Թɑցҽ 13

      ❄️❄️❄️❄️❄️❄️
        *Ḧ̤Ï̤B̤̈B̤̈Ä̤T̤̈Ṳ̈L̤̈L̤̈Ä̤Ḧ̤*
           ❄️❄️❄️❄️❄️❄️

        *°•(ĸyaυтa daga Aℓℓαн)•°*

*°ιиιqυιту,ємραтну,нυмιℓιαтισи & яσмαитι¢ ℓσνє💑°*

  *MALLAKAR:HAFSAT HAFNAN💕*

      *WATTPAD:HAFNANCY*

*•°ѕadaυĸarwa ga Dr.υмαя fαяυq вαнαgσ,ємιя σf иιgєя ѕтαтє,мιииα•°*

_*°•don Aℓℓαн ιna ѕon ĸυ ғaнιмcι dalιlιna na rυвυтa wannan laвarιn,вawaι nayιѕнι don ajι dadιnѕa ne вa ĸawaι,ĸaмar yadda naga waѕυ нar ѕυn ѕoмa мιn ĸoraғι ĸan ya ĸaмaтa na ѕaѕѕaυтawa rayυwar нayaт,don Allaн ĸυ daιna вanaѕo,nιna тѕaro laвarιna don ιna ѕon ne na ιѕar da waтa мυнιммιyar ѕaĸo хυwa gareĸυ,ѕo naĸe ĸυ тѕιncι darυѕѕa da yawa acιĸιn rayυwar wa'ennan вayιn Allaнn мυѕaммan мa нιввaтυllaн wacce don ιтa мa nayι wannan lιттaғιn,тa ĸυѕan ѕнιgowa cιĸιn laвarιn nan вada jιмawa вa,ιdan ĸυwa ĸυĸace ѕaι anyι yadda ĸυĸeѕo,тoн ĸυwa вazaĸυ вanι daмar ιѕar da aвιnda naĸeѕon ιѕarwa вa,don нaĸa ιnaѕon don Allah ĸυ вanι нadιn ĸaι ĸυмa ιna ѕonĸυ dυĸa мy ғanѕ,ιna godιa da coммenтѕ dιnĸυ•°*_

_*•••wannan ѕнaғιn мallaĸιnĸι ne ĸe daya мy вlood ѕιѕ anтιna ѕaιnaн,ιnaѕo ĸι ѕanι cewar qaυnarĸι araιna ya wυce yadda ĸιĸe zaтo da ĸυмa тѕaммanι,ѕaιnaн нaғnan dιnĸι тana мιĸι тrυe love вaвυ yaυdara acιĸι❤️💕°°°*_

   

  *°•ιnтellιgenт wrιтerѕ aѕѕo✍•°*
______________________________

                     💥

     *Թɑցҽ 1⃣3⃣*

  "Hajiyata yanxu shikenan Haj.Karama ta tafi ta barmu da ƙewarta kenan?yanxu shikenan bazamu sake ganinta har abada ba kenan?lallai yau na ƙara tabbatar da cewar ita duniya makarantace,kamar yadda ka shigo cikinta,tofa haka watarana zaka barta,acan kuma zaka soma wata rayuwa kai kadai ah inda ayyukanka na alkhairi ne kadai kawai zasu iya tseratar dakai daga azabar Allah, _*'RAYUWAR KABARI KENAN'*_ ..... "

   Fashewa da wani irin kuka yayi mai ban tausayi,kana ya cigaba"Hajiyata wallahi babu abinda yake sakani cikin tsananin firgici da kuma tsoro face inna tuna da zango-zango na tashin ƙiyama,Bahasi na farko shine *'MUTUWA DA KUMA TSANANINTA'*,mutuwa itace masauƙin farko na isa ga ƙiyama,sannan kuma zangon farko ta tayarwar lahira,manzon Allah (S.A.W) yana cewa *"mutuwa ƙofa ce ta lahira,haka kuma mutuwa ƙiyama ce,idan dayanku ya mutu tofa ƙiyamarsa ta tashi,Inda anan ne zaiga sakamakonsa na ayyukan daya aikata asanda yake duniya,wato khairan ko kuwa sharran..."*

  Bahasi na biyu shine, *'BARZAHU DA KUMA AZABAR DAKE CIKINTA'*,wato ita dai barzahu wata duniyace dake tsakanin mutuwa da kuma ƙiyama,ana ni'imta mamacine idan yazo ne da ayyukansa na alheri,ko kuwa ah azabtar dashi idan har yazo ne da munanan ayyuka,za'a cigaba ne da azabtar dashi har xuwa gobe ƙiyama."

Bahasi na uku shine *'SHARUDDAN ƙiyama'* ,wannan kuma alamomi ne dake nuni da samuwar Aljannah ko kuma wuta.."

   Bahasi na hudu shine *'ABUBUWAN DA ZASU FARU RANAR ƙIYAMA'*,Ranar tayarwa kenan,ranar da halittu zasu tsaya gaban ubangiji don hisabi. "

      Bahasin ƙarshe shine *'YAN ALJANNAH DA YAN WUTA'* wato anan ne zakasan makomarka,wato wuta ko aljannah?"

Sake rushewa yayi da wani sabon kuka yace"Toh meh zaisa mu 'yan adam mu dauki duniya da zafi?itafa gidan wuta da kudinka zaka siyeta,sabida chachar nan idan zaka bugata tofa tabbas zaika biya kudi,haka ma giya da sauran kayan maye idan zaka shasu suma tabbas saika biya kudi,kwanciya ma idan zakayi da karuwa(Zina) shima saika biyata kudi,da sauransu dai,amma itafa aljannah k'yauta za'a baka ita,zakayi sallah k'yauta babu ko sisinka da za'a k'arba,haka ma azumi k'yauta zakayi,da sauransu dai,toh fisabilillahi! Meh zaisa muyi wasa da damar da Allah ya bamu?"

         "Iyaye!iyaye!!iyaye!!! Manzon Allah da kansa ya k'ira sunayen iyaye sau uku kafin yace *"Iyayenku suna da matukar muhimmanci arayuwarku musamman kai d'a namiji,iyayenka sune hanyar samun aljannarka idan harka k'yautata musu kenan,samun aljannar ma dakyau yana tafin kafar mahaifiyarka ne,in taso ta daga ka samu,in taki kuma shikenan... "

Ya k'arashe zancensa da"Why Hayatu?meyasa ka biyewa son xuciya da kuma rudin abokanan banza har suka kaika suka baro?ta sanadiyyarka mahaifiyarka ta rasu adalilin rashin haqurinka da Kuma daukar dangana,uwa fa ba'a bar wasa bace..... "

   Cikin muryar kuka Haj.Babba ta katseshi"A'ah Faruq dena fadin hakan?ko kadan karka ga laifin Hayat acikin wannan al'amarin,a'ah lokacin Maymunerh ne yayi shiyasa ta amsa k'iran mahaliccinta,Kuma muna fatar Allah yakai rahama kabarinta,Maymunerh Allah yasa kinje asa'a,Maymunerh ubangiji Allah ya gafarta miki kurakurenki duka,na yafe miki duk wani laifi da kika min,da wanda na sani da wanda ban sani ba,duk na hada na yafe miki duk da cewar ni dai baki taba min komai ba,amma ance zaman tare dole watarana za'a dan samu 'yar sab'ani,amma wallahi harga Allah ni Hadizatouh na yafe miki...... "

   Kuka yaci k'arfinta,babu wanda kalamanta bai shigesa ba da har ya sanyasu kuka,Hidaya,Abida,Najmiy da kuma Faruq din duk kuka sukeyi mai tab'a xuciya.

Mai martaba wanda ya dade abakin kofar dakin tsaye yana sauraronsu ne ya shigo ciki,idanuwansa sunyi jawur dasu,sun kankace sabida kukan dayasha,yace"Hadizatouh sam Umari beyi k'arya ba,ta sandiyyar Hayatu maymunerh tabar duniya,kuma insha Allahu kamar yadda yasanya muka xubar da hawaye akansa toh kuwa........ "

   Da hanzari Faruq ya isa gareshi tare da sanya hannu ya rufe masa baki,alokaci daya kuma ya shiga girgiza masa Kai"A'ah Abba mai martaba don Allah na rokeka kar zuciya ta sanya ka tsinewa d'anka don hakan zai iya karasa tab'arb'arewar rayuwarsa,na rokeka Abbana karka debewa Hayatu albarqarka.... "

    Zubewa yayi akasa gami da rirrike masa kafafuwa yace"Abba Mai martaba ina rokarwa Hayat wata alfarma,ba donni ba,ba kuma donna isa ba,amma don Allah zakayi,ina son ayau ka sanyawa rayuwar Hayatudden albarqa aduk inda yake afadin duniyar nan..... "

Haj.Babba ma dasu Abida duk suka taso suka zube agabansa suna rokonsa,Mai martaba kuwa rintse idanuwansa yayi jin yadda xuciyarsa ke aikin soyuwa,can ya budesu,fes ya sauke kallonsa akansu,murmushin takaici yayi kana yace"wani albarka ne kuma yayi saura da zan sanyawa Hayatu?ai ina aza ko yana da wasu iyayen ne can wa'enda suka fimu shiyasa ya gujemu?kuyi haquri amma wannan bakin nawa bazai iya furta kalmar 'Albarka' akan Hayatu ba,ni nama riga da na cireshi acikin 'ya'yana,na sallamawa duniya shi......."

   Cike da tashin hankali Faruq ya mik'e yana kuka,yace"No!No!No!! Abba Mai martaba don't say dat,don Allah na rokeka karka tsinewa dan'uwana,Abba mai martaba idan bazaka iya sanya masa albarqa ba,toh idan ana iya debewa akan wani d'an,toh inason ka kwashe nawa idan yaso shi azuba masa,ni kuma atsine min.... " agigice Faruq ke fadin wannan maganar😢

   Da sauri Najmiy ta mik'e ta rufe masa baki,tace"No Yayah prince Babba daina fadin hakan,babu wanda za'a tsinewa acikinku saima dumbin albarkarsa da zaku samu...... "

Zubewa ta sakeyi akasa ta shiga rokan Mai martaba,shi kuwa Faruq hannu yakai yana taba bakinsa inda tafin hannunta ya taba,lumshe idanuwa yayi yana mai jin wani sabon al'amarin da bai taba ji ba yana shigar xuciyarsa,wato *'SHAUKIN SO'*

     "Najmiy naji ya isa amma da sharadi idan har kun yadda.... " haka suka ji mai martaba ya fada cikin wata kakkausar murya.Babu wanda baiji gabansa ya fadi agame da hakan ba.

Dakyar Hayat yace"Wani sharadi kenan Abba mai martaba?"

  With full confidence yace"Idan an gama zaman makoki zan daura auran *'NAJMIYYA GADDAFI'* da kuma *'YARIMA UMAR FARUQ BAHAGO'* "

    Gabaki daya dakin yayi tsit kamar babu wasu halittun dake ciki,gaban kowa sai harbawa yake da sauri da sauri musamman ga wa'enda abin ya shafa,wato 'Faruq' da kuma 'Najmiy'.

     "Ya naji duk kunyi shiru?idan kuma baku yadda ba shikenan bazan sanyawa Hayatun albarka ba... " acewar mai martaba.Har ya juya zai fita,da sauri Faruq ya riko rigarsa yace"A'ah Abba mai martaba don Allah karka tafi wallahi duk mun amince,zamu maka biyayya idan har hakan ne zaisa ka sanyawa dan'uwana albarqa.... "

Mai martaba yace ba tare da ya juyo ba"Dakyau Umar Faruq,kefa Najmiy yaya kin amince ko kuwa a'ah?"

   Kafeta da idanuwa Faruq yayi,ai kuwa anci sa'a itama shi din take kallo,signal yayi mata alamun itama tace ta amince.Da sauri tace"Abba mai martaba harni na isa naja da hukuncin da mahaifina ya yanke akaina?akullum fatarmu shine mu wanye daku lafiya kuna masu alfahari da kuma shi mana albarka,don haka ni Najmiyya nayi na'am da zab'inka na auren Yarima umar Faruq.."

   Murmushin jindadi Mai martaba yayi tare da juyowa yana fuskantarsu,yace"Alhamdulillah! Najmiy ina godia kwarai da gaske da daukata da kikayi tamkar wanda ya haifeki,kaima Faruq ayau ka nuna min cewar lallai na haifa,kuma na isa na bada umarni har abi,sannan kuma ka nuna min cewar na isa na zartar da hukunci har ah amsheshi da hannu bibbiyu ba tare da anmin korafi ba,nagode kwarai da gaske Umaru da biyayyarka agareni kuma ina rokan Allah kaima ya baka 'ya'yan da zasu maka hakan daga kai har Najmiy,kuma yanxu zan muku abinda kukeso... "

   Hawaye na gangarowa saman kuncinsa yace _*"d'ana Hayatudden ubangiji Allah yayiwa rayuwarka albarqa aduk inda kake,Allah ya karkato da hankalinka gida ka dawo cikin zuri'arka"*_

Duk suka amsa da "Ameen Yah Allah" suna masu kuka,mai martaba yana gama fadar hakan ya juya ya fice don har xuwa yanzu suna kan karbar gaisuwar ta'aziyyar mutane ne,yau kwana bakwai da rasuwarta amma idan kaga yadda mutane keta tururun zuwa kai kace ko yau ne akayi rasuwar.

_*υp!υp υp υмar ғarυq вaнago,wallaнι ĸayι мυgυn вιrgenι awannan page dιn,ѕaмυn dan'υwa ĸaмarĸa ѕaι an тona,мaĸιyιn υмarι people lιĸe мaryaм cнυввy нope yaυ ғarυq ya ѕoмa вιrgeĸυ????*_

_*ιѕ lιĸe ĸaмar ғarυq ya ѕoмa ĸaмυwa da ѕon najмιy ĸo?wнaт???aĸwaι rιĸιcι ĸenan?нaнaнa!can'т ѕay,ĸυ daι ĸυ cιgaвa da вιвιyaтa*_

       *тaĸυ ce*

    *ⓗⓐⓕⓝⓐⓝ💕*

   

       

Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top