Chapter 9



20 minutes ne ya karasa da yasmin c'est bon cafe wanda hakan yai dai-dai da 4pm,kallon mirror din motan tayi a hankali ta gyara murya tace hey i,m yasmin hayat,,,saurin girgiza kai tayi tace ba haka ya kamata nace ba sannan tai murmushi tace hey i,m yasmin hayat tsaki tayi tace no ba haka ya kamata nayiba saboda aunty rahma tace rayuwar turawa yakeyi kamata yayi na mika mishi hannu mu gaisa sannan nace hey i,m yasmin hayat,,,,muryan driver ne ya katse mata acting din da takeyi yace yasmin munxo inda hajiya tace na kawoki,wani irin takaicine ya kama yasmin jin driver ya ambaci sunanta kai tsaye ba tare da ya bata wani girmaba,a zafafe ta kalleshi tace daga rana irinta yau karka sake kirana da yasmin kai tsaye ba tare da wani respect ba,ko baka da labarin na zama yar shugaban kasa?bata jira ya bata answer ba ta fita daga motar tana tattare gown din jikinta sannan ta sake kallonsa tace ka jirani nan da 1 hour zan fito mu tafi.....jikinsa sanyaye yake bin yasmin da kallo shi dai a iya saninsa tabbas yasmin din daya sanice yar gidan malam jauro me bawa shukokin gidan ruwa sannan mahaifiyarta me aikice a gidan toh abin mamaki kuma yau yar president da kanta ce ta rako yasmin har bakin mota?tagumi yayi yace lallai wannan alamari akwai wata a kasa

"Kasancewar wannan ne karo na farko da yasmin ta fara shiga restaurant,cafe ko wani joint haka yasa gabanta faduwa,tunda ta shigo ya kasa sauke idonsa daga kanta wannan shine karo na farko da armaan ya taba zubawa yarinya ido kamar wanda yaga sarauniyar kyawawa,shigowar text message ne ya sata saurin bude message din "i'm sorry dear,,we can't meet today till tomorrow"shine abinda ke rubuce jikin message din,wani gumi ne ya karyowa yasmin duk da kasancewarta yar talakawa amma ta tsani disappointing(haha i hate it too)sosai bacin rai ya bayyana a fuskar yasmin lallai ma wannan mutumin ya cika dan rainin hankali meyasa tuntuni be fadamin bazai samu damar zuwaba sai yanzu karfe 4,a fusace ta mike daga kujerar da take zaune zata fita daga gurin,kamshin hadadden turarensa ne ya shiga hancinta jin mutum tsaye gabanta ya sata saurin daga kanta ta kalleshi,murmushi yayi kadan wanda ya bawa dimple dinsa damar lomawa yace hey miss beauty,tunowa tai da maganar da rahma ta fada mata cewa armaan rayuwarsa ta turawa ce ya sata saurin mikawa armaan hannu kamar yanda ake shaking tace hey fuskarta dauke da murmushi,sedai abinda ya bawa yasmin mamaki ganin armaan be mika mata hannu ba sedai kawai murmushi yayi a karo na 2 yace have a seat,cike da kunya yasmin ta zauna akan seat din da armaan yayi mata pointing ta zauna zuciyarta cike da tunanin yarfin da armaan yayi mata menene ya hanashi miko mata hannu su gaisa kamar yanda ta mika masa

"Coffee aka kawo musu da cookies ba tare da sunyi order ba,bayan armaan yayi sipping coffee din kadan ya dago kyawawan eyes dinsa yace I'm sorry for the surprising nasan ba kowa ne yakeson suprise ba,murmushi tayi kadan tace it's okay,sun danyi hira kadan sedai abinda ya bawa yasmin mamaki shine ganin yanda ake fasalta armaan matsayin playboy kuma cheater duk bata ga wannan alamun a tare dashi ba sai dai akasin haka,saurin kawar da wannan tunanin tayi tace toh banda abuna aishi dama mara gaskiya baya bayyana kansa sannan suma wanda ya yaudara din ai a matsayin mutumin arziki yaje musu,saurin kallon wrist watch din hannunta tayi taga it's 5pm,kallonsa tayi a takaice tace i have to go now,shima kallon agogon hannunsa yayi yace not bad as you wish sai yaushe kuma?murmushi tayi kadan tace after sometime,ajiyar zuciya yayi kadan yace tomorrow?daga kafadarta tayi alamar she don't care tace okay ta karasa maganar tana mikewa tsaye,,,,shima mikewa tsayen yayi yace okay i will pick you up tomorrow,wayarta ta dauka daga kan table din tace ok

"A tare suka fito bayan armaan ya biya kudin da aka musu bill sunyi exchanging number,sai da armaan ya ga tafiyar yasmin tukunna ya shiga mota zuciyarsa cike da tunanin yasmin,a gida ya tarar da mubarak cikin tsokana mubarak yace mr romeo how market?a gefen couch ya zauna fuskarsa cike da murmushi yace she's beautiful,a beautiful girl with an innocent smile and odd colored eyes that weren't supposed to hold a meaning behind them,I love her though i love her so much,I don't want to loose her,,,,,sosai mubarak yake dariya kamar ranshi zai fita sannan yace wait,wait asap karka manta dai wancan game din tuntuni an gama playing dinsa,tsaki armaan yayi yace look bro wlhy I'm serious kyakkyawace sosai,muryarta me dadi gata kyakkyawa babu abinda zai sake birgeka da ita sai idan tayi murmushi,shiru mubarak yayi yace amma wannan wacce yarinya ce haka daga haduwa da ita jiya harta sace maka zuciya sannan yar gidan waye?a ina gidansu yake?shiru armaan yayi kadan yace I really don't know amma am gonna pick her up tomorrow zan sameta a gida kafin mu fita,okay kawai mubarak yace sannan ya sake fashewa da dariya yana waqar beginning na joeboy

"A gajiye ta fito daga mota bayan driver yayi parking ta wuce apartment din rahma,a dinning area ta tarar da ita cike da murna rahma ta kalli yasmin bayan ta umarceta data zauna itama,gaba daya yanda sukai da armaan ta bata labari cikin farin ciki rahma tace good job dama nasan zaki iya,mikewa tai ta shiga dakinta bata dadeba ta dawo hannunta rike da rappers na kudi guda 5 ta ajiye gaban yasmin tace dauki wannan,zaro ido yasmin tayi tace aunty,,,shhhhhh!!!rahma ta fada tana dora finger dinta akan lips dinta tace jeki da wannan 500k ne kyautace kawayena su fadila suka ce na baki kafin na biyaki ladan aikinki da kikeyi,hannun yasmin na rawa ta dauki kudin ita kam gani take kamar anyi mata kyautar biliyoyin kudi ita kam ko haka aka barta kudin ladan aikinta ai ya isa,a bakin kofar da ze kaita apartment dinsu na masu aiki ta tsaya gabanta na matukar faduwa,ita yanzu ya zatayi da kudin nan?me zata cewa anna?tunowa tai da yanzu ta bar anna a main palour na first lady ya sata saurin nufar bangaren nasu ta dauki leda ta kulle kudin sannan ta daga kafitar kan gadon tasa don tasan babu wanda yake daga mata gado sau dayawa tana ajiya anan idan bataso anna ta gani

"bayan anna ta shigo ta tarar yasmin na sallar isha,seda ta jira ta iddar tukunna ta kira sunanta cike da tuhuma tace yasmin,jin yanda anna ta kira sunanta cike da tuhuma yasata saurin amsawa cikin kwarin gwiwa saboda kar anna ta gano halin da take ciki,dazu ina kikaje?murmushi yasmin tai tace lah anna kinsan na fada miki zanje gidansu mardy ai chanchaaan.....naje ta karasa magana cikin i,ina,ajiyar zuciya anna tayi tace gidansu mardy dinne har naga rahma ta rakaki bakin motar da babu wanda yake shiga daga shugaban kasa sai rahma?Sannan tasa driver ya kaiki?bayan kin dawo kuma kika wuce bangarenta bayan mintuna kadan kika fito hannunki rike da makudan kudi,,,,,wannan duk kina nufin daga gidansu mardy kike?gaban yasmin ne yai mummunar faduwa cikin tashin hankali ta sauke idonta akan na anna tabbas duk wanda yace zai munafinci iyayensa musamman mahaifiya toh lallai gaskiya sai tayi halinta,tunawa tai da anna macece mai fahimta tun tana karama take bata goyon baya a duk lamuran datasa gaba meyasa zata munafinci mahaifiyarta?jikinta sanyaye ta bayyanawa anna duk abinda yake faruwa sannan ta fito mata da kudin ta mika mata,a zafafe anna ta kalli yasmin tace karya kike wlhy yasmin ki zubar min da mutunci a duniya,tun kina karama nake shan wahalar ki don haka baki isa kin bata mana sunaba a duniya ya zama dole na mayarwa rahma kudinta sannan na ja mata kunne akan karta sake shiga rayuwarki tunda tana ganin don suna da karfin mulkine kuma muna karkashinsu muna aiki zata sanyaki ki lalata rayuwarki a banza toh a daren nan zamu bar musu tsinannen gidansu,ledar kudin ta dauka ranta a bace ta nufi bakin kofa tana huci,da sauri yasmin ta riko anna tana cewa don Allah anna kiyi hakuri wallahi baki fahimceni bane don Allah anna karkije,karkije.....a firgice ta farka daga mafarkin da takeyi gabanta na faduwa ta fara goge guminda yake zubo mata,,,,ganin anna zaune tana karatun kur,ani yasa yasmin kallonta cike da tuhuma,a tsorace anna tace lafiya yasmin kina bacci kika tashi haka a firgice,ajiyar zuciya yasmin tayi tace wlhy wani mugun mafarki nayi.....

Thank you for reading my story!!!

Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top