Թɑցҽ 19

❄️❄️❄️❄️❄️
          *Ḧ̤Ï̤B̤̈B̤̈Ä̤T̤̈Ṳ̈L̤̈L̤̈Ä̤Ḧ̤*
             ❄️❄️❄️❄️❄️

         *°•(ĸyaυтa daga Aℓℓαн)•°*

*°ιиιqυιту,ємραтну,нυмιℓιαтισи & яσмαитι¢ ℓσνє💑°*

  *MALLAKAR:HAFSAT HAFNAN💕*

     *WATTPAD:HAFNANCY*

https://m.facebook.com/Hafnans-Novell-246747739535534/

*°•ѕα∂αυкαяωα gα Dr.υмαя fαяυq вαнαgσ,ємιя σf иιgєя ѕтαтє мιииα°•*

      *°•ιnтellιgenт wrιтer'ѕ aѕѕo✍*

https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
__________________________________
                          💥

_*°•wαnnαn pαgє dín mαllαkínkí nє mαrчαm chuввч hαчαt,kαmαr чαddα kíkє ѕσn hαчαt αzαhírí,tσh kí ѕαní ѕhímα чαcє nα gαчα míkí cєwα чαnα mutuwαr ѕσnkí kumα zαí kσkαrtα чα αurєkí tundα αn mαѕα kwαcєn nαjmíч😉•°*_

     _*°•mαmαn αmírα tαwα ínα míkα gαíѕuwαr вαn gírmα αgαrєkí,nαgσdє ѕσѕαí dα qαunαrkí dα kumα kulαwαrkí αkαínα,hαfnαn ítαmα tαnα míkí ѕαn ѕσ fíѕαвílíllαhí💕•°*

  *Թɑցҽ 1⃣9⃣*

      """"Haj.Babba ta kasa haquri yama karaso gareta,don haka da dan gudu-gudunta ta soma kokarin isa zuwa gareshi,ganin ta nufoshi da gudunta,yasa shima ya kara sauri ya isa gareta tare da rungumeta tsam! tamkar wata babynsa.Hawaye na gangarowa mata saman kunci tace cikin sanyin murya"Hayatudden Bahago kai ne haka?ashe dama zamu sake sanyaka ah ido kafin mu kwanta hannun dama?Hayatu why?meyasa ka gujemu my son?"

    Rushewa yayi da wani uban kuka wanda har hakan ya saka jijiyon kansa mimmiƙewa,yace"Mother pls forgive me wallahi bin son zuciya beyi ba arayuwa,gashi na kashe mahaifiyata da bakin cikina,Abbana kuma yana kwance ba lafiya,na haddasa masa damuwa wanda hakan ya haifar masa da ciwon shanyewar barin jiki,sannan ace ni Hayat zan gama da duniya lafiya bayan na sab'awa mutanen da sukayi sanadiyyar zuwana duniya?na kuntata musu sannan ace naga haske acikin lamuran rayuwata?sannan kuma ace na samu rahamar ubangiji gobe kiyama?Gaskiya ni ba dan albarqa bane,am a cursed child..... "

   Ji kake tasss!Haj.Babba ta daukeshi da wani mahaukacin mari,cikin tsananin bacin rai tace"Hayatu menene kake fada ne haka?anya kanka daya ne kuwa?haba d'ana meh zai saka har kayi irin wannan furucin?ko shin bakayi imani da Allah bane?inason ka dauka cewa duk wani abinda ya faru dakai jarabawa ne daga ubangiji,don haka Allah yasa kaci wannan jarabawar,taho muje ga mai martaba yaga farin cikinsa,na tabbata insha Allahu daga yau ciwonsa ya kare,zaya mike akan kafafuwansa sannan kuma bakinsa zai bude insha Allah... "

     Ta kamo hannunsa suka nufi turakar mai martaba,suna dab! da isa sai ganin su Abida sukayi sunsha gabansu(Dake aranar Abida tazo don Haj.Babba ta mata waya cewa ai su Hayat na tafe shine tazo).

Sun fito gani ne koda gaske dinne Hayat ya dawo,Abida tace cikin muryar kuka"Yayah prince karami is diz you?kai such is life,Allah ya kyauta... " ta juya tayi ciki da gudu,ita kuwa Hidaya cewa tayi"Barka da dawowa Yayah prince... " itama tayi gaba,jikinsa duk ya mutu da kalaman Abida,ya dago kansa ya sauke kallonsa kan Najmiy wacce take tsaye tana zubda ruwan hawaye,jira yake tace masa wani abin amma ga dukkan alamu ya nuna cewa bata da niyyar magana.

    Ahankali yace"Najmiy kiyi magana pls,ko 'yar zagice kimin don naji dadi araina... " da sauri ta kalli Faruq wanda yake tsaye ya cika yayi fam dashi,alamu yayi mata da ido,ai tuni tayi cikin gida tare da fashewa da kuka.

    "Ni muje don Allah tunda har yanxu baka hankalta ba... " Haj.Babba ta fadi hakan tare da sake masa hannu tayi ciki abunta.Cike da kasala ya soma takawa,da sauri Faruq yasha gabansa yace"Mal.dakata bazaka shiga ganin mahaifina haka kai tsaye ba,ka bari na nemo maka izininsa tukunna... " kan yayi magana tuni Faruq ya juya ya shige turakar mai martaba ya barshi nan tsaye,shi kuwa kallon mamaki ya bishi dashi,wai shi da mahaifinsa ayau aka hana masa ganinsa kai tsaye wai har sai anje an nemo masa izini,lallai son xuciya bata kareshi da komai ba illa jefashi cikin bala'i da kuma kuncin rayuwa.

    Cak! ya tsaya wuri guda tare da harde hannayensa abaya,shike nema asulhunta tsakaninshi da mahaifinsa don haka bai kamata ya haifar da wata rigima ba,shiyasa ya kwantar da kai.

  ______________****_______________

     Haj.Babba na shiga dakin mai martaba,cak! ta tsaya abakin kofa ayayin data shiga wulla masa wani irin tattausan murmushi daga inda take tsaye,shi kuwa mai martaba dake kishingide asaman gado ya bita da kallon rashin fahimta,can ta soma takawa xuwa inda yake tana fadin"Ranka shi dade Ina tafe maka da wani babban albishiri... "

      Ta dan dakata tare da tsura masa ido tana mai son tantance irin yanayin daya shiga,gyad'a mata kai kawai yayi alamun yana jinta,da sauri ta waiga don azatonta Hayat ne ke biye da ita,sai kuma taga sab'anin hakan,Faruq ne ta gani ya sawo kai cikin dakin shi kadai,ahankali ta furta"Kai ina Hayatun yake ne?"

"Hajiyata kibar komai ahannuna,naki kawai shine kallo... " ya bata amsa cike da ladabi.

  Yana gama fadar hakan ya nufi Abbansa,shi kuwa mai martaba wani irin farin ciki ne ya ziyarcesa alokaci guda na ganin Faruq,sai yayi tunanin kila albishirin da Gimbiya Hadizarsa ke shirin fada masa kenan,wato dawowar shi Faruq din.

   

  Faruq na isa gareshi yayi saurin karya gwiwowinsa zuwa kasa,da sauri ya kamo hannun mai martaba mai lafiyar,babu bata lokaci hawaye ya soma sakko masa,Cikin raunin murya ya soma magana"Abbana Allah yayi na dawo lafiya,kuma nayi nasarar taho maka da maganin lalurarka,yanxu kai nake jira kawai kaban izini sannan naje na shigo maka dashi"

      Dakatawa yayi yana kallon mahaifin nasa wanda ya kura masa idanuwa cike da so da kuma qaunar dan nasa,nisawa yayi yace"Abbana naje na shigo maka dashi... "

Gyad'a kai mai martaba ya shiga yi babu gaggautawa wanda hakan ke nuni da cewa lallai yana maraba da koma meye ne dari bisa dari.

  "Thank you Abbana,u the best.. " Faruq ya fada tare dakai masa wani kyakkyawan sumba asaman hannun,kana ya mayar da hannun ya ajje ahankali akan filon dake gefen mai martaba,da sauri ya mike ya fice ayayin da Abbansa ya bishi da kallon qauna,ita kuwa Haj.Babba wani sassanyar ajiyar xuciya ta sauke kana ta sami wani sofa ta zauna,sosai take yabawa da halin kirki irinna danta Faruq,babu abinda ya baro na daga cikin halayyar mahaifinsa,he's just like a photocopy of his Abba.

  **
"Hey!you my dear naughty brother.. " Faruq ya fada ah sa'ilin daya sauke kallonsa kan Hayat,shi kuwa Hayat bema san yanayi ba don gabaki daya hankalinsa ya tafi can duniyar tunanin mutane uku ne,na daya gamuwarsa da Abbansa,abu na biyu kuma rasuwar mahaifiyarsa wanda ke dukansa sosai aynxu,abu na k'arshe kuma shine 'Najmiy Gaddafi',he still loves her,babu abinda ya ragu daga cikin irin son da yake mata,hasalima ji yake kamar wutar soyayyarta ta sake ruruwa ne acikin xuciyarsa na ganin daya mata ayanxu,kai Najmiy she's juz older than her age,yarinya 'yar 17 amma kamar 'yar 20,dama yawancin labarawan nan akwai girman jiki,gashi kuma education dinta is moving very very fast kuma kokarinta ne ya haifar da hakan,she's in her year two now ah midwifery,ita da Hidayah.

   "Wai ko bakaji abinda na fada bane?" Faruq ya sake fada cikin fusata.Sai asannan ne Hayat ya dawo cikin hankalinsa,yace"Yayah prince wai magana kake ne?"

Kallon rainin wayau Faruq ya wurgeshi dashi kana yace"Eh! cewa nayi ka shigo Abbana ya baka izini.. " yana gama fadar hakan ya juya ya shige ciki,shi kuwa Hayat sosai kalaman Faruq din ya daki xuciyarsa da kuma yadda yake nuna masa isa da gadara sai kace shima ba mahaifinsa bane,don kawai ya aikata ba dede ba shine Faruq ke masa irin wannan cin fuskar?

   Ahankali yaja jikinsa ya soma takawa ciki,xuciyar nan tasa kamar zata faso waje don tsananin tsoro da kuma fargaba.

    **
Faruq na shiga dakin ya sami waje ya zauna,Haj.Babba kuwa da Mai martaba wanda baisan inda aka dosa ba suka xubawa kofar shigowa ido,sai da Hayat ya kwashi kusan mintuna biyar kafin yayi shahada ya doka sallama ya shigo,idanuwan mai martaba ƙyam akansa.

   Acikin seconds biyar kawai,Abba mai martaba ya shiga vibrating sabida wani gagarumin shock daya kai masa attack alokaci guda na ganin Hayat,bai taba mafarkin sake ganin Hayat ba arayuwarsa,atunaninsa ma Hayat din baya ma araye ne.

Wani abin mamaki da kuma ikon Allah shine,bakinsa daya rufe,wato maganarsa da tayi ceasing ada sai gashi ayau Allah ya bude masa shi,cewa yayi"Hayatu dana kai ne?"

   Da sauri yace"Abba mai martaba wallahi Hayatunka ne" ya fada tare da karasawa inda yake da sauri.

Haj.Babba kuwa alokaci daya suka mike ita da Faruq har suna rige-rigen cewa"Alhamdulillah Allah mun gode maka bakin Abba mai martaba ya budu" suka fada cike da farin ciki,amma sai dai basu matsa kusa dashi ba,so suke ya gama ganawa da Hayat tukun.

     Hayat ya zube asaman kafafun Mai martaba,axuciye Faruq yace"Kai wai so kake ne ka karashe mana shi?ko kuwa bakasan cewa akan kafafuwansa da basu da lafiya bane ka zub'e?"maza ka dagashi don da'ace da gaske kake kana sonsa toh kuwa da baka bar gida ba...... " wani wawan kallo haj.Babba ta wurgeshi dashi ta wutsiyar ido wanda hakan ne ya sashi saurin yin shiru.

   "Am sorry Yayah prince mantuwa ce nayi... "Hayat ya fada cikin sanyin murya kana ya daga daga jikin mai martaba,kasa hada idanuwa dashi yayi don sosai yake jin kunyarsa,cikin kuka ya soma magana"Abbana haka ka koma wai duk akaina?wallahi ni har kunyar hada idanuwa dakai nake don ko kadan ban kyauta maka ba,nabi son xuciyata da kuma zugar abokai wanda gashi ya kaini ya baro acikin kogin danasani mara amfani,Abbana ko ahakan ma idan ka barni yayi don naga darussa da yawa na rashin bin maganar iyaye,Nayi sanadin barin mahaifiyata duniya,gashi kai kuma na janyo maka wani mugun ciwo,Abbana don Allah karka juya min baya,don Allah ka gafarta min,Hajiyata kema ki yafemin kuma Allah yakai rahama da haske kabarinki.... "

   Kuka yaci karfinsa,hawaye yadan zubowa Mai martaba saman kunci,hannunsa mai lafiyar ya daga,hannun na rawa amma saida ya kokarta yakaishi saman kan Hayat ya dire,ahankali ya soma magana"Allah yayi maka albarka Hayatu,ko bakomai nayi farin ciki da dawowarka gida kuma nafi kowa farin ciki daka furta da bakinka cewa kaga darussa da yawa arayuwarka daka tsallake maganar iyaye,alhamdulillah! hakan yayi kyau sosai kuma naji dadin hakan,kuma sannan wacce ka bar gida dominta kamar yadda na fada tun farko,'A' dina 'A' ne,na aurar da Najmiy ga Yarima Umar Faruq,don haka sai ka sake komawa inda ka fito idan kaga bazaka iya rungumar kaddararka ba............ "

  _*тoғa мy jaмa'areѕ wнo aмong yoυ can deѕcrιвe ιrιn yanayιn da нayaт ya ѕнιga yanхυ?*_

_*нммм! aввa мaι мarтaвa aм ѕorry тo ѕay ka ĸυnno rιĸιcι aн ғaмιly dιnĸa,нow ι wιѕн daĸa нana ĸowa najмιy,daĸa вaιwa wanι can awaje ne aυrenтa da ĸoмaι вaι ғarυ вa,мυje хυwa #тeaмнaғnanFans#*_

   _*ĸυyι мana нaqυrι da raѕнιn jιnмυ ĸwana вιyυ wlнy вaмυ dan jιndadι gaвaĸι dayanмυ мυ тrιpleтѕ,nι,мy ѕιѕ nerja'arт da ĸυмa ѕιѕ janaғ*_

_*σчα lєt'ѕ kíndlч nσvє tσ thє nєхt lєvєl👇*_

        _*mσm híввαh💕*_

Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top