Թɑցҽ 11


      ❄️❄️❄️❄️❄️❄️
        *Ḧ̤Ï̤B̤̈B̤̈Ä̤T̤̈Ṳ̈L̤̈L̤̈Ä̤Ḧ̤*
           ❄️❄️❄️❄️❄️❄️

        *°•(ĸyaυтa daga Aℓℓαн)•°*
  
      *°ιиιqυιту,ємραтну,нυмιℓιαтισи & яσмαитι¢ ℓσνє💑°*

     *MALLAKAR:HAFSAT HAFNAN💕*

      *WATPADD:HAFNANCY*

_*°wannan page dιn мallaĸιnĸυ ne нιввaтυllaн ғanѕ groυp,janaғ ғanѕ groυp,yarιмa ѕυнaιl ғanѕ groυp & ιnтellιgenт wrιтer'ѕ ғanѕ groυp,нaqιqa coммenтѕ dιnĸυ yana ѕυмar danι,ιna ѕon ĸυ ѕanι cewar нaғnan тana мυĸυ тѕaғтaтaccιyar ѕoyayya,acιgaвa da gaѕнι ѕυya ѕaι ranar ѕallaн😉•°*_

  *°•ιnтellιgenт wrιтerѕ aѕѕo🖊•°*
____________________________________

                           💥

       *Թɑցҽ 1⃣1⃣*

Acan dakin horo kuwa,tuni aka isar da saƙon xuwar prince Hayat,akacewa malamin horo cewar ga Yarima Karami nan tafe ai ga laifin da mai martaba ya kamashi dumu-dumu yana aikatawa,malamin horo wato Idrisu duk yaji jikinsa ba dadi don tabbas Hayat mutuminsa ne,sosai suke dasawa da juna.Babu yadda ya iya illa mik'ewa ya dauki dorinarsa kakkaura mai baki biyu,ya shiga gyarata kafin zuwansa,don hukunci ya zama dole,don ma wai yana d'an sarki kenan shiyasa aka dan masa sassauci,wannan hukuncin da mai martaba m.k ya sanya ayiwa Hayat ba karamin dadi yayiwa mutane da yawa ba,don hakan da yayi shine daidai,ya kwatanta adalci,ya nunawa duniya cewa sam baya da son kai ko kadan,baiyi tunanin cewar ai Hayat dansa ne ba don haka bazai hukuntashi bisa laifin daya aikata ba,a'ah ya kwatanta adalci anan.

    Mamman dogari shine gaba gaba,ayayin da sauran hudun ke rik'e da Hayat,shifa Mamman sosai abin ke masa dadi,ji yake tamkar ya xuba ruwa ak'asa yasha don murnar ganin za'a hukunta Hayat (Kunsan haka abin yake,kowa zaka ga da wanda jininsa ya hadu da,haka zalika akwai wanda jininsa bai hadu dana wani ba,toh hakan take ga Prince Hayat da kuma Mamman dogari.)

  Suna shiga cikin dakin Jabir ya nufi Idrisu wanda ke tsaye yake jiran isowar Hayat.Sauran dogarawan kuwa ahankali suka zaunar da Hayat ak'asa wanda sai faman basu haquri yake tayi akan kada su bugeshi,abin dai gwanin ban tausayi.

    Jabir ne ya danyiwa sauran dogarawan clapping 👏 sau biyu,duk suka dubi inda yake ah kusa da Idrisu,yace"Duk ku matso kusa.... "

Da hanxari suka isa gareshi don shine oganninsu gabaki daya,He has the final saying kuma dolene subi duk abinda yace,idan har ya kafa wata doka toh kuwa babu dogarin dake tsallakewa koda kuwa kana jin kai din wani shegen ne irinsu Mamman tofa dole ka lafar don Jabir ko kadan baya daukar ƙaniya.

     Yace"Meh zai hana mu hade kawunanmu mu taimaki Yarima Karami?kowa anan yasan Yarima karima dai mutumin kirki ne kuma sosai yake k'yautata mu'amalarsa da mutane kamar dai mahaifinsa,shidai  abarshi da saurin fushi,mugun zuciyar tsiya wanda har hakan ke sanya ko kadan bashi da yafiya idan aka masa wani abin da ransa bai so ba,amma apart from dat,sam sam Yarima Karami bashi da matsala,kowa nasa ne,don haka abinda nakeso daku shine,kar abugeshi,mu dan bada lokaci sai awuce dashi Fada,sai yayi acting kamar an bugeshin,koya kuka ce?"

   Kowannensu ya gyad'a kai har Idrisu mai horo alamun amincewa,Cike da rashin jindadi Mamman yace"Amma dai kunsan Mai martaba yana iya gane cewar ba'a dakeshi bako?don haka nidai babu ruwana,haba ko bulala goma ne dai ayi masa gudun shiga cikin matsala..... "

Axuciye Jabir yace"Wato kai Mamman na lura kai hassadarka mai lasisi ne akan Yarima Karami,sannan kuma hassadarka bama akansa kadai ta tsaya ba,akan kowa take,toh bari kaji babu wanda zai dakesa acikinmu,idan kuma kai zakayi bismillah ina kallonka,idan kuma a'ah kai ƙararmu zakayi,toh shima bismillah kayi sauri kaje kafin iska ta rigaka... "

   Bai ce kala ba illa gungunin da yake tayi,da sauri Jabir ya matsa kusa dashi yace"Dan uwarka idan ba tsoro ba fada inji in ban k'akkarya banza anan gun ba... "
  
      "Master ayi masa haquri... " haka sauran suka fada,shi kuwa Hayat sai binsu yake da kallo cike da qaunar Jabir aransa.Jabir ya sanya wani dogari tsayawa abakin kofa sabida at anytime Mai martaba yana iya zuwa.Kai Jabir akwai wayau,samun wani abu sukayi wanda ni kaina bansan ko menene ba,kasa kasa ne kuma dan jaja amma ba ja can sosai ba,suka goggogawa Hayat ajikinsa,dake shi din farin mutum ne,sai nan da nan fatarsa ta canza Kala,kai kace ko da gaske bugunsa din akayi.Kowa sai yabawa aikin Jabir yake banda Mamman wanda yayi fuska kamar na shanu😀.

   Hayat ya fashe da kuka tare da kamo hannun Jabir,yace"Jabir thank u so much,haqiqa kai din mutumin kirki ne kuma ka cika masoyina na gaske,yadda kuka taimakeni dinnan kuma ina muku addu'ar samun taimako mafiyin nawa wataran,ubangiji Allah ya saka muku da mafificin alherinsa.

Dan muskutawa Jabir yayi kana yace"Allah ya taimaki Yarima karami ai ka cancanci ataimaka makan ne,shawararmu dai agareka yanzu shine don Allah ka dawo kan hanya,zunubi babba ne kake kokarin daurawa akanka sannan kuma kana kokarin b'atawa mahaifinka da kuma wannan masarautar suna,don Allah kabar shaye-shaye,buga chacha da kuma bin abokan banza,duk nan munsan abinda ke damunka kuma insha Allah zamu tayaka da du'a'i don mahaifinka mutum ne mai tsassauran ra'ayi,idan yace 'A' toh baka isa kace 'B' ba,kayi kokari ka karbi kaddararka ayadda tazo maka kuma na tabbata nan gaba zakaci ribar haquri,kazamar rayuwar daka jefa kanka ciki ya sanya ka zamo tamkar ragon namiji sabida ka kasa yin tawakkali,har ka biyewa rudin abokanan banza,don Allah abokina ka dawo kan hanya kaji ko?"

   Murmushi Hayat yayi yace"Nagode Jabir insha Allahu daga yau nabar shaye shaye da kuma bin abokanan banza... "

Jabir ya sake duƙawa yace"Alhamdulillahi naji dadin hakan,My little prince ka mana afuwa zamu maka askin kai don wannan ya zama dole ayishi... "

    "Ba damuwa... " Nan da nan kwalla ya sake taruwa acikin ramin idon Hayat don arayuwarsa ya tsani ƙwaryar molo😀,amma toh yaya ya iya?

Haka yana ji kuma yana gani akai masa correct tantali😂,bayan an gama Jabir yace"My little prince yanzu sai kayi acting kamar wanda yasha bugun tsiya har xuwa fada.... " Jabir ya mik'e ya soma tafiya yana dan d'ingisawa da kuma babbanƙaro baya tamkar wanda dai aka dakan.

    Sauran suka fashe da dariya,Idrisu yace"Dakyau Yarima Karami,agaskia zaka fa iya yin wasar ƙwaiƙwayo,jinjina mai tarin yawa gareka jarumin jarumai.... " (Jarumin dake tsoron bulala?😂).

Jabir ne yaje ya soma dubawa ko babu kowa acikin fadar don baya son gimbiyoyi da kuma baƙin Mai martaba susan abinda ake ciki,yana zuwa kuwa ya tarar da Haj.Babba aciki suna fira da mai martaba,gaban mai martaba ne ya fadi na ganin Jabir don atunaninsa tare suke da Hayatun.Gaisar dasu kawai yayi kana ya juya ya fice,mai martaba hadda sauke ajiyar xuciya ganin ba'a taho da Hayatun ba.

   Haj.Babba ta mik'e tace"Ranka shi dade ni na shige ciki bacci nakeji,yau kwata-kwata ban sanya d'ana Hayat ah ido ba,don Allah idan ya shigo yazo ina nemansa."

Murmushi kawai Mai martaba yayi tare da d'aga mata kai alamun yaji,ta fice abinta,Jabir nanan tsaye hatta zo ta wuceshi,sai daya tabbatar da ta shige turakarta kana ya wuce da gudu yaje ya taho da Hayat xuwa Fada.

   Mai martaba na had'a idanuwa dashi yayi saurin k'awar da kansa gefe tare da runtse idanuwansa,ko kadan baya son ganin yanayin Hayat don yasan kalar fatarsa tabbas ta canza,sosai tausayinsa ke dukan xuciyarsa.Shi kuwa Hayat ganin mahaifin nasa ya dauke kallonsa daga gareshi,hakan yasa ya fashe da kuka tare da rugawa aguje xuwa gareshi,zubewa yayi agabansa ya rirrik'e kafafuwansa,Jabir kuwa ficewa yayi don ya baiwa d'a da mahaifi damar ganawa dakyau.

   Yace"Abbana don Allah kayi hakuri wallahi nabar shaye shaye da kuma bin abokan banza,kuma itama Najmiy din na haqura da ita.... "

Girgiza kai Mai martaba yayi,kana yace"A'ah Hayat nifa nasan halin d'ana,duk fa abinda yace yana so toh kuwa kota halin ƙaƙa ne sai yasan yadda zaiyi ya sameshi,Hayatudden zan iya bugar k'irji ince baka haqura da Najmiy ba,kadai fada ne kawai don naji dadi,Hayatu bawai bazan iya baka auran Najmiy bane,a'ah so nake kawai na nuna maka cewar ba komai ne mutum idan ya nema kuma yake samu ba arayuwarsa,ina son na koya maka daukar haquri da kuma dangana don duk baka sansu ba."

   "Abba mai martaba da gaske nake na haqura... " ya fadi hakan tare da d'agowa yana kallon mai martaba.

Murmushi mai martaba yayi kana yace"Toh Allah yasa,maganar da kayi dazu kuma bakayi k'arya ba,ni da mahaifiyarka mun bada tamu gudummawar wajen jefa rayuwarka acikin garari,amma kuma ina son ka sani cewar hadda son xuciyarka acikin,don da'ace kayi haquri kayi tawakkali ga ubangiji toh kuwa da hakan bata faru ba,kuma nasan tabbas zakaci ribar haquri da biyayya nan gaba,amma sai ka biyewa son zuciya,ita kuma xuciyar ta biyewa rudin abokanan banza,Hayat ina baka shawara daka gyara ko don lahirarka,sannan kuma ka dauki haquri da dangana don Najmiy ta riga ta maka nisa,maza ka tashi kaje kayi wanka sannan kaje ga mahaifiyarka Haj.Babba tana nemarka. "

   Zancen Mai martaba be wani daga masa hankali ba kamar yadda yace wai Haj.Babba na nemansa,mai martaba ya lura da tashin hankalin daya shiga don haka yace"Bayan ni dasu Jabir babu wanda yasan halin da muka riskeka dazu... "

Saukar da ajiyar xuciya yayi,kana yayiwa mai martaba godia sannan ya mik'e ya fice ayayin da Mai martaba ya bishi da kallon tausayi,ahankali ya furta"Allah ya shirya abinsa... "

   _*тoн мy ғιғυl ĸυna ganιn da gaѕĸe нayaт ya нaqυra da 'yar вalaraвιyar nan ĸυwa???*_

_*ĸυdaι ĸυ вιyo🏃*_

   

      *ⓗⓐⓕⓝⓐⓝ💕*

   

 

Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top