page 7
ABLA ADNAN
NA CHUCHUJAY.
PAID BOOK.
FREE PAGE
7.
Sallama yayi ya karaso Ya zauna ,Da wani kisisina matar tace "baby ka dawo kenan, ga matar nan tazo lets talk ina da meeting da zan attending wallahi."
Zama yayi yana mai gyaran murya kana ya maida kallan sa gan su Abla wadda tace ina kwana,
Lapia lau "barka da safiya hajiya".
"Barka mama ta faɗa kamar wadda ke cikin shock amma daga bisani sai da saita kanta.
Gyaran murya Ya kuma yi yace "kamar yarda mukayi magana dake hajiya nida matata kinga Allah ya bamu yara uku amma dukkan su matane ,muna bukatar namiji wanda likitan mu Ya tabbatar mana da akwai technology yanzu da Ya bunƙasa Wanda akwai abunda za'a bama mace tayi conceiving namiji,
Amma iyali na a yanzu bata bukatar haihuwa saboda tayi uku tagaji gashi kuma soyayyar ɗa namiji ta shigemu,hakika tsarin wadda zatayi surrogate mother din yayi mun kuma kamar yarda na faɗa maki zan bada 1.5million , " duban sa ya maida kan Abla wadda da ace kallo na kisa da tuni mamanta ta dade da mutuwa saboda ba karamun shammatar ta maganar tayi ba ,wato surrogate mother ta kawo ta tayi,a saka mata kwan haihuwarsu sannan saboda ita yar iskace ta haifa musu ɗa tana matsayin wadda bata taba aure ba.
Tsaye Abla ta miƙe tana Mai bin su da kallo kana ta kalli mutumin tace "Alhaji,ni kam bazan maku surrogate mother ba sannan da nasan abunda ya kawo ni nan da bazan taba zuwa ba 'dan haka ka rike 1.5 dinka ƙilan tayi maka Amfani ko ka ƙara habakawa ta hanyar zubasu ciki gidan marayu,kilan ma rabon ɗa namijin ne baka dashi .
Aikuwa bashi dashi."hajiya maimuna ta ɗauke"tsaye ta miƙe itama tana Mai Nunasa da yatsa tace "wallahi salees Bazaka taba samun ɗa namiji ba na maka baki,"Kayita haifar ƴaƴa mata kenan kaga uku ga wata ta huɗu ,ta nuna Abla wadda ta tsaya chak a lokacin da mahaifiyar ta tayi wannan furucin.
Rai a bace ta juyo tace"mama 'dan Allah mubar wannan wasan wanda zamu buga a gida ma kawai Ya isa tunda ke kinsan banyi daya abunda kike so ba Babu yarda za'ayi nayi wannan amma duk da haka kika rufe ni kika kawoni wanda bai mun daɗi ba ."
Wata kwalla ce ta zubo idanun hajiya Maimuna amma ta share kafun ta kuma cewa"ko baka ganeni ba salees ni bazan taba manta mugu irinka ba ,bari na tuna maka wacece ni,
Maimuna harka ce ta garin jos wadda ka gudu ka bari da ciki wanda kace kawai naje na zubar ba tare da ka damu da rayuwata ba daga bisani ma ka bace ,to ga shegiyarka nan na haifa kuma ta rayu sannan inaso ka sani gobe da wannan labarin zakayi kumallon safe a jaridar karfe bakwai.
"Ke tsohuwar kilaki"matarsa ta daka ma hajiya maimuna tsawa,
Ke baƙar balama,ki rike kanki ki kuma iya bakinki ,nafiki iya shege ,dama Ai Allah yayi gaskiya mazinaci sai mazinaciya wanda bama sai an faɗa mun ba gashi a goshinki ,kuma ki sani babu abunda zai cire Abla a matsayin ƴar mijinki da Ya haifa a bariki,ki kalleni da kyau bana tsoran abun kunya ni gaba na bashi ba baya ba.
"Hajiya Maimuna ta bata amasa".
Zata mayar mata da raddi mijin nata Ya riƙe ta yana ma faɗin 'bilki barni da ita,
Kallansa Ya mayar kanta yace 'dama Maimuna ai nasan tun ba yau ba abun kunya kin basa gaba ne ba baya ba saboda keɗin a cikin kazamai ta ajin farko ce ,karuwa da ke yar tasha Ƴar titi wadda babu abunda kika saka a gabanki sai san kuɗi da buɗe ma maza kafafafu,
Na yarda nayi kuskure wanda Babu wanda Ya wuce sa amma ki sani wannan shegiyar karuwar irin ki ba ƴata bace kije chan ki nemo mata uba tunda ke ɗin kazar ko wanne karene ,sannan ki kalleni, ni ba irin mazajen da zaki wa barazana bane a dare daya zan iya sa a batar dake ɗan haka ba sai anjima ba yanzu ku fice mun da warin jikinku a office kafun na wulakantaku ,
Now leave.
Goge wasu zafafan hawaye Abla tayi,bata taba jin kasƙanci irin na yau ba ,bata taba jin zamanta shegiya Ya dameta kamar yau ba,bata taba wulakanta irin yau ba,Share hawayen dake bin kuncinta tayi ta taka har table dinsa ta dora hannayenta akan table dinsa ,lasar lebenta na kasa tayi kana ta kallesa tace"Idan naga ina wani wulakancin sai na ringa tunanin inda na samosu amma a yau na samu amsata ,a gun mutumin da bai chanchanci a kirasa da uba ba ,ka ce mama karuwa ce Mai buɗe ma kowanne kare kafa,ring ring,does that ring a bell?"
Sound ɗin disagreement tayi da bakinta kafun tace "bazan dauki zunubin kiran Mahaifina kare ba duk da kuwa yace shi ba mahaifina bane ,kamar yarda kayi kokarin tsorata mama ,ni bana tsoro sannan na maka alkawari sai na sauke wannan tsaurin dake kanka,kafara kirgen faɗuwarka a hannun shegiya daga yau,namaka Alkawari dakanka zaka nemi na kiraka baba Amma Bazaka samu ba saboda bana mantuwa kuma bana yafe wulakanci ,".
Zagayawa tayi daidai inda kujerarsa take ta shafa a hankali tace "namaka alkawari sai na kwace kujerar nan taka,zan zauna akanta kuma Babu abunda zaka iya akai,".
Na hau kan mission a nan gurin a gabanka,sai na wulakanta maza irinka sannan a hannu daya sai na kwace kamfaninka a hankali Alkwarine wannan.
Hanyar fita da dauka kafun ta juyo ta kallesa tace 'yauwa sunana ABLA ADNAN yarinyar da ta bama kanta sunan uba ,bana bukatar salis domin dafin ABLA ADNAN baya bukatar wani uba tun ba ace uba irinka ba,
Hannayenta ta haɗa biyu tace 'nabarku lapia .
CHUCHUJAY✍🏽.
08130229878
Bạn đang đọc truyện trên: AzTruyen.Top