CHAPTER 21

DAN ALLAH KARKU MANTA DA FOLLOWING DINA SECOND BIYAR KACAL ZAI DAUKA.

Shiru parlourn yayi yayinda kowa ke nazari aransa,mom tana fata Allah yasa su yarda

Yayinda baba ke nazarin me Yan anguwa zasuce ai Dan abin duniya ya aurarta, Yayinda inna ke Mazarin anya minal zata iya zaman gidan miji kuwa?

Yayinda ya abubakar ke farinciki finally dirty sister dinshi ta samu miji nagarcacce Duba da mutuncin mahaifiyarsa kuma dai ruwa da kankara Abu daya ne samfuri ne kawai ya banbanta

Baba ne ya dago ya kalli mom kamin yace agaskiya hajiya.........

Minal koda ta fito hanyan gidansu zaliha tayi malam bala ne yayi saurin kunna mota tare dayi mata horn sannan ya zuge glass yace hajiya kihau nakaiki Inda zaki mana

Allah ya gani malam bala naaon yarinyan saboda babu ruwanta gashi batada girman kai irin na madam zakiyya

washe baki tayi kamin tace malam bala da ka barhi kawai

yace a ah dai kizo muje

shiru tayi tana Neman hujjan da zata bayar da taji medulla oblongata dinta bai harbo mata Ba kawai sai tahau baya

Owners kwana ta Shiga sai tayi wani das da ita kamar hajiyar gaske

Kwatanta mai ta fara yi.........

Zaliha's POV

Hm

Swthrt Wai me ya samekine duk kin canja min gashi na kosa na ganki amatsayin matata

Dagaske?

Eh dagaske nake, kina gida ne?

Eh ina gida Kasan tunda aminiyata ta bata jiya....hhhh....na dawo..daga....gid......

Sai kawai ta fashe da kuka

swthrt me kike Cewa kina nufin Amina jagwal ta bata?

Tace eh,yace
Kiyi hakuri ganinan zuwa kinji ki yi shiru kinsan kukanki yana tada min hankali.

Toh kawai tace kamin suka datse kiran taci gaba da kukanta

After 10 minutes

Karan mota zaliha taji a kofar gidansu ana horn
Mamaki take Dan Ba haka karan motan Suleiman yake Ba

To kodai yasai wani mota ne?
Hakadai ta dinga sake sake yayinda take saka hijabi da takalmi Dan yau Ba kwalliya aminiya ta bata

Kofar dakin iya taleka tace mata Suleiman yazo

Iya tace to tamai iso mana tace Toh sannan ta fita

MINAL kuwa tun ahanya take sake sake yanda zatayi surprising zally Suna isowa tace baba kayi mata horn Dan Allah

Yace toh yata sannan yayi horn Kamar bayan minti biyu saiga zaliha ta fito

Tsayawa tayi sakoko tana kallon motar kawai sai ta basar tahau waige waige tana Neman motan future hubby dinta da taga dai babu alamarsa kawai sai ta juya zata koma ciki tana mai yana kyau irin na motar

Daidai lokacin minal tace wa bala ya sauke mata window ta control din wajensa akwai Abu a hannunta

agaskiya dai babu Komai a hannuta tana tsoran kar yaje ta taba abinda Ba daidai bane ta lalatawa mutane mota wannen azzalumin oga sir din ya kasheta Dan bayida imani

(Kaji fa minal Wai bayida imani hmm Allah dai ya kyauta)

Yana saukewa kuwa tace "Yan mata ki mana" tana dariyan shekiyanci

Zaliha dai inba kuskure take Ba to lallai muryan minal taji may be depression na batan minal din yasan ta fara imagining things

Juyowa tayi aiki karaf suka hada ido murza idonta tayi yayinda bakinta ya budu mamaki da tambayoyi fal ranta

Da sauri ta karaso tana mai saka hannu domin taba fiskan minal Dan ta tabbatar da kokontonta
Aiko minal dince Ba gizo gizo Ba

Cikin dashasshiyar murya tace minal

Smiling minal tayi tana gyada kai

Zaliha tace Kece ?minal tace nice
Bude kofan motan tayi ta sauko kamin suka daka tsalle atare suka rungume juna suna ihu tare da juyi

Smiling kawai baba bala keyi

Nanfa minal ta juya tacewa baba bala zai iya tafiya

Yace hajiya kin tabbata Ba matsala? murmushi ta masa alaman eh kamin sukayi jikin gida aguje sai dakin iya bakinnan nasu har kunne

Aiko iya taji dadin ganinta sosai bayan ta mata jaje ne suka fito suka koma dakin zaliha

Zaliha tace kawas wayar dani, Wai yankan kai kika fara ne?ko sata?ko kidnapping?

Minal ta kyalkyale da dariya tace Kamar kinsan yanxu haka kanki nazo cira kuwa

Ai bashiri zaliha ta rufe kanta

Wannan karan minal dariya take harda buga cinya tace ke dallah wasa nikeyi matsoraciya

Zaliha tace anji ai tsoran ma da dalili nakeyi nidai yi mini bayanin yadda akayi kika samu mota irin wannan kuma harda driver

Minal tace "jiya........

Nan ta labarta mata abinda ya faru Kamar yadda mom ta tsara har izuwa yanzu zaliha ko sai gyada kai take Kamar kadangaruwa alamar gamsuwa

Minal ko taki fada mata Gaskiya ne saboda tasanta da karadi yanxu sai tayi subul da baka ta fada Ba tare da tasani Ba

Aiko hira suka kafa minal na bata labarin yadda gidan su yazeed din yake wani abin ma Zaliha sai tace "kai minal arage na tomorrow"
minal tayita rantsewa amma zaliha bata yadda ba

Wayan zalihanne yayi ringing ta Duba Suleiman ne dauka tayi yace mata ya iso tace to gatanan zuwa kamin suka fito ita da minal

Jingine yake ajikin motarsa kin 406 Yace lallai ma swthrt dama kawai so kike kiga fiskana shine kika wani cemin minal ta bata minal tace eh hakane na bata amma yanxu na dawo

nan zaliha ta labarta masa abinda ya faru yace Allah dai ya kiyaye na gaba tace Ameen

Hira suka ci gaba dayi abinsu sai wajen azahar tukunna minal tace zata tafi Suleiman yace bari ya rage mata hanya

🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
.........agaskiya hajiya Duba da irin mutunci da karamci da kika nuna mana dukda Cewa kin fimu arziki zamuso kuma zamuyi farin ciki ace Mun hada jini dake saide wani hanzari Ba gudu ita yarinyan bamusan ra'ayinta Ba

Dan! Dan!! Dan!!!

Gaban mom ne ya fara lugude lallai dakyar minal zata yarda da wannan batu Duba da irin abinda yazeed din ya mata saide ikon Allah

Tace to shikenan ga card dina duk shawaran da kukayi sai kusanar dani ko?sukace Insha Allah

Sannan ya Abubakar ya amsa card din

Yayi waje shida baba yayinda inna ta bisu da Karin kumallo sannan ta dawo ta sami mom bata fara Ciba

Tace hajiya kick mana mom tace aike make jira muci tare sannan ki dena ce min hajiya kicemin yar uwa

Toh kawai inna tace sannan ta zauna suka fara ci tana mai kara jin mom har cikin ranta

Wajajen azahar saiga minal ta Shigo alokacin mom ta Dade da tafiya

Baba da ya Abubakar ta gani zaune suna dan hiransu yayin da inna ke dafa abinci

Tsalle minal ta daka taje ta fada jikin sa
Baba yace yi ahankali kada ki karya Mani d'a

/\/\inal tace ai Nayi kewansa ne nan ta jona aka ci gaba da labari da ita can inna ta leko tace a ah har kin dawo kenan? Tace eh
Inna tace ya kika tadda kawar taki minal tace lahiyatta lau kawai de tayi kuka ne baba yace Allah sarki

Inna ce tayi ma baba Alama da ido Cewa ya fada mata

Gyara zama yayi yace AMINATU

Tace na'am baba yace ki saurareni da kyau sannan Kiyi tunani

Tace Toh

Yace nasama maki miji sunansa YAZEED........

Tofa fans kuna ganin minal zata amince da wannan batu?

Ya ake cikine tsakanin yazeed da
Zakiyya

Ina jiran comments dinku kada ku manta da offer na.

NAGODE

takuce @mzz_untichlobanty

24 August, 2019

Miss untichlobanty💕

Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top