Թɑցҽ 8
*INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION*
{Onward together}
*{ we give the reader's of ours the best out of the best's,, our inks are melodious And dropping a kinda light's to reader's}*
'''THE PEN OF LOVE 😘 HEART TOUCHING ❤ TEARS OF SORROWS😭 CURDLES 😊 GIGGLES 😁 AND MARRIAGE THINGS 💑'''
*JUST GIVE US FOLLOW.....*✔
💥
❄️❄️❄️❄️❄️❄️❄️❄️
*Ḧ̤Ï̤B̤̈B̤̈Ä̤T̤̈Ṳ̈L̤̈L̤̈Ä̤Ḧ̤*
❄️❄️❄️❄️❄️❄️❄️
*°•(ĸyaυтa daga Aℓℓαн)•°*
*°ιиιqυιту,ємραтну,нυмιℓιαтισи & яσмαи¢тι¢ ℓσνє💑°*
*MALLAKAR:HAFSAT HAFNAN💕*
*WATTPAD:HAFNANCY:*
*°ѕα∂αυкαяωα gα Dr. υмαя fαяυq вαнαgσ,ємιя σf иιgєя ѕтαтє,мιииα*°
____________________________________
💥
*Թɑցҽ 8⃣*
Najmiy kuwa tana shiga b'angaren Haj.Babba taji wani uban kuka ya taho mata,sam bata lura da Haj.Babba da kuma Haj.karama dake zaune afalo ba,sai kuma ƙuyangun dake durkushe agabansu suna musu hidima,masu firfita sunayi,haka kuma masu tausa nayi.ko lura dasu batayi ba dake makeken falo ne,ta nufi dakin baccinsu da gudu tana 'yar shessheƙa.
Haj.karama ce ta soma hango bayanta tana wucewa zuwa daki da dan gudu-gudu.Cike da tashin hankali ta dubi Haj.Babba wacce bata masan abinda ke faruwa ba sai aikin baiwa wata ƙuyangi order take dake mata tausa.Tace"Yaya kalli auta can ta shigo da gudu kuma kamar ma kuka take... "
Agigice Haj.Babba ta dubeta tace"Ina autar take?"
"ta shige daki.. "acewar Haj.Karama
"maza Maymunerh tashi muje mu dubota nidai Allah yasa lfy dai... " Haj.Babba ta fadi hakan tare da mik'ewa at once,suka sallami kuyangu,kana suka nufi hanyar dakin da Najmiy ta shige da sauri saurinsu.
***
Bawan Allah kuwa Hayat yana nan zaune dai inda Faruq ya barshi,zuwa yanzu hawayen ya daina zubo masa,sai saukar da numfashin da yake tayi da karfi,acikin wannan halin ne su Jabir suka shigo suka riskesa,acikinsu babu wanda ma ya lura da yanayin da yake ciki don suna shigowa ko hada idanuwa dashi basuyi ba suka zube ak'asa,kafin Jabir yakai ga magana tuni yaji Hayat yayi saurin katse masa hanxari"Jabir wai sau nawa ne zan gaya muku cewar ku dena zub'e min ak'asa?karfa ku manta dani daku duk daya muke awajen Allah,wanda kawai yafi wani matsayi awajensa shine wanda yafi tsoronsa,kuma ko ba komai ai ni din k'anin bayanka ne na nesa ba kusa bama,don Allah ku daina bana so,pls get up immediately.... "
Allah sarki!ta inda kuma suke son Hayat kenan,sam bashi da ganin kansa azuwan shi din wani ne,infact yama daukesu kamar yan'uwansa ne.
Jabir yace"Allah ya taimaki jarumin jarumai,amatsayinka na dan sarki ya zama dole kaima mu girmamaka,don haka kayi haquri bazamu iya dainawa ba...... "
Bai tankashi ba,ya dauki ruwan faron dake gabansa,ya balle marfinta,sai daya furta"Meke tafe daku yakai amintaccen Abba mai martaba?" kafin yakai bottle din bakinsa.
Jabir yace"Allah yaja da ran Yarima Karami,ga sako zuwa gareka daga mai martaba,yace yana nemarka da gaggawa..... "
Da sauri ya cire bottle din daga bakinsa,ruwan kuwa ya kwareshi sosai wanda ya janyo masa wani mugun tari har idanuwansa sukai jajawur,duk kuma adalilin tashin hankalin daya shiga ne,hakan na nufin Faruq yakai kararsa ne koko menene?don fitarsa kenan baa wani jima ba sai ga dogarai wai mai martaba na nemarsa da gaggawa kuma yanxun nan.
Dogarawan kuwa sai sannu suke ta masa ayayin da yake ta aikin gyad'a musu kai alamun amsawarsa kenan.Can ya dubesu cike da faduwar gaba bayan tarin ya sakeshi yace"Jabir kuje gani nan tahowa... "
"A'ah Yarima karami mai martaba yace kafarmu kafarka. " Gabansa ne ya tsananta faduwa jin furucin Jabir,atake anan ya sake tabbatarwa kansa da cewar lallai kararsa Faruq yakai.
Mik'ewa yayi ya shige gaba yace"ku muje... " suka take masa baya da sauri sauri.
**
Gabansa ne ya karashe tsinkewa ah sa'ilin da sukayi ido hudu da mai martaba wanda se faman jifarsa yake da wani irin mugun kallo,kana iya cewa ma kashe masa wani Hayatun yayi.Shi kuwa Faruq kansa ya saddar kasa alokacin daya jiyo takun tafiyar Hayat,ko kadan baya son su hada idanuwa.
"Barka da warhaka Abba mai martaba,sakonka ya riskeni don haka gani gareka Allah dai yasa lafiya.... "
"Ba lafiya ba..... "acewar mai martaba cikin hargowa.Hayat baiyi mamakin jin furucinsa ba don dama can jikinsa ya bashi cewar Faruq ne ya kawo kararsa,watakil k'arya da gaskiya ne ya fad'a masa.
Mai martaba ya sake cewa"kana jina ko?nace ba lafiya ba,meh ka gayawa Najmiy dazun?"
Murmushin takaici Hayat yayi kana yace"Abba mai martaba cewa nayi ina sonta ko kuwa yanzu ya zama laifi ne mutum yace yana son wani?"
"Rufemin baki anan mutumin banza da wofi,ita ya kamata ka gayawa hakan ko ni?meyasa baka sameni ka nemi izinin tunkarenta ba ko kuwa zamanka take agidan ne?"
Hayat na kokarin magana tuni mai martaba ya rigashi"Shhhhhhh! yi min shiru anan bana son jin komai daga gareka,ka bude kunnuwanka ka saurareni dakyau,daga yau sai yau bana son ka sake keb'ancewa da ita don Najmiy amanar Allah ce agareni,idan na kuskura nayi sakaci har rayuwarta ya gurbata toh kuwa Allah bazai tab'a yafemin ba,Hayatudden Bahago bazan tab'a baka auren 'yata Najmiyya Gaddafi ba,Najmiy marainiyace don haka yasa nakeson na aurar da ita ga namiji nagartacce wanda nasan zai kula min da ita,wanda kuma nasan bazai taba bari tayi kukan maraici ba dede da minti daya,amma bakai ba Hayat,kaje na yarje maka ka zab'o duk wacce ta maka afadin duniyar nan,muddin dai tana kai kanta k'asa tofa zan aura maka ita,amma ba Najmiy ba,kuma daga yau sai yau na haramta maka k'ebancewa da ita,wannan shaquwar kuma arageta bana so,idan kuma aka kuskura aka sab'a umarnina tofa zanyi hukunci da kuma daukar kwakkwarar mataki,don haka kayi gaggawan yakiceta daga cikin xuciyarka... "
Gabaki daya network din jikin Hayat ya tsaya cak! ya daina aiki,haka ma dukkan jijiyoyin jikinsa sun tsinke da kalaman mai martaba,gwiwowinsa sun sake,gaba daya kawai yaji duniyar tana juya masa,dakyar ya budi baki yace"Abba mai martaba don Allah karka sa na soma tunanin cewa bakai ne ka haifeni ba,don aganina da kuma iya sanina babu mahaifin da zaiso ganin ya salwantar da farin cikin dansa da gangan,fisabilillahi! Menene aibuna don kawai nace ina son Najmiy?don Allah ba abin farin ciki bane ma don ina son na taimaka mata ita da bata da asali ma?kuma wanene yace ni din bazan iya share mata kukan maraicinta ba?haba Abbana meyasa?
Fashewa yayi da wani kuka mai tsuma xuciya,da sauri ya isa ga Mai martaba ya zub'e agabansa tare da kamo kafafuwansa,yace"Don Allah Abba mai martaba idan wani laifi na maka wanda ni ban sani ba,toh don Allah ina rokanka daka yafemin dan'adam ajizine,amma pls karka hanamin samin farin cikina,wallahi ina son Najmiy,she really captured my heart starting from day one,kuma itama nasan tana sona,wallahi ku k'irata ku tambayeta nasan zata fad'a muku gaskiya...... "
"Hey! Young man karkayi tunanin cewar shaquwar dake atsakaninku so ce,sam abin ba haka bane,shaquwa daban haka kuma so daban yake,don haka bana tsammani Najmiy sonka take kamar yadda kai kace kana sonta.... "Faruq ne ya fadi hakan.
Hayat ya dago yana dubansa,cike da tsanarsa yace"Ai dama nasan kaine ka hada komai,ka shimfidawa Abba mai martaba k'arya da kuma gaskiya,waya sani ma ko kaima son Najmiy din kake shiyasa kake son ka hada bomb?"
"Allah ya kiyaye,tirr da wannan negative thinking din naka,Najmiy kallon qanwar da muka fito ciki daya nake mata,kallon Hidaya da kuma Abida nake mata,kai ko zan nemi budurwa ma ni bazan taba nemar yar kankanuwa kamar Najmiy ba,haba brother wat You are trying to do is simply child abuse.... "
Haqiqa kalmar 'child abuse' ta daki Xuciyar Hayat don har runtse idanuwansa yayi gam,kuma agaskiya Umar ba wai son Najmiy yake ba,shi kawai gani yake Najmiy bata kai matsayin da har zata soma soyayya ba (waya gaya maka?)
Mai martaba kuwa saddar dakai yayi kasa yana saurarensu,yama rasa ta cewa,shidai gaskiya acikin 'ya'yansa yafi qaunar Hayat amma bazai iya bashi Najmiy ba don sosai zata cutu da halayyarsa bayan aure,wanda ko kadan bazai taba so hakan ta faru ba.
*
Acan daki kuwa,su gimbiyoyin ne suka tasa Najmiy agaba akan tayi musu bayanin abinda ya sakata kuka,dakyar ta hadiye kukanta kana tace"Wai ya za'ayi ace Yaya Prince karami ya kalli cikin k'wayar idanuwana yace yana sona?shin ya manta cewar ni din k'anwarsa ce?ko kuwa haka kukeyi anan?ko kuma nace shin haka kukeyi ah al'adarku wa yace yana son k'anwarsa da soyayya?"
Jikin Haj.karama ne yayi sanyi qalau da jin wannan zance na Najmiy,ita kuwa Haj.Babba sosai abin yayi mata dadi na ganin za'ayi 'yar gida gida ne,haka ma su Abida abin yayi musu siga sosai.
"Abinda ya sakaki zubda hawaye kenan?" haka haj.karama ta furta sam babu ko digon annuri akan fuskarta,kai kawai Najmiy ta daga mata alamun eh. "Toh share hawayenki yarinya don nima ko kadan bana qaunar wannan hadin.... "
Cike da mamaki Haj.Babba tace"Haba Maymunerh lafiyarki kuwa?wannan wani irin zancen banza kenan?Najmiy ce fa?shine kike ambaton cewar bakya qaunar hadin nan?toh gaskia ki sake tunani Maymunerh don nidai banga dalilin dazai saka kiyi irin wannan furucin ba.... "
"Yaya akwai dalili... "acewarta
Haj.babba tace"Wani dalili kenan?"
"ki bari anjima zamuyi magana... "
Ta maida kallonta ga Najmiy tace"Ke ina Hayatun yake?"
Da rawar murya Najmiy tace"Na barosa ah inda muka saba bitar karatunmu..... "
Fuuu! ta mike tayi hanyar kofa,Haj.Babba na mata magana ko waigowa batayi ba balle asa ran zata tankata,da hanzari Najmiy tabi bayanta tasha gabanta,kamo hannayenta tayi tace cikin muryar kuka"Ummi khuddha basat (take it easy),don Allah na rokeki karki masa fada,kedai ki sake tunatar dashi cewar Najmiy qanwarsa ce,don haka bai kamata ace ya furta Kalmar so agareta ba...... " kala bata ce mata ba ta rab'a ta gefenta ta wuce.
Haj.Babba wacce fitowarta daga daki kenan tace"Ke kuwa Najmiy in banda abinki ai akwai aure atsakaninki da Hayat,Hayat ba shaqiqinki bane,ba ciki daya kuka fito dashi ba,don haka akwai aure tsakaninku..... " she was suprised sabida ita bata taba sanin cewa ana iya auran gida gida bama,kuma ita ta dauki su faruq kamar 'Akhee dinta ne wanda suka fito ciki daya.
Haj.karama ta janyo hannunta suka zauna saman kujera,kana ta shiga warware mata komai dalla dalla harta fahimta,sai dai har yanzu mamakin bai bar fuskarta ba.
_*Toh yanzu bari mu koma fada mu dubo wainar da ake toyawa,sannan kuma meh Gimbiya Maymunerh take nufi ne?kuma meh take shirin aikatawa?ku biyoni*_
*ⓗⓐⓕⓝⓐⓝ💕*
Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top