Թɑցҽ 18
❄️❄️❄️❄️❄️
*Ḧ̤Ï̤B̤̈B̤̈Ä̤T̤̈Ṳ̈L̤̈L̤̈Ä̤Ḧ̤*
❄️❄️❄️❄️❄️
*°•(ĸyaυтa daga Aℓℓαн)•°*
*°ιиιqυιту,ємραтну,нυмιℓιαтισи & яσмαитι¢ ℓσνє💑°*
*MALLAKAR:HAFSAT HAFNAN💕*
*WATTPAD:HAFNANCY*
https://m.facebook.com/Hafnans-Novell-246747739535534/
*°•ѕα∂αυкαяωα gα Dr.υмαя fαяυq вαнαgσ,ємιя σf иιgєя ѕтαтє мιииα°•*
*°•ιnтellιgenт wrιтer'ѕ aѕѕo✍*
https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
__________________________________
💥
_*°•wαnnαn pαgє dín mαllαkínkí nє mч lσvlч ukhtí 'rαmlєrh',ínα ѕσ kí ѕαní cєwα ѕíѕ hαfѕαt dínkí tαnα míkí ѕσ mαrα íчαkα wαndα вαвu αlguѕ αcíkí,uвαngíjí Allαh чαвαr qαunα dα хumuncí mαí dσrєwα,αmєєn°•*_
*Թɑցҽ 1⃣8⃣*
_*°αddu'αr nєmαr tѕαrí dαgα αzzαlumαí kσ kumα mαhαѕѕαdα👇°*_
_*°•Allαhummα rαввαѕ-ѕαmααwααtíѕ-ѕαв'í,wαh rαввαl-αrѕhíl-αzєєm,kun lєє jααrαn mín(ѕαíkα αmвαcí ѕunαnѕα),wα'αhzααвíhí mín khαlαα'íqíkα 'αn чαfrutα 'αlαччα 'αhαdun mínhum 'αw чαtghαα 'αzzα jααrukα,wαjαllα thαnαα'ukα,wα lαα'ílαhα 'íllα αntα•°*_
💥💥
---------Har Hayat ya daga yalalon labulen dakinsu zai shige,sai kuma ya jiyo sallama daga bayansa,muryoyi fiye da biyu ne suka daki dodon kunnuwansa amma yafi saurin shaida muryar Tsoho,don shi da karfinsa ya doka sallamar.Cike da fara'a Hayat ya saki labulen ya juyo yana mai fuskantarsu dakyau,yace"Ayyah baba tsoho abokina kaine tafe?Don Allah kayi haquri yau banzo kiranka muje masallaci ba wallahi yau ban dawo da wuri bane,hasalima yau sallah raka'a daya ce kawai na samu ta magrib,ina can har isha'i amma ko mai kama dakai ban gani ba,nace toh yau Tsoho lafiya kuwa ban gansa amasallaci ba?yanzu haka ma so nake naci abinci sannan na shigo dubiyarka sannan na damkawa Yah Rilwan raguwar kudin gidansa.. "
Shi kwata-kwata hankalinsa ma baya ga mutane biyun dake tsaye agefen tsoho,kuma ko kadan yaki baiwa Tsoho damar magana,yacigaba"Tsoho albishirinka?gobe Zan koma....... "
Wutar da nepa suka kawo ne ya katse masa maganarsa,kuma wutar lantarkin dake can sama ah bangon kofar dakinsu ya matuqar taimaka wajen haskaka masa fuskokin duka halittun dake tsaye agabansa.Ido cikin ido suke kallon juna da prince Faruq.
Akalla sun kwashi kusan daƙiƙu hamsin suna kallo-kallon junansu,Hayat shine wanda ya soma kawar da dogon silent din ta hanyar furta" *'YAYA PRINCE......... '* Ya fadi hakan cikin ƙaryewar murya,sannu ahankali wasu hawaye masu dumi suka soma gangaro masa saman cheeks.Jaa da baya ya soma yi kadan da kadan fuskar nan tasa shimfide take da tsansar mamakin ganin Faruq agarin Lagos kuma wai acikin gidansu,cikin rashin sani yaci karo da wata 'yar karamar kujera dake bayansa,ai kuwa kiris ya rage ya fadi,amma kafin yakai kasa sai yayi saurin sanya hannu ya dafe Bango.
"Hayatu kabi ahankali karka fadi don Allah... " acewar Tsoho.
Tsoho ya maida kallonsa kan Faruq wanda yayi mutuwar tsaye,ruwan hawaye ne kawai keta bulbulowa saman kuncinsa,kuma har yanxu bai dauke kallonsa akan Hayat ba.Duk da cewa dare ne amma wutar lantarki ta taimaka wajen hasko masa yadda kamannin Hayat ya sauya,ya mugun tara sumar kai,haka ma kasumbarsa ta cika fuskarsa,abu dai kamar ba Hayatudden Bahago dan Qayun daya sani ba.
Maganar tsoho ce ta maido da hankalinsa daga duniyar nazarin daya shiga akan Hayat,cewa yayi"Mal.Faruq mu zamu koma gida,zamu baku wuri ku sulhunta,idan har kun daidaita saiku samemu acan... "
"Toh Baba" shine kawai abinda ya iya furtawa cikin dauriya.
"Kai Rilwanu muje.. " acewar Tsoho,har sun juya zasu fice sai kuma Tsoho ya tuna da wani abu,ai kuwa da hanzari ya koma da baya,ya nufi kofar dakinsu Hayat,daga labulen sama yayi,can ya hango Roughcoin raƙube abango,jikin nan nasa sai aikin maƙyarƙyata yake don duk yana ta jin conversation dinsu dake ta wakana atsakar gidan,wato dai *'PRINCE UMAR FARUQ BAHAGO'* is here kenan,lol yasan kashinsa ya bushe shiyasa ya shiga cikin tsantsar tashin hankalin nan.
Dariyar mugunta Tsoho yayi kana yace"Shege katon arne ashe dai kaji komai,dan'iska mayaudari kawai,don wallahi ba'a gaya min ba amma nasan dasa hannunka acikin lamarin bawan Allah Hayatu,wallhi karshenka baza tayi k'yau ba,ni wallahi harna hango mazauninka acikin gidan wuta,zaka fito ne ko kuwa saina shigo na sameka anan?" hahah! Tsoho ya sami opportunity don ko dama can shida Roughcoin ko kadan basa shiri,Roughcoin sam baya daraja Tsohon,har ce masa yake Tsohon banza.
"Baba hadda son zuciyar shi Hayatun aciki don haka karka gama dora laifin akan abokinsa.... " haka yaji Faruq ya fada cikin wata kakkausar murya.Jikin Tsoho ne yayi sanyi qalau,ahankali ya juya yaja hannun Rilwan wanda nashi kawai kallo ne yake tayi,har sun kai kofar fita sukaji Faruq yace"Baba ina fatar ba fushi kayi da kalamaina bako?idan kalaman nawa sunyi tsauri ne da yawa toh don Allah ina nemar yafiyarka.. "
Harga Allah ba fushi Tsoho yayi ba,jikinsa ne kawai ya soma tsinkewa da lamarin Hayat,ya tabbata akwai magana akasa sosai akanshi,wai ma don bai san cewa mahaifiyarsa ta rasu akanshi ba kenan.
"Dana wallahi ba fushi nayi ba,nidai idan kun gama ina jiranku agida... " yasa kai ya fice ayayin da Rilwan ya take masa baya.
Roughcoin ne yayi shahada ya fito aguje saura kiris suci karo da Faruq,yayi kofar fita daga gidan ah 180 kai kace ko wani babur ne😂.
Hakan kuwa da yayi ba karamin dariya ya baiwa Faruq ba,harda kwallansa kuwa,ya rakashi da"Bloody monster daka bi ahankali donni bata kai nake ba,infact bani da deal dakai don hadda son xuciyar kanin nawa aciki,kadai je ka gyara rayuwarka if not kana iya karewa agidan wuta,asararre kawai.... "
Yana gama fadar hakan ya dauke dariyarsa,alokaci daya kuma ya juya yana fuskantar Hayat.
Ahankali ya furta"Hayatudden Bahago...... "
Cikin rawar murya yace"Ya... yah princeeeee waya gaya maka inda nake?"
"Ibrahim spanzy.. " Faruq ya bashi amsa atakaice ah sa'ilin daya watsa hannayensa cikin aljihun wandonsa.
Kafin Hayat ya gama shanye mamakinsa kawai yaji Faruq ya cigaba"Spanzy shine wanda ya gayan komai,garin da kake da kuma unguwar da kake zaune,da kuma sana'ar da kake yi,u hav completely turned into an enormous drunker,what an outrageous and shameful thing?the whole prince of sarkin minna has turned his life into a mess!!! Shame on you Hayatudden freaking Muhammad Khamis Bahago.. "
Hayat ya karya gwiwowinsa zuwa kasa tare da fashewa da wani irin matsanancin kuka tamkar wani karamin yaro,sosai yayi nadamar biyewa zugar aboki kamar Roughcoin.
"Wai duk akan 'ya macece kabar gida?'ya macen ma da bata san kana yi ba?'ya macen da ayanxu hankalinta nacan wani wuri ne daban ba'a kanka ba?macen da take can tana rayuwarta hankalinta kwance kai kuma kana nan kana fuskantar kalubalen rayuwa akanta?bayan bata San kana yi ba?akanka mahaifiyarka ta kamu da congestive heart failure har yayi sanadiyyar barinta duniya,kuma abin mamaki da haushi wai duk kana da information akan hakan amma don toshewar kwakwalwa da kuma rashin imani ka kasa dawowa gida.... "
Matsawa yayi kusa da inda Hayatun ke zaune,shima ya karya gwiwowi zuwa kasa kamar yadda yaga Hayatun yayi,in otherwords,kneels down nake nufi,kana ya cigaba"Hayatu mahaifiyace fa?wacce ta dauki cikinka for good 9months,alokacin da zata haifoka kuwa kafarta daya aduniya dayan kuma alahira ne,alokacin ta fidda rai ne ga rayuwa,tayi nakudarka cikin radadi da kuma azaba,ta raineka cikin tsananin sonka da qaunarka kasancewarka dan data haifa kwara daya tak aduniya,taci kashinka,tasha fistarinka,ta tsotse majinar hancinka don kawai kayi looking good,dede da minti daya bata qaunar taji kukanka,da sauransu dai,shine kai kuma Hayatu ta hanyar da zaka saka mata kenan?ta hanyar kasheta da bakin cikinka?ta hanyar banzantar da mutuwarta?Brother u surely need prayers and deliverance.... "
"Akanka kuma mahaifinmu ke can kwance ciwon stroke ta kamashi,wai duk akanka kai daya Hayatu?kai ne kawai dan da suka Haifa?ta hanyar da zaka saka musu kenan ta kashesu da bakin cikinka?well,ni inason iyayena idan kai baka sansu,nazo nan ne ba don komai ba sai don na rokeka ka bini mu koma gida don kaine maganin lalurar Abba mai martaba,pls pls Hayatu bana son na rasa mahaifina don Allah ka biyoni mu koma gida... "
Da sauri Hayat ya rungumo dan'uwan nasa tare da bude wani sabon shafin kukan,kana yace"Yayah prince I hate myself for the cause of all this,dan'uwa nayi nadama sosai don Allah ku yafeni,bin son xuciya bai kareni da komai ba illa jefani cikin bala'i,nayi sanadin barin mahaifiyata duniya,haka kuma nayi sanadin da mahaifina ya kamu da ciwon shanyewar barin jiki,infact na jefa duk wani masoyina cikin kuncin rayuwa akaina,tirr! da haihuwata Yayah prince,nasan da'ace Haj.karama na raye,watakila zatace, _*'Hayatu dana san haka zakazo ka zama arayuwa harka samu kuka akanka,toh kuwa dana dade da barar da cikinka tun kana gudan jini'*_.... "
Da karfi faruq yace"Shut up! Hayat,zaka soma sakin layi ko?kodayake I won't blame you becuz I can see dat harwa yau bakasan meye kaddara ba,haka kuma baka san meh kalmar *'HAKURI'* da kuma *'DANGANA'* suke nufi ba,amma nevertheless,ina maka addu'a Allah yasa nan gaba ka sansu duka,sannan kuma kasan lokacin daya dace kayi amfani dasu... "
Tsagaitar da kukansa yayi,ya koma 'yar shessheka kana yace"Dan'uwa kayi haquri dama ina da niyyar komowa gida gobe don gabaki daya rayuwa ta juyan baya,haqiqa nayi nadama sosai Yayah prince,don Allah ka tashi mu wuce ma yanxu,inason naje ga Abba mai martaba na nemi yafiyarsa... " kan Faruq yayi magana tuni ya mike,har zai shige daki yaji kawai Faruq ya ruƙo hannunsa.
"Ina zaka?" acewar Faruq.
Ya juyo yana dan dubansa kafin yace"Hado kayana zanyi nazo mu tafi.. "
Murmushin takaici Faruq yayi,yace"Lallai Hayat na yadda baka da hankali,yanxu fisabilillahi sai mu dau hanyar doguwar tafiya acikin wannan daren?mu sami motar ma ah ina?ko azatonka amotar gida nazo?toh don ka sani amotar gwamnati nazo,kuma yasin bazaka bini da kayan kwarmasanka ba,jeka ciki ka kwaso important documents dinka kazo kawai mu tafi,sannan ka rufe gidan muje ka damkawa landlord makullin gida,nawa ne ma suke binku don kamar dazu naji ka ambaci cewa zaku basu sauran kudin gida da ake binku?"
Ahankali yace"Dubu hamsin ne. "
Jinjina masa Faruq yayi kana yace"kuma kana dasu?don gashi dai abokin cin mushen naka ya gudu ya barka aciki."
"Eh gasu acikin aljihuna cikakke don yau muka saida bus don mu samu mu biyasu kudinsu,sauran daya rage kuma muyi kudin motar komawa gida.. " ya fadi hakan tare da fiddo kudaden ya nunawa Faruq.
Murmushi kawai Faruq yayi kana yace"Hayatudden Bahago kaga rayuwa,fatana ayanxu shine Allah yasa hakan ya zamo babban darasi agareka da kuma duk masu bin son xuciya kamarka.. "
"Ameen amin,Yayah kayayyakin ciki fa su kuma ya za'ai dasu?"
Faruq yace"Masu gidan sa rabawa almajirai don wallahi bayan documents dinka ko tsinke bazaka bini dashi ba,kuma kamin sauri don ahotel zamu kwana,washeqari kuma mu Kama hanya... " Da sauri-sauri Faruq ya shiga ciki ya kwaso credentials dinsa,ya dudduba dakin da kyau yaga ashe Roughcoin ya kwashe nashi,ko bin takan kosai da biredin da Rough ya rage masa beyi ba ya fito ya sami Faruq,suka fito Hayatu ya kulle gidan,kana suka shige gidansu Tsoho,alokacin agogo ya nuna 9:35pm.
Tsoho na ganinsu ya shiga kabbara da nuna tsantsar farin cikinsa afilli,yace"Masha Allah abu yayi kyau sosai,naji dadi sosai da kuka daidaita kanku,ubangiji Allah yayi muku albarqa,Allah yasa kufi karfin xukatanku akodayaushe,haqiqa Mal.Faruq ka cika dan'uwa na gari daka ceto rayuwar dan'uwanka daga halaka,Allah yayi maka sakayya da gidan aljanna,kai kuma Hayatu ba karatu ba,ba komai ba,ka bi rudin abokin banza,kun shigo cikin rayuwar kashe wando,yanxu ba don 'yar sana'ar tukin nan da kukeyi kuke dan samun kudi ba da kuwa rayuwarku ta zamo kalar tausayi,don Allah abinda nakeso dakai shine kabi dan'uwanka ku koma gida,kuma koman rintsi koman wuya karka taba mantawa da irin halaccin da Umar Faruq yayi maka arayuwa,Faruq masoyinka ne na gaskiya,karka kuskura ka butulce masa nan gaba,Hayatu ina mai gargadinka da kakkausar murya daka guji bin son xuciya da kuma hulda da abokanan banza wanda gashi ayanxu sun kaika sun baro,dadin abin ma ka rike addini shiyasa abin yaso da dan sauki,kudin gida kuma mun yafe muku harga Allah,ubangiji Al-gafur Al-rahim ya yafe mana duka gabaki daya.... "
Babu wanda jikinsa beyi sanyi ba da kalaman Tsoho musamman ma shi Hayatun wanda yake feeling guilty sosai,duk suka amsa da "Ameen amin Baba muna godia sosai."
Ashe Mal.Rilwan ya yankawa Faruq kaza daya yasa Anty Ummi ta masa ferfesu dinsa,sai kuma tuwon masara da miyan kubewa danye wanda yasha man rago sosai,aka kawo musu,ai kuwa Faruq yayi farin ciki sosai da irin wannan karramawar da aka musu,kuma daga shi har Hayat sun sake jiki sun kwashi girki,yau itace karon farko da Hayat yaci abincin gidansu Tsoho,don koya shigo gidan aka masa tayi baci yake ba amma ayau yaci.
Bayan sun kare Faruq yacewa Tsoho zasu wuce Hotel inda ya kama musu daki sannan kuma gobe zasu wuce Minna don nan ne garinsu kuma su din 'ya'yan sarkin minna ne.
Daga Tsoho har Mal.Rilwan saida wuta ya dauke musu na wani dan wucin gadi,mamaki ne shimfide karara asaman fuskokinsu,Tsoho yace"'ya'yan sarkin minna?ashe da manyan mutane muke tare da shine bamu sani ba?sannuku Faruq ai mahaifinku sanannan mutum ne,ina da labarinsa,mutumin talakawa,mai taimako da kuma daukar kowa nasa ne,kai Hayatu ni bansan dalilin daya saka ka baro gida ba,amma kamar yadda na fada afarko bana son tonon silili,ku koyi boye sirrin gida,madallah Allah yayi muku albarqa,ina son na roqi wata 'yar alfarma idan har zan samu.... "
"Baba fadi buqatarka kawai don kafi karfin nemar alfarma awajenmu... "acewar Faruq.
Saida Tsoho ya fesar da wata iska daga bakinsa kafin yace"Idan babu wata matsala ko ince takura,idan komai ya daidaita zanso na baiwa Hayatudden auren 'yar wajena wato *'MARYAM SANI FALALU'* 'yar autata.... "
Dif! Wuta ya daukewa Hayat,sai bin tsohon yake da kallon mamaki don bai taba tunanin jin hakan daga gareshi ba,Faruq kuwa ba karamin dadi zancen ta masa ba,haka ma Rilwan,cike da farin ciki Faruq yace"Allah sarki Baba wannan babbar kyauta haka?baka duba cewa Hayatu ba mutumin kwarai bane ka dauki nutsastsiyar yarinya zaka bashi,toh mun karbi wannan tsadaddiyar kyautar,Allah ya saka da alheri. "
Tsoho yace"Ai d'a na kowa ne,idan ka guji dan wani ko kayi tir! da halayyarsa ai bakasan ya rayuwar naka dan zai kasance nan gaba ba,kuma ni na yaba da hankalin 'Hayatu ne shiyasa naji shaawar bashi 'yata Maryam,ga kuma addinin daya rike,nidai shawarata agareshi ko kuma nace addu'ata agareshi shine Allah yasa yabar shaye-shaye da kuma bin son xuciya... "
"Nagode sosai Tsoho da wannan kyauta,insha Allah idan na koma gida bada jimawa ba Zan turo magabatana ayi maganar aure." haka sukaji Hayat ya fada wanda hakan kuwa ba karamin baiwa Faruq mamaki yayi ba.
"Masha Allah" shine abinda Tsoho ya fada,daga haka Mal.Rilwan ya rufe taron da addu'a,Hayat ya damkawa Mal.Rilwan makullin gida tare dace masa kayan ciki arabawa almajirai.Aka daukowa Faruq jakarsa,Ummi Aysha ce kawai ta fito sukayi sallama,sai kuma 'ya'yanta amma ita uwar gayyar wato Maryam tuni har tayi bacci abinta.Har can Titi su Tsoho suka rako su Faruq.
Bayan tafiyarsu Faruq ya dubi Hayat yace"Kai nifa bazan iya tafiya da mahaukaci ba don haka ka nuna mana shagon aski muje kayi donna tabbata basu tashi ba... "
Hayat ya shaka wannan cin fuskar da Hayat ya masa amma ai baya data cewa tunda duk shine silar komai.Suka dunguma zuwa wani shagon aski aka kwashe sumar kansa,aka bar masa low cut,kana aka masa gyaran kasumba,ai kuwa ya fito shar! dashi,daga nan wani boutique suka shiga,Faruq ya zabo masa kaya kala daya wanda zai saka gobe.Daga haka suka nufi hotel tare da directives din Hayat don yasan hotel din sosai.
Saida Faruq ya nuna musu evidence of payment da kuma room number din da suka bashi sannan wani ya jagorancesu zuwa dakin.Wanka Faruq ya soma yi kafin ya latso Hajiyarsa wacce ya tarar da missed calls dinta da yawa dana spanzy.Bayan sun gaisa yayi mata bayanin komai,tayi murna ba kadan ba har tace abata Hayat din suyi magana,shi kuwa Hayat kunyarta yakeji sosai shiyasa yaki karba.
Bayan sun gama waya ya kira Spanzy ya sanar dashi komai tare da yi masa godia,daga haka kuma ya kashe wayar,yaso kiran Habib Albinsa amma kuma bayason yayi waya da ita agaban Hayat.Basuyi ordering komai ba don akoshe suke,its exactly 15mins to 12am.Faruq ya nemi lafiyar gado,nan da nan kuwa bacci yayi awon gaba dashi.
Shi kuwa Hayat yadda yaga rana haka kuma yaga dare,kwana yayi yana ibada da kuma nemar gafarar ubangiji da kuma yiwa mahaifiyarsa addu'ar samun rahamar ubangiji.
***
Washeqari misalin karfe biyar da rabi ta yamma suka iso garin Minna,Faruq ya kira Hajiyarsa yace ah turo musu direba,ai kuwa babu bata lokaci direba yaje ya daukosu,suna sakkowa acikin mota,cike da mamaki dogarawa suka soma bin Hayat da kallo don basu taba tunanin cewa fitar da Faruq yayi yaje nemo Hayatun ne ba.
Sai zubewa ake akasa ana cewa"Barka da dawowa Yarima karami,muna farin ciki da dawowarka..... "
Bebi ta tankasu ba ya nufi Haj.Babba wacce take can tsaye sai washe haqora take tana jiran ya karaso inda take,ta jagoranceshi xuwa turakar mai martaba........
_*ĸaѕн! ѕorry gυyѕ alĸalaмιn rυвυтυna ne ya ĸare don нaĸa ѕaιna ѕιye wanι*_
_*тoн ya ĸυĸe ganιn нadυwar нayaт da мaι мarтaвa zaι ĸaѕance?*_
_*нayaт ya dawo wнaт neхт now?*_
_*#тeaмнayaт# ĸυ ғιтo ayι ѕнarнι*_
*тaĸυ ce*
*ⓗⓐⓕⓝⓐⓝ💕*
Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top