Թɑցҽ 7

      https://mobile.facebook.com/Intelligent-Writers-Association-1194933670662901/

      *INTELLIGENT WRITER'S ASSOCIATION*
*{ we give the reader's of ours the best out of the best's,, our inks are melodious And dropping a kinda light's to reader's}*
'''THE PEN OF LOVE 😘 HEART TOUCHING ❤ TEARS OF SORROWS😭 CURDLES 😊 GIGGLES 😁 AND MARRIAGE THINGS 💑'''
*JUST GIVE US FOLLOW.....*✔

                       💥
 
        
      ❄️❄️❄️❄️❄️❄️❄️
        *Ḧ̤Ï̤B̤̈B̤̈Ä̤T̤̈Ṳ̈L̤̈L̤̈Ä̤Ḧ̤*
             ❄️❄️❄️❄️❄️❄️❄️

      *❄️(ĸyaυтa daga Aℓℓαн)❄️*

  **ιиιqυιту,ємραтну,нυмιℓιαтισи & яσмαитι¢ ℓσνє💑**

  *MALLAKAR:HAFSAT HAFNAN💕*

        *WATTPAD:HAFNANCY*

*°ՏɑժɑմƘɑɾաɑ ցɑ Dr.υмαя fαяυq вαнαgσ,ємιя σf иιgєя ѕтαтє,мιииα°*
__________________________________

    _*°•wannan ѕнaғιn naĸυ ne мoмy zιl,υммυl мeenal da ĸυмa мaмan ĸнaυѕar,ιna ѕo ĸυ ѕanι cewar нaғnan тana мυĸυ ѕo мaι cιĸe da dυмвιn qaυna❤•°*_

             💥

   *Թɑցҽ 7*
Faruq bai saurarawa Hayat ba har saida ya sadasu da dakin baccinsu,suna shiga ya jefar dashi ayayin da shi kuma ya juya ya sanyawa kofar dakin nasu key.shi kuwa Hayat tangal tangal yayi zai fadi,toh dayake shi din jarumin jarumai ne,sai yayi kokari ya rike kansa.

    Ya juya yana duban wan nasa xuciyarsa na tafarfasa kamar danyar ganda,yace"Wai Yayah prince meye hakan?what's the meaning of all diz bullshits?wani laifi nayi da har yakai girman wannan cin fuskar daka min?iyyeh tambayarka nake...... "

Ji kake tassss! Faruq ya kwasheshi da wani wawan mari wanda har saida yaga wasu shining stars⭐ na blinking.

      "Kayi gaggawan kiyaye harshenka da irin kalaman rainin da kake jifana dasu,that slap was simply a reminder to tell you dat am ur elder one and not ur junior neither ur mate...... "

Murmushi Hayat yayi tare da shafa fuskarsa inda aka watsa masa marin,yace"Wow rana ta farko da Yayah prince ya taba daga hannu ya mari k'aninsa wanda yafi so duk duniya,ban san dalilin wannan rashin mutuncin da kake shirga min ba amma kuma bai kamata hakan takai ga mari ba,anyway am grateful buh seriously the slap was kinda hot Prince Faruq Bahago...... "
 
   Ya sakar masa wani killer smile amma axuciyarsa shi kadai yasan irin takaicin dake cinsa.Shi kuwa Faruq jikinsa ne yayi sanyi qalau,meyasa yayi hakan?meyasa zai daga hannu ya mari dan'uwansa akan abinda bai tabbatar ba?

Kallon kwayar idanuwan Hayat yayi daya tsura masa ido yana jifarsa da kallo mai cike da ma'anoni iri iri.Duk da hakan kuma yana iya hango true 'love & affection' kwance cikin k'wayar idanuwan Hayatun wanda babu tantama it's for Najmiy Gaddafi.

      "Meye dalilinka na rik'ewa Najmiy hijab dazu sannan kuma meye ka fada mata wanda har ya sanya ta fincike hijabinta tayi cikin gida da gudu?"

Wani irin malalacin dariya ya fashe dashi wanda yafi kuka ciwo,yama maida Faruq wawa wanda hakan ya sake fusata Faruq din.
    "stop laughing like a mad man and answer my question....... "

Wayyo!haqiqa kalmar 'mad man' yayi nasarar soya xuciyar Hayat,amma baice komai ba illa tamke fuska da yayi kamar ba wanda shine ya gama k'yak'yatar dariyar ban haushi ba.

     Yace"Ohh! now I see,was dat the reason why you treated me like a coward in the presence of those servants out there?well na fada tarkon so ne,prince Hayatudden freaking m.k Bahago is inlove with Princess auta Najmiyya Gaddafi.... "
Ya fadi hakan ne with full confidence babu alamun tsoro atattare dashi.

    "Shut the hell up! Hayatudden Bahago,ain't you ashame of urself?kai baka ji kunya ba?yarinya kankanuwa kamar Najmiy wacce ko gama sanin kanta batayi ba itace kake furtawa kalmar so?ta gane meh acikin soyayyar?look,tun ba yau ba na dade da gano take-takenka akanta ta hanyar shisshige mata da kake yawan yi which is earnestly out of bound,amma naki amincewa da zargin da xuciyata take akanka agame da hakan,nace kila kawai ba sonta kake ba,shaquwace kawai ta yan'uwantaka,amma ayau zargina akanka ya tabbata gaskiya,ni ban hanaka sonta ba amma meyasa baka bari harsai ta dan kara girma da wayau ba kafin ka furta mata wannan kalmar?kai infact! Kai dinma har guda nawa kake da harka soma tunanin soyayya in banda iskanci irinta 'ya'yan zamani?You are juz 22 fa Hayat?ko ni da nake da shekaru 24 wallahi yan mata ma basa gabana for now,burina ayanzu na samu na kammala karatuna lafiya qalau,naje service dina,na kuma samu aikin yi kafin na nemi matar aure,donni wlhy babu ruwana da wata yarinya ayanzu tazo ta yaudareni ko ni kuma na yaudareta,arabu ana dibar albarkar juna.......... "

      Hayat ya tari numfashinsa"Wannan kuma kai kakesowa kanka wannan tsarin,da kake jifana da maganganu,toh ni din ba dan'iska bane da nake shirin lalatata ba,nadai furta mata ne don tasan da zamana amatsayin mai sonta kafin wani yayi min shigar sauri harya sami wani gurbi acikin xuciyarta............... "

    "Rufemin dirty mouth dinka anan,idan har da gaske din sonta kake tsakaninka da Allah toh ai kamata yayi ka sami Abba mai martaba wanda shine uban rikonta kace masa _*KA GANI KUMA KANA SO*_,don haka amaka kamun kafanta,amma furta mata kai tsaye da kayi sam bai dace ba,kai look daga yau sai yau,ina son ka fita aharkarta kabar yarinya ta maida hankali kan karatu,karka sake ka raba mata hankali gida biyu........ "

    Azuciye Hayat yace"Ban gane yaren wai in fita harkarta ba,ni da qanwata kuma shine ake kokarin yimin iyaka da ita?"

"Toh ai gani nayi kamar baka dauketa kamar qanwartaka ba,tunda har zaka iya tsayawa ka kalli cikin kwayar idanuwanta sannan ka furta mata kalmar 'so' awannan yan kankantar shekarun nata,In banda girman jiki ma da Najmiy take dashi ai tsarar Hidaya ce,Hidayar ma ai tama dan girmeta,don dai kawai ita bata girma ne shiyasa ake ganin kamar Najmiy ce babba,yanzu idan wani yayiwa Hidaya hakan zakaji dadi?I am very pretty sure dat saika kusan ganin bayansa......... "

     "Yayah Prince kalamanka suna nemar wuce limit dinsu..... "

Da sauri Faruq yace"Amma hannuna yafisu sauri..... "😂 (Hayat kabi ahankali kada Faruq din sahiba ya mazgeka anan😁)

     Murmushi Hayat yayi kana yace"Kada ka kuskura ka kaini bango.... "

"Inma na kaika zaka dawo da baya da kanka ne,na dai gaya maka ka fitar ahanyar Najmiy,karka batawa yarinya rayuwa,Najmiy amanar Allah ce agaremu,karka kuskura ka yaudareta da soyayyar k'aryarka Hayatu,ina baka shawara ne don wallahi hannuna yafi kalamaina saurin aiki,na barka lafiya Yarima karami..... "

   Ya juya ya bude kofa yasa kai ya fice fuuuu! Kamar kububuwa,Hayat kuwa wani dunkulen bakin ciki ne ya tokare masa qahon xuciya,meya shiga cikin kwakwalwar dan'uwan nasa ne da har yake jifarsa da zazzafar kalamai haka?Ayau shi Faruq ke yiwa kallon dan'iska kuma mayaudari?har yake ce masa kada ya kuskura ya b'ata rayuwar yarinya?

Tuni hawayen bakin ciki suka soma shatato masa saman kunci don shi harga Allah ne yake son Najmiyya Gaddafi,sonta har cikin jinin jikinsa yake jinsa,shi kawai yayi saurin fad'a mata ne sabida kada wani can daban ya dauke mata hankali.zubewa yayi saman wata two seater tare da dafe kansa da hannayensa bibbiyu,yama rasa tantance abinda ke masa dadi acikin duniyarsa.

   ****
Faruq kuwa yana fita fadar mai martaba ya nufa zuciyarsa ah dagule,yana shiga kuwa ya tarar babu kowa acikin fadar sai dogarai biyu da kuma mai martaba wanda ke hakimce kan kujerar sarautarsa.

   Samun wuri yayi ya zauna tare da rike Kansa da hannayensa bibbiyu,hankalin mai martaba ne ya daga ganin yanayin dan nasa wanda kana gani kasan yana cikin damuwa ne.
   Ahankali yace"Umari meya faru na ganka cikin damuwa?wani abin aka maka acikin gidan?

Dakyar ya iya cewa"A'ah babu abinda aka min" ya fada ba tare da ya kalli inda mai martaba yake ba.

   Murmushi mai martaba yayi kana yace"A'ah Faruq ba haka yanayin d'an nawa yake ba,duk da cewar kai din miskili ne amma kana da faram-faram da mutane,yanxu Umari ashe har akwai ranar da zatazo da har zaka iya boyemin damuwarka ka barwa cikinka kai daya?iyyeh Umari tambayarka nake?"

   Ahankali ya furta"A'ah Abba mai martaba ka gafarceni..... ",Faruq ya dubisu Jabir(dogari)yace"Ku dan bamu wuri jabir zamuyi magana."

Zubewa sukai akasa sukace"Allah ya taimaki Yarima mai jiran gado,agama lafiya..... " suka fice,asannan ne ya juyo ga mahaifin nasa ya kora masa bayani.

Jikin mai martaba ne yayi sanyi qalau,kuma haqiqa zancen yayi mugun girgizashi,duk da cewar shi karan kansa ya dade yana zargin Hayat akan cewar kamar son Najmiy yake sabida irin muguwar sabon da sukayi,amma still bai taba tsammanin cewar irin wannan ranar zata zo ba,shifa tun zuwan Najmiy gidan ya kudurta aransa cewar insha Allahu Faruq zai baiwa aurenta don ya tabbatar da cewar zai rike masa amanarta kuma bazai taba barinta tayi kukan maraici dede da minti daya ba,don Faruq mutum ne mai sanyi hali,haquri da kuma tausayi,uwa-uba kyautatawa,sab'anin Hayat yana da zafi sosai kuma ga saurin fushi,sam bashi da haquri kamar zawo yake,tun yana karaminsa ya taso da wani irin mugun hali,idan har ka masa wani abinda ransa baiso ba toh kuwa saiya rama,haka kuma idan har yana son abu toh kuwa kota halin ƙaƙa ne saiya sameshi,ahalin yanzu kuwa rikici babba ne ke shirin kunno kai cikin royal family din don agaskiya mai martaba baya jin zai iya baiwa Hayat auren Najmiy sabida ko kadan basu dace ba,Najmiy zata cutu sosai idan ta auri Hayat,yana hango mata kukan maraicin da zata sha bayan ta aureshi,shi kuma bazai taba so hakan ta faru ba don Najmiy amanar Allah ce agaresu shiyasa yakeson aurar da ita ga nagartaccen namiji wanda zai kula da ita kamar Faruq.

    Daga murya yayi ya kira sunan Jabir,nan da nan kuwa sai gashi ya iso ya zube akasa"Allah yaja da ran mutumin talakawa gani gareka ya shugabana......  "

      "Maza kuje ku taho min da Yarima Karami,ace masa ina nemansa da gaggawa yanxun nan kuwa..... "

"An gama ranka shi dade...... " ya Mike ya fice don isar da sakon mai martaba.

    _*Tofa my fiful yau ake yinta,wayyo Hayat😭 wallahi harna tausaya maka*_

    *ⓗⓐⓕⓝⓐⓝ💕*

Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top