintim kamar Doya.

Shikuma Other Half abin ya fara damunsa, ya lura check ɗin daya ajiye bata ɗauka ba kuma next day yayi withdrawing cash ya ajiye mata amma bata bi takai ba. Ya rasa menene matsalar ta gashi ko abinci anyhow takeyi.

Kuma rabon daya ganta tun sanda tayi wani hot kwalliya. Shi Bawai Santa yake ba but atleast.... Sai kawai ya kasa Karasa tunanin.

Zama yayi a falo daga safe har wajen azahar yaki zuwa aiki yana son yaga kozata wulkita amma Sam. Kwafa yayi saiya dauki key ɗin motarsa ya tafi gidansu, gwara yaje yaga Miemie yafi kafin Bad luck ɗinta ya jaza mai!
À wajen Miemie babu yabo babu fallasa tanata fara’a kuma sunsha hira. “ina Anty yar gayu?” ta tambaya. Dadi sosai ya kamashi saboda an taɓo mashi inda yake mai k’aik’ayi.

“Ban sani ba amma bari na ara wayar Momyn ki sai mu kirata. Zulumi a ranshi yana tunanin mai zai ce ma Anty Saudah bcs kwata kwata bayada number ɗinta.
Aiko wayar ya gani akan centre table kuma Anty Saudah tana kitchen, a guje ya sure wayar yana jin ɗadi. Bugu ɗaya, biyu sai ta dauka.

“Assalamu Alaikum, Anty ina wuni?” ta faɗa. Shi kuma yana jin muryanta sai ya kauda da sauri tareda kara ma Miemie a kunnenta.
“Anty yar gayu yaushe zaki zo?”
“Ah ah Miemie Kece ?”
“Eh please yaushe zaki zo?”
“Gaskiya ban sani ba saboda banida lafiya”

Kallon Naufal Miemie tayi tareda faɗin “Ya Naufal dama Anty batada lafiya shine baka faɗa min ba?”
Tsuru tsuru yayi saboda baiso Fadeela taji yana wajen ba, harara ya watsa ma Miemie tareda juyar da kansa.

“Anty kiyi hakuri kinsan halinsu koda nace zanzo dubaki bazasu barni ba” ta cigaba da wayarta. Hira sosai sukayi daga bisani aka kashe.

Burin Naufal ya cika yasan meke faruwa but still baisan meke damunta in particular ba. Anty Saudah tazo tana tambayar Naufal koyaga wayanta data ajiye a falo.

“Eh dama nine na dauka saboda Miemie tanaso tayi waya da Anty ɗinta”
“bakada wayane? Innalillahi kodai bakada number ɗinta ne?”
Kana ganin yanda yayi kasan cewa bashida gaskiya, kallonsa Anty Saudah tayi kafin tace, “Allah zai saka mata koma menene”

Anan ta barshi tsuru tsuru ta koma ɗaki saboda haushin takeji ainun, ita tasan basa jituwa amma batayi tunanin haka bane.
Baiji daɗin yanda ran Anty Saudah ya ɓaci ba, kawai saiya yanke shawara ya bita ya bata hakuri tunda a matsayin uwa ya ɗauketa ba step mom ba, Thou bazata haife shiba.
A bakin gado ya ganta tana matse kwalla, kakalo murmushi tayi data ganshi. Yasan sarai shi takema kuka.

A kasa ya zauna dab da ita saiya daura hannunsa akan cinyarta. Nadama karara saiya soma magana kasa kasa.
“Dan Allah Anty kiyi hakuri, Karki min haka, bana so kiyi kuka a kaina. Insha Allah I will do better.”
“Allah yasa” kawai ta iya faɗa bcs zata iya barkewa da kuka wiwi.
Sallama yayi mata kuma tashi mai da albarka saiya koma wajen Miemie sukayi sallama sannan ya tafi.

A hanya tunani kawai yakeyi bcs ya ɗebo ruwan dafa kansa tunda yayi ma Anty Saudah alkawari amma baya tunanin zai cika mata ba.

*****

Ita kuma tana jin tashin motarsa saita ɗingisa kafarta har kitchen, Feldin ɗinta ya kare saura Paracetamol gashi tana shan wuya.

Abinda yasa take gudun Naufal baifi sanin halinshi na mugunta data yiba, tabbas muddin yaga tana pain zai kara inflicting mata more bcs burinsa kenan yaganta ta su suce.

Nan take ta yanke shawara akan tayi Cous Cous saboda  it’s very easy.
Ta gama saita je dauko Fanta a fridge amma to her surprise ya kare. Dama tasan ya kusa gashi bazata iya zuwa kasuwa ba. Ruwa na sachet ta ajiye mashi kawai saita koma ɗaki.

Zaman ɗirshan tayi a kasa tana numfashi sama sama, fisge ɗankwalin kanta tayi ta jefar. Ji tayi kamar ana tsikarinta a kafan gashi yayi nauyin. Ko numfashi ta lura yana kara mata zafi.

Dukta fita hayacinta ta rasa meke mata daɗi, kwalla kawai takeyi gashi bata iya cin abinci sai shayi. “Wayyo ni Fadeela na shiga uku!”

Shi kuma yana shiga falo ya lura har tayi abinci, kwafa yayi a ranshi tareda faɗin “ke kika sani”

Haka yaci abincin kamar maɗaci saboda ya kwaɓe. Daya gama saiya kora ruwa yayi ɗakinsa, daya kai kofar Fadeela saida yaɗan tsaya koh zaiji motsi amma shiru kawai.

8:30 pm...

Yaune nake ina tunani tareda kallon TV, ko ganewa banayi saboda tunanin yarinyar chan nakeyi, “karfa ta mutu” na faɗa da sauri tareda mikewa saboda nasan Abba zaiyi balangu dani muddin haka ya faru.

A hankali na haye sama saboda banso taji karar zuwana. Safa da Marwa na rinka yi wajen ɗakinta na kasa shiga. Ni dai ban iya amai ba na lashe, Sam idan na shiga zata iya raina ni.

Shiru nayi na rasa TUDUN DAFAWA(littafin my awesome UmmieeJafar) Kawai  na yanke shawara na shiga tareda zare mata ido kamar mugu. Idea ɗin yayi min daɗi bcs haka nayi.

Banka kofa nayi da k’arfin gaske tareda shiga, ina jin ta yanda tayi salati a razane. Ta bani tausayi ainun amma no time for weakness yanzu.

“Ke dan raini zaki dafa min wani abinci babu kyan gani? Waye sa’anki?” sanda na faɗa ina jin ciwo a raina but a haka na cigaba.

Narai narai tayi da ido tana kuka batace komai ba, jan magina kawai takeyi. Tausayinta ya kamani sosai saboda nasan tana kokari but it’s not enough bcs Itace dai Bad luck.

Bance mata komai ba kawai na tsaya ina kollonta, data lura ita nake jira ta bani amsa saita fara share hawayenta, “Kayi hakuri Yaya wlh bada gangan nayi ba, banida lafia ne” ta faɗa cikin muryan kuka.

“But Bari naje na dafa maka wani” saita fara Kokarin tashi. Duk rashin imaninka saika sosu. A hankali nace, “Dont worry” saina fita daga ɗakin, nawa na koma saina zauna akan gado.

Hannaye biyu na daura akan kumatu na ina tunani, gaskiya ya kamata na taimaka mata koba dan halinta ba sai dan Allah. Ban koma cikin ɗakin ba but haka na rinka zirya wajen, idan naje sai na saka kunne na akan kofarta.

Kukanta nakeji a hankali yana tashi. Gabaki daya ranar dagani har ita bamuyi barci ba. Sau biyu ko uku a cikin awa daya ina bakin ɗakin, sai wajen asuba naji tayi shiru da alamun barci tayi.

Ban kwanta ba illa nafila danayi, na rok’on ma Miemie lafiya tareda ita bcs dey need it.

7:30am...

Ta fito tana ɗingisa kafa which sai a locacin na lura da mai ke damunta, dukta kumbura ta susuce. Ji nayi kamar naje na daukota tsam daga stairs bcs ta dade bata sauko ba balle dama akwaita da nawa.

Sannu a hankali harta isa inda nake, “Ina kwana yaya?” ta faɗa murya kasa kasa.
“Lafia lau, ya jikinki?” ashe na sosa mata inda yake mata k’aik’ayi. Nan take ta barke sosai da kuka babu kama hannun yaro. Tanayi tana Sheshek’ar, bata tafi illa tsayawa a wajen.

A hankali na karasa wajen datake, har zan saka hannuna nayi patting bayanta saina fasa kafin ya zama wani abu.

“Kinaso akaiki asibiti ne?”
Bata amsani ba kuma nima naji haushin tambayan bcs yanda take tana ɓukatar medical attention. Key ɗin mota ɗina na zura saidai kash.........
Bazan iya bari ta fita haka ba, wani armless chiffon gown ta saka kuma bazan yarda wani Katon banza ya ganta ba, thou bawai ina Santa bane, but still!

“Bakida wani kaya dazaki haɗa da wannan kinsan akwai maza a wajen?”

Kallon kanta tayi saita sinna kai kafin tace, “bari naje na dauko abaya ɗina”
Juyawa tayi ta fara tafiya, idan na biye mata zamu kwana a wajen.

“just wait! Yana Ina ne idan na biye maki zaki ɓata min lokaci”
Kallona tayi kafin tace, “Cikin drawer ɗina third shelf” Haka naje na dauko mata na bata abinta. Tana ɗingishi kamar raina zai fita saboda ni ko ban san mutum banaso naga ciwonsa .

Wani private mukaje nan kusa damu, cikin sa’a Doctor yana nan. Tambayoyi ya rinka watso min wanda na kasa amsawa, wani irin kallo yayi min wanda kaida matarka amma bakasan komai a kanta ba.

Kunyar duniya naji shi ranar saboda mutumin yana mutuntani sosai saboda unguwar mu ɗaya but daga alamu ya daina.
Fadeela ne ta rinka shigan min tana amsawa, gaskiya yarinyar is very smart Kuma nagode mata cikin raina.
Anzo za’a ja mata k’afa shi kuma Naufal zai fita kawai ta chapke masa hannu ”please stay with me Yaya, Karka tafi ka barni. Im very scared”
Ta faɗa da puppy face idonta yana kwalla.

 

#NiDaDiYata



   *All Rights Reserved*

Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top